< Yoshuwa 7 >

1 Amma Isra’ilawa ba su yi aminci game da kayan da aka hallaka ba; Akan ɗan Karmi, ɗan Zabdi, ɗan Zera, na kabilan Yahuda ya kwashi waɗansu abubuwa, saboda haka fushin Ubangiji ya sauka a kan Isra’ilawa.
But the sons of Israel committed a trespass in what was set apart. For Achan, the son of Carmi, the son of Zabdi, the son of Zerah, of the tribe of Judah, took from what was set apart, and the anger of Jehovah was kindled against the sons of Israel.
2 Sai Yoshuwa ya aika mutane daga Yeriko zuwa Ai kusa da Bet-Awen gabas da Betel, ya ce musu, “Ku je ku leƙo ku ga yadda yankin yake.” Sai mutanen suka je suka leƙo asirin ƙasar Ai.
And Joshua sent men from Jericho to Ai, which is beside Beth-aven, on the east side of Bethel, and spoke to them, saying, Go up and spy out the land. And the men went up and spied out Ai.
3 Da suka dawo wurin Yoshuwa suka ce, “Ba lalle dukan jama’a su je yaƙi da Ai ba, ka aika mutum dubu biyu ko dubu uku su je su ciwo ƙasar da yaƙi, ba sai ka dami mutane duka ba, gama mutanen wurin kaɗan ne.”
And they returned to Joshua, and said to him, Let not all the people go up, but let about two or three thousand men go up and smite Ai. Do not make all the people to toil there, for they are but few.
4 Saboda haka sai kimanin mutum duba uku suka haura; amma mutanen Ai suka fatattake su,
So there went up there of the people about three thousand men. And they fled before the men of Ai.
5 suka kashe Isra’ilawa wajen mutum talatin da shida, suka fafari Isra’ilawa tun daga bakin ƙofar birnin har zuwa wurin da ake fasa duwatsu. Suka karkashe su a gangare. Wannan ya sa zuciyar Isra’ilawa ta narke suka zama kamar ruwa.
And the men of Ai smote of them about thirty-six men. And they chased them from before the gate even to Shebarim, and smote them at the descent. And the hearts of the people melted, and became as water.
6 Sai Yoshuwa ya yaga tufafinsa ya fāɗi rubda ciki a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, yana can har yamma. Dattawan Isra’ila ma suka yi haka, suka zuba toka a kawunansu.
And Joshua tore his clothes, and fell to the earth upon his face before the ark of Jehovah until the evening, he and the elders of Israel, and they put dust upon their heads.
7 Yoshuwa kuma ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, me ya sa ka sa mutanen nan suka ƙetare Urdun don ka bari mu shiga hannun Amoriyawa su hallaka mu? Kila da mun haƙura mun zauna a ɗaya gefen Urdun da ya fi mana!
And Joshua said, Alas, O lord Jehovah, why have thou at all brought this people over the Jordan, to deliver us into the hand of the Amorites, to cause us to perish? Would that we had been content and dwelt beyond the Jordan!
8 Ya Ubangiji me zan ce, yanzu da abokan gāban Isra’ilawa suka ci ƙarfinsu?
Oh, Lord, what shall I say after Israel has turned their backs before their enemies!
9 Yanzu Kan’aniyawa da sauran jama’a za su ji, za su zo su kewaye mu su share sunanmu daga duniya. To, yanzu me za ka yi don girman sunanka?”
For the Canaanites and all the inhabitants of the land will hear of it, and will encompass us around, and cut off our name from the earth, and what will thou do for thy great name?
10 Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka tashi! Me kake yi kwance rubda ciki?
And Jehovah said to Joshua, Get thee up. Why are thou thus fallen upon thy face?
11 Isra’ilawa sun yi zunubi, sun karya sharaɗin da na yi musu. Sun ɗauki waɗansu abubuwan da aka keɓe; sun yi sata, sun yi ƙarya, sun ɓoye su cikin kayansu.
Israel has sinned. Yes, they have even transgressed my covenant which I commanded them. Yes, they have even taken from what was set apart, and have also stolen, and also dissembled. And they have even put it among their own stuff.
12 Shi ne ya sa Isra’ilawa suka kāsa yin tsayayya da abokan gābansu; suka juya suka gudu domin za a hallaka su. Ba zan sāke kasancewa tare da ku ba sai in kun hallaka duk abin da aka keɓe don hallaka.
Therefore the sons of Israel cannot stand before their enemies. They turn their backs before their enemies because they have become accursed. I will not be with you any more unless ye destroy what was set apart from among you.
13 “Tashi, ka je ka tsarkake mutane. Ka ce musu su tsarkake kansu, su yi shiri domin gobe; gama ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, a cikinku akwai abubuwan da aka keɓe, ya Isra’ilawa. Ba za ku iya yin tsayayya da abokan gābanku ba sai in kun rabu da abubuwan nan da aka haramta.
Up, sanctify the people, and say, Sanctify yourselves against tomorrow. For thus says Jehovah, the God of Israel, There is what has been set apart in the midst of thee, O Israel. Thou cannot stand before thine enemies until ye take away the devoted thing from among you.
14 “‘Da safe ku zo kabila-kabila. Kabilar da Ubangiji ya ware, za tă zo gaba gida-gida; gidan da Ubangiji ya ware, za su zo gaba iyali-iyali. Iyalin kuma da Ubangiji ya ware, za su zo gaba mutum bayan mutum.
In the morning therefore ye shall be brought near by your tribes, and it shall be, that the tribe which Jehovah takes shall come near by families, and the family which Jehovah shall take shall come near by households, and the household which Jehovah shall take shall come near man by man.
15 Mutumin da aka same shi da haramtattun abubuwan kuwa za a ƙone shi, duk da mallakarsa domin ya karya sharaɗin da Ubangiji ya yi muku, ya yi abin kunya a Isra’ila!’”
And it shall be, that he who is taken with the devoted thing shall be burnt with fire, he and all that he has, because he has transgressed the covenant of Jehovah, and because he has wrought folly in Israel.
16 Kashegari da sassafe Yoshuwa ya sa Isra’ilawa suka fito kabila-kabila, aka ware kabilar Yahuda.
So Joshua rose up early in the morning, and brought Israel near by their tribes, and the tribe of Judah was taken.
17 Gidan Yahuda suka zo gaba, sai aka ware gidan Zera, aka sa suka fito iyali-iyali, sai aka ware Zabdi.
And he brought near the family of Judah, and he took the family of the Zerahites. And he brought near the family of the Zerahites man by man, and Zabdi was taken.
18 Yoshuwa kuwa ya sa iyalin Zabdi suka fito mutum-mutum, sai kuwa aka ware Akan ɗan Karmi, ɗan Zimri, ɗan Zera na kabilar Yahuda.
And he brought near his household man by man, and Achan, the son of Carmi, the son of Zabdi, the son of Zerah, of the tribe of Judah, was taken.
19 Sai Yoshuwa ya ce wa Akan, “Ɗana, sai ka ba Ubangiji, Allah na Isra’ila ɗaukaka, ka yi masa yabo. Ka gaya mini abin da ka yi; kada ka ɓoye mini.”
And Joshua said to Achan, My son, give, I pray thee, glory to Jehovah, the God of Israel, and make confession to him, and tell me now what thou have done. Hide it not from me.
20 Akan kuwa ya amsa ya ce, “Gaskiya ne! Na yi wa Ubangiji, Allah na Isra’ila zunubi. Ga abin da na yi.
And Achan answered Joshua, and said, Of a truth I have sinned against Jehovah, the God of Israel, and thus and thus have I done:
21 A cikin ganimar, na ga doguwar riga mai kyau irin ta Babilon, da shekel ɗari biyu na azurfa, da kuma sandan zinariya mai nauyin shekel hamsin, sai raina ya so su, na kuwa kwashe su. Na tona rami a cikin ƙasa a tentina; na ɓoye.”
When I saw among the spoil a goodly Babylonian mantle, and two hundred shekels of silver, and a wedge of gold of fifty shekels weight, then I coveted them, and took them. And, behold, they are hid in the ground in the midst of my tent, and the silver under it.
22 Sai Yoshuwa ya aiki’yan aika suka tafi da gudu zuwa tenti ɗin, haka kuwa suka same su a ɓoye a tentinsa, da azurfa a ƙarƙashi.
So Joshua sent messengers, and they ran to the tent. And, behold, it was hid in his tent, and the silver under it.
23 Suka kwashe kayan daga tenti ɗin suka kawo wa Yoshuwa da sauran Isra’ilawa, suka baza su a gaban Ubangiji.
And they took them from the midst of the tent, and brought them to Joshua, and to all the sons of Israel, and they laid them down before Jehovah.
24 Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka ɗauki Akan ɗan Zera, da azurfar, doguwar rigar, sandan zinariya,’ya’yansa maza da mata, shanunsa, jakuna da tumaki, tentinsa da duk abin da yake da shi, suka kai su Kwarin Akor.
And Joshua, and all Israel with him, took Achan the son of Zerah, and the silver, and the mantle, and the wedge of gold, and his sons, and his daughters, and his oxen, and his donkeys, and his sheep, and his tent, and all that he had, and they brought them up to the valley of Achor.
25 Yoshuwa ya ce, “Me ya sa ka jawo mana wahala haka? Ubangiji zai kawo maka wahala kai ma a yau.” Sai dukan Isra’ilawa suka jajjefe shi, bayan da suka gama jifarsa sai suka ƙone sauran.
And Joshua said, Why have thou troubled us? Jehovah shall trouble thee this day. And all Israel stoned him with stones, and they burned them with fire, and stoned them with stones.
26 Suka tara manyan duwatsu a kan Akan, tarin duwatsun na nan a can har wa yau. Sa’an nan Ubangiji ya huce daga fushinsa mai zafi. Saboda haka ake kiran wurin Kwarin Akor.
And they raised over him a great heap of stones, to this day, and Jehovah turned from the fierceness of his anger. Therefore the name of that place was called the valley of Achor to this day.

< Yoshuwa 7 >