< Yoshuwa 7 >
1 Amma Isra’ilawa ba su yi aminci game da kayan da aka hallaka ba; Akan ɗan Karmi, ɗan Zabdi, ɗan Zera, na kabilan Yahuda ya kwashi waɗansu abubuwa, saboda haka fushin Ubangiji ya sauka a kan Isra’ilawa.
Forsothe the sones of Israel braken `the comaundement, and mystoken of the halewid thing; for Achar, the son of Charmy, sone of Zabdi, sone of Zare, of the lynage of Juda, toke sum thing of the halewid thing; and the Lord was wrooth ayens the sones of Israel.
2 Sai Yoshuwa ya aika mutane daga Yeriko zuwa Ai kusa da Bet-Awen gabas da Betel, ya ce musu, “Ku je ku leƙo ku ga yadda yankin yake.” Sai mutanen suka je suka leƙo asirin ƙasar Ai.
And whanne Josue sente men fro Jerico ayens Hai, which is bisidis Bethauen, at the eest coost of the citee Bethel, he seide to hem, Stie ye, and aspie ye the lond. Whiche filliden `the comaundementis, and aspieden Hay;
3 Da suka dawo wurin Yoshuwa suka ce, “Ba lalle dukan jama’a su je yaƙi da Ai ba, ka aika mutum dubu biyu ko dubu uku su je su ciwo ƙasar da yaƙi, ba sai ka dami mutane duka ba, gama mutanen wurin kaɗan ne.”
and thei turneden ayen, and seiden to hym, `Not al the puple stie, but twey ether thre thousynde of men go, and do awei the citee; whi schal al the puple be trauelid in veyn ayens feweste enemyes?
4 Saboda haka sai kimanin mutum duba uku suka haura; amma mutanen Ai suka fatattake su,
Therfor thre thousynde of fiyteris stieden, whiche turneden the backis anoon,
5 suka kashe Isra’ilawa wajen mutum talatin da shida, suka fafari Isra’ilawa tun daga bakin ƙofar birnin har zuwa wurin da ake fasa duwatsu. Suka karkashe su a gangare. Wannan ya sa zuciyar Isra’ilawa ta narke suka zama kamar ruwa.
and weren smytun of the men of Hay; and sixe and thretti men of hem `felden doun; and aduersaries pursueden hem fro the yate til to Saberym; and thei felden doun fleynge bi lowe places. And the herte of the puple dredde, and was maad vnstidefast at the licnesse of watir.
6 Sai Yoshuwa ya yaga tufafinsa ya fāɗi rubda ciki a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, yana can har yamma. Dattawan Isra’ila ma suka yi haka, suka zuba toka a kawunansu.
Sotheli Josue torente hise clothis, and felde lowe to the erthe bifor the arke of the Lord, `til to euentid, as wel he, as alle the elde men of Israel; and thei castiden powdir on her heedis.
7 Yoshuwa kuma ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, me ya sa ka sa mutanen nan suka ƙetare Urdun don ka bari mu shiga hannun Amoriyawa su hallaka mu? Kila da mun haƙura mun zauna a ɗaya gefen Urdun da ya fi mana!
And Josue seide, Alas! alas! Lord God, what woldist thou lede this puple ouer the flood Jordan, that thou schuldist bitake vs in the hond of Ammorrey, and schulde leese vs? Y wolde, that as we bygunnen, we hadden dwellid biyondis Jordan.
8 Ya Ubangiji me zan ce, yanzu da abokan gāban Isra’ilawa suka ci ƙarfinsu?
My Lord God, what schal Y seie, seynge Israel turnynge the backis to hise enemyes?
9 Yanzu Kan’aniyawa da sauran jama’a za su ji, za su zo su kewaye mu su share sunanmu daga duniya. To, yanzu me za ka yi don girman sunanka?”
Cananeys, and alle dwelleris of the lond schulen here, and thei schulen be gaderid togidere, and schulen cumpas vs, and schulen do awei oure name fro erthe; and what schalt thou do to thi grete name?
10 Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka tashi! Me kake yi kwance rubda ciki?
And the Lord seide to Josue, Rise thou; whi liggist thou low in the erthe?
11 Isra’ilawa sun yi zunubi, sun karya sharaɗin da na yi musu. Sun ɗauki waɗansu abubuwan da aka keɓe; sun yi sata, sun yi ƙarya, sun ɓoye su cikin kayansu.
Israel synnede, and brak my couenaunt; and thei token of the halewid thing, and thei han stole, and lieden, and hidden among her vessels.
12 Shi ne ya sa Isra’ilawa suka kāsa yin tsayayya da abokan gābansu; suka juya suka gudu domin za a hallaka su. Ba zan sāke kasancewa tare da ku ba sai in kun hallaka duk abin da aka keɓe don hallaka.
And Israel may not stonde bifore hise enemyes, and Israel schal fle hem, for it is defoulid with cursyng; Y schal no more be with you, til ye al to breke hym which is gilti of this trespas.
13 “Tashi, ka je ka tsarkake mutane. Ka ce musu su tsarkake kansu, su yi shiri domin gobe; gama ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, a cikinku akwai abubuwan da aka keɓe, ya Isra’ilawa. Ba za ku iya yin tsayayya da abokan gābanku ba sai in kun rabu da abubuwan nan da aka haramta.
Rise thou, halewe the puple, and seie thou to hem, Be ye halewid ayens to morewe; for the Lord God of Israel seith these thingis, A! Israel! cursyng is in the myddis of thee; thou schalt not mowe stonde bifor thin enemyes, til he that is defoulyd bi this trespas, be doon awei fro thee.
14 “‘Da safe ku zo kabila-kabila. Kabilar da Ubangiji ya ware, za tă zo gaba gida-gida; gidan da Ubangiji ya ware, za su zo gaba iyali-iyali. Iyalin kuma da Ubangiji ya ware, za su zo gaba mutum bayan mutum.
And ye schulen come eerli, alle men bi youre lynagis; and whateuer lynage the lot schal fynde, it schal come bi hise meynees; and the meynee schal come bi housis, and the hous schal come bi men.
15 Mutumin da aka same shi da haramtattun abubuwan kuwa za a ƙone shi, duk da mallakarsa domin ya karya sharaɗin da Ubangiji ya yi muku, ya yi abin kunya a Isra’ila!’”
And whoeuer schal be takun with this trespas, he schal be brent bi fier with al his catel, for he brak the couenaunt of the Lord, and dide vnleueful thing in Israel.
16 Kashegari da sassafe Yoshuwa ya sa Isra’ilawa suka fito kabila-kabila, aka ware kabilar Yahuda.
Therfor Josue roos eerly, and settide in ordre Israel, bi hise lynagis; and the lynage of Juda was foundun;
17 Gidan Yahuda suka zo gaba, sai aka ware gidan Zera, aka sa suka fito iyali-iyali, sai aka ware Zabdi.
and whanne that lynage was brouyt forth bi hise meynees, the meyne of Zare was foundun. And Josue brouyte forth it bi men, ethir housis, and foond Zabdi;
18 Yoshuwa kuwa ya sa iyalin Zabdi suka fito mutum-mutum, sai kuwa aka ware Akan ɗan Karmi, ɗan Zimri, ɗan Zera na kabilar Yahuda.
whos hows he departide in to alle men bi hemsilf; and he foond Achar, the sone of Charmy, sone of Zabdi, sone of Zare, of the lynage of Juda.
19 Sai Yoshuwa ya ce wa Akan, “Ɗana, sai ka ba Ubangiji, Allah na Isra’ila ɗaukaka, ka yi masa yabo. Ka gaya mini abin da ka yi; kada ka ɓoye mini.”
And he seide to Achar, My sone, yyue thou glorie to the Lord God of Israel, and knowleche thou, and schew to me what thou hast do; hide thou not.
20 Akan kuwa ya amsa ya ce, “Gaskiya ne! Na yi wa Ubangiji, Allah na Isra’ila zunubi. Ga abin da na yi.
And Achar answeryde to Josue, and seide to hym, Verily, Y synnede bifor the Lord God of Israel, and Y dide `so and so;
21 A cikin ganimar, na ga doguwar riga mai kyau irin ta Babilon, da shekel ɗari biyu na azurfa, da kuma sandan zinariya mai nauyin shekel hamsin, sai raina ya so su, na kuwa kwashe su. Na tona rami a cikin ƙasa a tentina; na ɓoye.”
for among the spuylis Y siy a reed mentil ful good, and two hundrid siclis of siluer, and a goldun reule of fifti siclis; and Y coueytide, and took awei, and hidde in the erthe, ayens the myddis of my tabernacle; and Y hilide the siluer with erthe doluun.
22 Sai Yoshuwa ya aiki’yan aika suka tafi da gudu zuwa tenti ɗin, haka kuwa suka same su a ɓoye a tentinsa, da azurfa a ƙarƙashi.
Therfor Josue sente mynystris, whyche runnen to his tabernacle, and foundun alle thingis hid in the same place, and the siluer togidere; and thei token awei fro the tente,
23 Suka kwashe kayan daga tenti ɗin suka kawo wa Yoshuwa da sauran Isra’ilawa, suka baza su a gaban Ubangiji.
and brouyten `tho thingis to Josue, and to alle the sones of Israel; and thei castiden forth bifor the Lord.
24 Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka ɗauki Akan ɗan Zera, da azurfar, doguwar rigar, sandan zinariya,’ya’yansa maza da mata, shanunsa, jakuna da tumaki, tentinsa da duk abin da yake da shi, suka kai su Kwarin Akor.
Therfor Josue took Achar, the sone of Zare, and the siluer, and the mentil, and the goldun reule, and hise sones, and douytris, oxun, assis, and scheep, and the tabernacle `it silf, and al the purtenaunce of household, and al Israel with Josue; and thei ledden hem to the valei of Achar;
25 Yoshuwa ya ce, “Me ya sa ka jawo mana wahala haka? Ubangiji zai kawo maka wahala kai ma a yau.” Sai dukan Isra’ilawa suka jajjefe shi, bayan da suka gama jifarsa sai suka ƙone sauran.
where Josue seide, For thou disturblidist vs, the Lord schal disturble thee in this dai. And al Israel stonyde hym; and alle thingis that weren hise, weren wastid bi fier.
26 Suka tara manyan duwatsu a kan Akan, tarin duwatsun na nan a can har wa yau. Sa’an nan Ubangiji ya huce daga fushinsa mai zafi. Saboda haka ake kiran wurin Kwarin Akor.
And thei gaderiden on hym a greet heep of stoonys, whiche dwellen til in to present day. And the strong veniaunce of the Lord was turned awei fro hem; and the name of that place was clepid the valey of Achar `til to day.