< Yoshuwa 6 >
1 Ƙofofin Yeriko kuwa a kulle suke ciki da waje saboda Isra’ilawa, ba mai fita babu kuma mai shiga.
Иерихон же заключен и огражден бысть от лица сынов Израилевых: и никтоже из него исхождаше, ниже вхождаше.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ba ka nasara a kan Yeriko, duk da sarkinta da mayaƙanta.
И рече Господь ко Иисусу: се, Аз предаю тебе в руце Иерихон и царя его, и сущыя в нем, сильны крепостию:
3 Da kai da dukan sojoji, ku zaga birnin sau ɗaya kullum. Ku yi haka har kwana shida.
и обходите град окрест вси мужие крепцыи единою (на день), тако сотворите шесть дний:
4 Ka sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni raguna su kasance a gaban akwatin alkawari. A rana ta bakwai sai ku zaga birnin sau bakwai, firistocin suna busa ƙahoni.
и седмь жерцы да возмут седмь труб рожаных пред кивотом: и в седмый день оыдите град седмижды, и жерцы да вострубят в трубы рожаны:
5 Sa’ad da kuka ji sun ɗauki dogon lokaci suna busa ƙaho, sai mutane gaba ɗaya su tā da murya su yi ihu da ƙarfi; katangar birnin kuwa za tă rushe, sai sojoji su haura, ko wanne yă nufi inda ya fuskanta kai tsaye.”
и будет егда вострубите трубою рожаною, внегда услышати вам глас трубы, да воскликнут вси людие: и воскликнувшым им, падут сами стены града во основании своем, и внидут вси людие устремившеся кийждо прямо себе во град.
6 Yoshuwa ɗan Nun kuwa ya kira firistoci ya ce musu, “Ku ɗauki akwatin alkawari, ku sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni su kasance a gabansa.”
И вниде Иисус сын Навин к жерцем сынов Израилевых и рече им глаголя: возмите кивот завета Господня, и седмь жерцы да возмут седмь труб рожаных пред лицем кивота Господня.
7 Sai ya umarci jama’a ya ce, “Mu je zuwa! Ku zaga birnin, masu tsaro da makamai su shiga gaban akwatin alkawarin Ubangiji.”
И рече им глаголя: повелите людем оыти и окружити град, и воини да предидут вооружени пред кивотом Господним.
8 Da Yoshuwa ya gama yin wa mutane magana, sai firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai a gaban Ubangiji suka sha gaba suna busa ƙahoninsu, akwatin alkawari kuwa yana biye da su.
И бысть егда рече Иисус к людем, и седмь жерцы имуще седмь труб священных да предидут такожде пред Господем, и да вострубят доброгласно: и кивот завета Господня вслед по них да идет:
9 Masu tsaro da makamai kuma suna gaban firistoci waɗanda suke busa ƙahoni, masu tsaro daga baya kuma suna bin akwatin alkawari, ana ta busa ƙahoni.
воини же да предидут напреди, и жерцы трубяще в трубы, и последующии созади кивота завета Господня бяху идуще и трубяще трубами.
10 Amma Yoshuwa ya umarci mutane ya ce, “Kada ku yi kururuwar yaƙi, kada ku tā da murya, kada ku ce kome, sai ranar da na ce ku yi ihu, a sa’an nan ne sai ku yi ihu!”
Людем же заповеда Иисус, глаголя: не вопите, ниже да слышит кто гласа вашего, ниже да изыдет из уст ваших слово до дне, в оньже повелю вам сам воскликнути, и тогда воскликните.
11 Sai ya sa aka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji aka kewaye birnin da shi sau ɗaya, sa’an nan mutane suka dawo masauƙinsu suka kwana a can.
И обшед кивот завета Божия окрест града (единою), абие иде в полк, и ста тамо.
12 Kashegari, Yoshuwa ya tashi da sassafe, firistoci kuma suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji.
Во вторый же день воста Иисус заутра, и воздвигоша жерцы кивот завета Господня.
13 Firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai suka shiga gaba, suna takawa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji suna kuma busa ƙahoni, masu tsaro ɗauke da makamai suna gabansu, sai masu tsaro da suke baya suna biye da akwatin alkawarin Ubangiji.
И жерцы седмь носящии седмь труб предидяху пред кивотом Господним и трубиша трубами, и воини вооружени идяху, и прочии людие вслед кивота завета Господня идуще, и жерцы вострубиша трубами рожаными.
14 A rana ta biyu suka sāke zaga birnin sau ɗaya, suka kuma koma masauƙinsu. Haka suka yi har kwana shida.
И обыдоша град в день вторый единою, и поидоша паки в полк: сице творяху шесть дний.
15 A rana ta bakwai, suka tashi da sassafe suka zaga birnin sau bakwai yadda suka saba. A wannan rana kaɗai ne suka zaga birnin sau bakwai.
И бысть в седмый день, восташа в востание утреннее, и обыдоша град в той день седмижды.
16 A zagawa ta bakwai, da firistoci suka busa ƙahoni, sai Yoshuwa ya ba sojojin umarni ya ce, “Ku yi ihu, gama Ubangiji ya ba ku birnin!
И бысть во обхождении седмем вострубиша жерцы трубами, и рече Иисус к сыном Израилевым: воскликните, предаде бо Господь вам град:
17 Birnin da dukan abin da yake cikinta za a miƙa su ga Ubangiji. Rahab karuwan nan kaɗai ce, da dukan waɗanda suke tare da ita a gidanta za a bari da rai domin ta ɓoye’yan leƙen asirin ƙasa da muka aika.
и будет град сей проклят, и вся, елика суть в нем, Господу сил: токмо Раав блудницу снабдите ю, и вся, елика суть в дому ея, яко сокры прелагатаи, ихже посылахом:
18 Amma, ba za ku ɗauki wani abin da za a hallaka ba, idan kuka yi haka, za ku jawo masifa da hallaka a kan mutanen Isra’ila a inda kuka sauka.
но вы соблюдитеся от клятвы, да не когда помысливше вы возмете от клятвы, и сотворите полк сынов Израилевых клятву, и потребите ны:
19 Dukan azurfa da zinariya, da kwanonin tagulla da na ƙarfe, keɓaɓɓu ne ga Ubangiji, dole a sa su cikin ma’ajin Ubangiji.”
злато же все и сребро, и медь и железо свято да будет Господу: в сокровище Господне да внесется.
20 Da aka busa ƙahoni, sojoji suka yi ihu, da jin ƙarar ƙahoni, mutane suka kuma yi ihu, sai katangar ta rushe; dukan mutanen kuwa suka shiga birnin kai tsaye, suka yi nasara a kanta.
И вострубиша жерцы трубами: егда же услышаша людие глас трубный, воскликнуша вси купно людие гласом великим и сильным: и падоша вся стены града окрест, и внидоша вси людие во град, кийждо противу себе, и прияша град.
21 Suka miƙa wa Ubangiji birnin, suka hallaka kowane abu mai ran da yake cikin birnin da takobi, maza da mata, yara da tsofaffi, shanu, tumaki da jakuna.
И прокля и Иисус, и елика быша во граде, от мужеска полу и до женска, от юноши и до старца, и от телца до овцы и до осляте, все под мечь.
22 Yoshuwa ya ce wa mutanen nan biyu waɗanda suka je leƙen asirin ƙasar, “Ku shiga gidan karuwan nan ku fitar da ita da duk waɗanda suke nata bisa ga alkawarin da kuka yi mata.”
И двоим юношам соглядавшым землю рече Иисус: внидите в дом жены блудницы, и изведите ю оттуду, и вся, елика суть ея, якоже клястеся ей.
23 Sai samarin waɗanda suka je leƙen asirin suka shiga suka fitar da Rahab, mahaifinta da mahaifiyarta, da’yan’uwanta da duk abin da yake nata. Suka fitar da iyalinta gaba ɗaya suka sa su a wani wuri, ba a cikin masauƙin Isra’ilawa ba.
И внидоста два юношы соглядавшии град в дом жены, и изведосте Раав блудницу, и отца ея и матерь ея, и братию ея и все сродство ея, и вся елика быша ей, изведоста и постависта я вне полка Израилева.
24 Sa’an nan suka ƙona birnin tare da dukan abin da yake ciki tatas, amma suka sa azurfa da zinariya da kayan tagulla da na ƙarfe a cikin ma’aji na haikalin Ubangiji.
И град сожгоша огнем со всем, еже бе в нем, кроме злата и сребра, меди и железа, яже отдаша в дом Господень внести Господеви.
25 Amma Yoshuwa ya bar Rahab karuwan nan bai kashe ta ba, ita da iyalinta da duk abin da yake nata, domin ita ta ɓoye mutanen da Yoshuwa ya aika Yeriko don su leƙo asirin ƙasar kuma ta zauna tare da Isra’ilawa har wa yau.
И Раав блудницу и весь дом ея отеческий остави живы Иисус, и обитати сотвори во Израили даже до дне сего, понеже сокры прелагатаи, ихже посла Иисус соглядати Иерихона.
26 A lokacin nan Yoshuwa ya yi wannan alkawari cewa, “Ubangiji zai tsine wa mutumin da zai yi ƙoƙarin sāke gina birnin nan, Yeriko. “A bakin ran ɗan farinsa zai kafa harsashin birnin; a bakin ran ɗan autansa kuma zai sa ƙofofin birnin.”
И прокля Иисус в той день, глаголя: проклят человек пред Господем, иже поставит и созиждет град сей Иерихон: на первенце своем оснует его, и на меншем своем поставит врата его. И сице сотвори Азан, иже от Вефиля: на Авироне первенце своем основа и, и на меншем спасенем постави врата его.
27 Ubangiji ya kasance tare da Yoshuwa, aka kuma san da shi a duk fāɗin ƙasar.
И бяше Господь со Иисусом, и бе имя его по всей земли.