< Yoshuwa 6 >

1 Ƙofofin Yeriko kuwa a kulle suke ciki da waje saboda Isra’ilawa, ba mai fita babu kuma mai shiga.
IJeriko yayivaliwe-ke ngci ngenxa yabantwana bakoIsrayeli. Kakho owaphumayo, njalo kakho owangenayo.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ba ka nasara a kan Yeriko, duk da sarkinta da mayaƙanta.
INkosi yasisithi kuJoshuwa: Bona, nginikele esandleni sakho iJeriko lenkosi yayo lamaqhawe alamandla.
3 Da kai da dukan sojoji, ku zaga birnin sau ɗaya kullum. Ku yi haka har kwana shida.
Lizawubhoda-ke umuzi, wonke amadoda empi, awubhode umuzi kanye. Uzakwenza njalo insuku eziyisithupha.
4 Ka sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni raguna su kasance a gaban akwatin alkawari. A rana ta bakwai sai ku zaga birnin sau bakwai, firistocin suna busa ƙahoni.
Labapristi abayisikhombisa bazathwala impondo zenqama eziyisikhombisa phambi komtshokotsho; kuthi ngosuku lwesikhombisa lizawubhoda umuzi kasikhombisa, labapristi bevuthela impondo.
5 Sa’ad da kuka ji sun ɗauki dogon lokaci suna busa ƙaho, sai mutane gaba ɗaya su tā da murya su yi ihu da ƙarfi; katangar birnin kuwa za tă rushe, sai sojoji su haura, ko wanne yă nufi inda ya fuskanta kai tsaye.”
Kuzakuthi-ke lapho bekhalisa uphondo lwenqama isikhathi eside, nxa lisizwa ukukhala kophondo, abantu bonke bazamemeza ngokuklabalala okukhulu, lomduli womuzi uzadilikela phansi; labantu bazakwenyuka, ngulowo lalowo maqondana laye.
6 Yoshuwa ɗan Nun kuwa ya kira firistoci ya ce musu, “Ku ɗauki akwatin alkawari, ku sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni su kasance a gabansa.”
Ngakho uJoshuwa indodana kaNuni wabiza abapristi wathi kibo: Thwalani umtshokotsho wesivumelwano, labapristi abayisikhombisa bathwale impondo zezinqama eziyisikhombisa phambi komtshokotsho weNkosi.
7 Sai ya umarci jama’a ya ce, “Mu je zuwa! Ku zaga birnin, masu tsaro da makamai su shiga gaban akwatin alkawarin Ubangiji.”
Wasesithi ebantwini: Dlulani liwuzingelezele umuzi, lohlomileyo kadlule phambi komtshokotsho weNkosi.
8 Da Yoshuwa ya gama yin wa mutane magana, sai firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai a gaban Ubangiji suka sha gaba suna busa ƙahoninsu, akwatin alkawari kuwa yana biye da su.
Kwasekusithi uJoshuwa esekhulume ebantwini, abapristi abayisikhombisa bethwele impondo eziyisikhombisa zenqama bakhokhela phambi kweNkosi, bavuthela impondo, lomtshokotsho wesivumelwano seNkosi wabalandela.
9 Masu tsaro da makamai kuma suna gaban firistoci waɗanda suke busa ƙahoni, masu tsaro daga baya kuma suna bin akwatin alkawari, ana ta busa ƙahoni.
Abahlomileyo basebehamba phambi kwabapristi ababevuthela izimpondo, lesigaba sasemuva salandela umtshokotsho, bahamba bevuthela izimpondo.
10 Amma Yoshuwa ya umarci mutane ya ce, “Kada ku yi kururuwar yaƙi, kada ku tā da murya, kada ku ce kome, sai ranar da na ce ku yi ihu, a sa’an nan ne sai ku yi ihu!”
UJoshuwa wayelaye-ke abantu esithi: Lingamemezi, loba lizwakalise ilizwi lenu; kungaphumi lizwi emlonyeni wenu kuze kube lusuku engizalitshela ngalo ukuthi limemeze; beselimemeza.
11 Sai ya sa aka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji aka kewaye birnin da shi sau ɗaya, sa’an nan mutane suka dawo masauƙinsu suka kwana a can.
Ngakho umtshokotsho weNkosi wawubhoda umuzi, uzingelezela kanye; basebesiza enkambeni, balala enkambeni ebusuku.
12 Kashegari, Yoshuwa ya tashi da sassafe, firistoci kuma suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji.
UJoshuwa wasevuka ekuseni kakhulu, labapristi bathwala umtshokotsho weNkosi.
13 Firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai suka shiga gaba, suna takawa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji suna kuma busa ƙahoni, masu tsaro ɗauke da makamai suna gabansu, sai masu tsaro da suke baya suna biye da akwatin alkawarin Ubangiji.
Labapristi abayisikhombisa bephethe impondo zezinqama eziyisikhombisa phambi komtshokotsho weNkosi baqhubeka behamba, bevuthela izimpondo, labahlomileyo bahamba phambi kwabo, lesigaba sasemuva salandela umtshokotsho weNkosi, bahamba bevuthela izimpondo.
14 A rana ta biyu suka sāke zaga birnin sau ɗaya, suka kuma koma masauƙinsu. Haka suka yi har kwana shida.
Langosuku lwesibili bawuzingelezela umuzi kanye, babuyela enkambeni. Benza njalo insuku eziyisithupha.
15 A rana ta bakwai, suka tashi da sassafe suka zaga birnin sau bakwai yadda suka saba. A wannan rana kaɗai ne suka zaga birnin sau bakwai.
Kwasekusithi ngosuku lwesikhombisa bavuka ngovivi emadabukakusa, bawubhoda umuzi kasikhombisa ngendlela efananayo. Kuphela ngalolosuku bawubhoda umuzi kasikhombisa.
16 A zagawa ta bakwai, da firistoci suka busa ƙahoni, sai Yoshuwa ya ba sojojin umarni ya ce, “Ku yi ihu, gama Ubangiji ya ba ku birnin!
Kwasekusithi ngesikhathi sesikhombisa, abapristi bavuthela impondo, uJoshuwa wasesithi ebantwini: Memezani, ngoba iNkosi ilinikile umuzi.
17 Birnin da dukan abin da yake cikinta za a miƙa su ga Ubangiji. Rahab karuwan nan kaɗai ce, da dukan waɗanda suke tare da ita a gidanta za a bari da rai domin ta ɓoye’yan leƙen asirin ƙasa da muka aika.
Kodwa umuzi wona lakho konke okukuwo kuzakwehlukaniselwa eNkosini; nguRahabi iwule kuphela ozaphila, yena labo bonke alabo endlini yakhe, ngoba wafihla izithunywa esazithumayo.
18 Amma, ba za ku ɗauki wani abin da za a hallaka ba, idan kuka yi haka, za ku jawo masifa da hallaka a kan mutanen Isra’ila a inda kuka sauka.
Kodwa lina sibili zigcineni kokuqalekisiweyo, hlezi lizenze abaqalekisiweyo nxa lithatha kokuqalekisiweyo, lenze inkamba yakoIsrayeli ibe yinto eqalekisiweyo, liyihluphe.
19 Dukan azurfa da zinariya, da kwanonin tagulla da na ƙarfe, keɓaɓɓu ne ga Ubangiji, dole a sa su cikin ma’ajin Ubangiji.”
Kodwa sonke isiliva legolide, lezitsha zethusi lezensimbi, kungcwele eNkosini. Kuzakuza endlini yokuligugu kweNkosi.
20 Da aka busa ƙahoni, sojoji suka yi ihu, da jin ƙarar ƙahoni, mutane suka kuma yi ihu, sai katangar ta rushe; dukan mutanen kuwa suka shiga birnin kai tsaye, suka yi nasara a kanta.
Abantu basebememeza, kwavuthelwa izimpondo. Kwasekusithi abantu besizwa ukukhala kwempondo, abantu bamemeza ngokuklabalala okukhulu, umduli wadilikela phansi, labantu benyukela emzini, ngulowo lalowo maqondana laye, bawuthumba umuzi.
21 Suka miƙa wa Ubangiji birnin, suka hallaka kowane abu mai ran da yake cikin birnin da takobi, maza da mata, yara da tsofaffi, shanu, tumaki da jakuna.
Batshabalalisa konke okusemzini, kusukela kowesilisa kusiya kowesifazana, kusukela komutsha kusiya komdala, kuze kube senkabini lemvini lobabhemi, ngobukhali benkemba.
22 Yoshuwa ya ce wa mutanen nan biyu waɗanda suka je leƙen asirin ƙasar, “Ku shiga gidan karuwan nan ku fitar da ita da duk waɗanda suke nata bisa ga alkawarin da kuka yi mata.”
Lakulawomadoda amabili ayeyehlola ilizwe uJoshuwa wathi: Ngenani endlini yowesifazana oliwule, likhuphe kuyo owesifazana lakho konke alakho, njengokufunga kwenu kuye.
23 Sai samarin waɗanda suka je leƙen asirin suka shiga suka fitar da Rahab, mahaifinta da mahaifiyarta, da’yan’uwanta da duk abin da yake nata. Suka fitar da iyalinta gaba ɗaya suka sa su a wani wuri, ba a cikin masauƙin Isra’ilawa ba.
Lamajaha izinhloli angena akhupha uRahabi loyise lonina labanewabo lakho konke ayelakho; akhupha zonke izihlobo zakhe, azibeka ngaphandle kwenkamba yakoIsrayeli.
24 Sa’an nan suka ƙona birnin tare da dukan abin da yake ciki tatas, amma suka sa azurfa da zinariya da kayan tagulla da na ƙarfe a cikin ma’aji na haikalin Ubangiji.
Basebewutshisa umuzi ngomlilo lakho konke okwakukiwo; kuphela isiliva legolide lezitsha zethusi lezensimbi bakufaka kokuligugu kwendlu yeNkosi.
25 Amma Yoshuwa ya bar Rahab karuwan nan bai kashe ta ba, ita da iyalinta da duk abin da yake nata, domin ita ta ɓoye mutanen da Yoshuwa ya aika Yeriko don su leƙo asirin ƙasar kuma ta zauna tare da Isra’ilawa har wa yau.
Ngakho uRahabi iwule, lendlu kayise, labo bonke ayelabo, uJoshuwa wabayekela bephila; wahlala phakathi koIsrayeli kuze kube lamuhla, ngoba wafihla izithunywa uJoshuwa ayezithume ukuhlola iJeriko.
26 A lokacin nan Yoshuwa ya yi wannan alkawari cewa, “Ubangiji zai tsine wa mutumin da zai yi ƙoƙarin sāke gina birnin nan, Yeriko. “A bakin ran ɗan farinsa zai kafa harsashin birnin; a bakin ran ɗan autansa kuma zai sa ƙofofin birnin.”
UJoshuwa wabafungisa esithi: Uqalekisiwe umuntu phambi kweNkosi osukuma akhe lumuzi iJeriko. Uzawusekela ngezibulo lakhe, amise amasango awo ngecinathunjana lakhe.
27 Ubangiji ya kasance tare da Yoshuwa, aka kuma san da shi a duk fāɗin ƙasar.
Ngokunjalo iNkosi yaba loJoshuwa, lodumo lwakhe lwaba selizweni lonke.

< Yoshuwa 6 >