< Yoshuwa 6 >
1 Ƙofofin Yeriko kuwa a kulle suke ciki da waje saboda Isra’ilawa, ba mai fita babu kuma mai shiga.
Un Jērikus aizslēdza vārtus un bija aizslēgts priekš Israēla bērniem; tur neviens ne izgāja, ne iegāja.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ba ka nasara a kan Yeriko, duk da sarkinta da mayaƙanta.
Tad Tas Kungs sacīja uz Jozua: redzi, Jēriku ar viņa ķēniņu un stipriem karavīriem Es dodu tavā rokā.
3 Da kai da dukan sojoji, ku zaga birnin sau ɗaya kullum. Ku yi haka har kwana shida.
Un ejat ap pilsētu, visi kara vīri visapkārt ap pilsētu vienreiz; tā dari sešas dienas.
4 Ka sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni raguna su kasance a gaban akwatin alkawari. A rana ta bakwai sai ku zaga birnin sau bakwai, firistocin suna busa ƙahoni.
Un septiņi priesteri lai nes septiņas gaviles bazūnes tā šķirsta priekšā, un septītā dienā ejat septiņas reizes ap pilsētu un tie priesteri lai pūš bazūnes.
5 Sa’ad da kuka ji sun ɗauki dogon lokaci suna busa ƙaho, sai mutane gaba ɗaya su tā da murya su yi ihu da ƙarfi; katangar birnin kuwa za tă rushe, sai sojoji su haura, ko wanne yă nufi inda ya fuskanta kai tsaye.”
Un kad tie pūtīs gaviles bazūni un jūs dzirdēsiet bazūnes skaņu, tad lai visi ļaudis kliedz lielā kliegšanā, un pilsētas mūri sagrūs, un tie ļaudis lai kāpj iekšā, kur katrs stāvēdams.
6 Yoshuwa ɗan Nun kuwa ya kira firistoci ya ce musu, “Ku ɗauki akwatin alkawari, ku sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni su kasance a gabansa.”
Tad Jozuas, Nuna dēls, aicināja tos priesterus un uz tiem sacīja: nesiet derības šķirstu, un lai septiņi priesteri nes septiņas gaviles bazūnes Tā Kunga šķirsta priekšā.
7 Sai ya umarci jama’a ya ce, “Mu je zuwa! Ku zaga birnin, masu tsaro da makamai su shiga gaban akwatin alkawarin Ubangiji.”
Un uz tiem ļaudīm viņš sacīja: ejat apkārt ap pilsētu, un tie apbruņotie lai iet Tā Kunga šķirsta priekšā.
8 Da Yoshuwa ya gama yin wa mutane magana, sai firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai a gaban Ubangiji suka sha gaba suna busa ƙahoninsu, akwatin alkawari kuwa yana biye da su.
Un kā Jozuas uz tiem ļaudīm bija sacījis, tā tie septiņi priesteri gāja nesdami septiņas gaviles bazūnes Tā Kunga priekšā, tie gāja un pūta bazūnes, un Tā Kunga derības šķirsts tiem gāja pakaļ.
9 Masu tsaro da makamai kuma suna gaban firistoci waɗanda suke busa ƙahoni, masu tsaro daga baya kuma suna bin akwatin alkawari, ana ta busa ƙahoni.
Un tie apbruņotie gāja to priesteru priekšā, kas bazūnes pūta, un tas pulks gāja tam šķirstam pakaļ, ejot bazūnes pūzdami.
10 Amma Yoshuwa ya umarci mutane ya ce, “Kada ku yi kururuwar yaƙi, kada ku tā da murya, kada ku ce kome, sai ranar da na ce ku yi ihu, a sa’an nan ne sai ku yi ihu!”
Un Jozuas tiem ļaudīm bija pavēlējis sacīdams: jums nebūs kliegt, un lai jūsu balss netop dzirdēta, un lai ne vārds neiziet no jūsu mutes līdz tai dienai, kad es jums sacīšu: kliedzat! Tad jums būs kliegt.
11 Sai ya sa aka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji aka kewaye birnin da shi sau ɗaya, sa’an nan mutane suka dawo masauƙinsu suka kwana a can.
Un Tā Kunga šķirsts gāja ap pilsētu apkārt vienreiz; tad tie nāca atkal lēģerī un palika par nakti lēģerī.
12 Kashegari, Yoshuwa ya tashi da sassafe, firistoci kuma suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji.
Un Jozuas cēlās no rīta agri, un tie priesteri nesa Tā Kunga šķirstu.
13 Firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai suka shiga gaba, suna takawa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji suna kuma busa ƙahoni, masu tsaro ɗauke da makamai suna gabansu, sai masu tsaro da suke baya suna biye da akwatin alkawarin Ubangiji.
Un tie septiņi priesteri, kas tās septiņas gaviles bazūnes nesa Tā Kunga šķirsta priekšā, gāja un ejot pūta bazūnes un tie apbruņotie gāja viņiem pa priekšu, un tas pulks gāja Tā Kunga šķirstam pakaļ, un ejot pūta bazūnes.
14 A rana ta biyu suka sāke zaga birnin sau ɗaya, suka kuma koma masauƙinsu. Haka suka yi har kwana shida.
Un otrā dienā tie gāja ap pilsētu vienreiz un griezās atkal lēģerī; tā tie darīja sešas dienas.
15 A rana ta bakwai, suka tashi da sassafe suka zaga birnin sau bakwai yadda suka saba. A wannan rana kaɗai ne suka zaga birnin sau bakwai.
Un septītā dienā tie cēlās agri, gaismai austot, un gāja ap pilsētu tādā pašā kārtā septiņas reizes; tik vien šai dienā tie gāja ap pilsētu septiņas reizes.
16 A zagawa ta bakwai, da firistoci suka busa ƙahoni, sai Yoshuwa ya ba sojojin umarni ya ce, “Ku yi ihu, gama Ubangiji ya ba ku birnin!
Un septītā reizē, kad tie priesteri bazūnes pūta, Jozuas sacīja uz tiem ļaudīm: kliedzat, jo Tas Kungs jums to pilsētu ir devis.
17 Birnin da dukan abin da yake cikinta za a miƙa su ga Ubangiji. Rahab karuwan nan kaɗai ce, da dukan waɗanda suke tare da ita a gidanta za a bari da rai domin ta ɓoye’yan leƙen asirin ƙasa da muka aika.
Un tā pilsēta un viss, kas tur ir, Tam Kungam lai top izdeldēts; Rahaba tikai, tā mauka, lai paliek dzīva, un visi, kas pie viņas ir namā, jo viņa ir paslēpusi tos vīrus, ko bijām izsūtījuši.
18 Amma, ba za ku ɗauki wani abin da za a hallaka ba, idan kuka yi haka, za ku jawo masifa da hallaka a kan mutanen Isra’ila a inda kuka sauka.
Tikai sargājaties no tā izdeldējamā, ka jūs paši netopat izdeldēti, un neņemat no tā izdeldējamā, un nedarāt, ka Israēla lēģeris netop izdeldēts, un nevedat to postā.
19 Dukan azurfa da zinariya, da kwanonin tagulla da na ƙarfe, keɓaɓɓu ne ga Ubangiji, dole a sa su cikin ma’ajin Ubangiji.”
Bet viss sudrabs un zelts un vara un dzelzs rīki, - tas lai Tam Kungam ir svēts, tam būs nākt pie Tā Kunga mantas.
20 Da aka busa ƙahoni, sojoji suka yi ihu, da jin ƙarar ƙahoni, mutane suka kuma yi ihu, sai katangar ta rushe; dukan mutanen kuwa suka shiga birnin kai tsaye, suka yi nasara a kanta.
Tad nu tie ļaudis kliedza, un bazūnes tapa pūstas. Un notikās, kad tie ļaudis dzirdēja bazūnes skaņu, tad tie ļaudis kliedza lielā kliegšanā, un tas mūris sagruva, un tie ļaudis kāpa pilsētā, kur katrs stāvēdams,
21 Suka miƙa wa Ubangiji birnin, suka hallaka kowane abu mai ran da yake cikin birnin da takobi, maza da mata, yara da tsofaffi, shanu, tumaki da jakuna.
Un tie uzņēma to pilsētu un izdeldēja ar zobena asmeni visu, kas pilsētā bija, vīrus un sievas, bērnus un vecos līdz ar vēršiem un sīkiem lopiem un ēzeļiem.
22 Yoshuwa ya ce wa mutanen nan biyu waɗanda suka je leƙen asirin ƙasar, “Ku shiga gidan karuwan nan ku fitar da ita da duk waɗanda suke nata bisa ga alkawarin da kuka yi mata.”
Tad Jozuas sacīja tiem diviem vīriem, tās zemes izlūkiem: ejat tās sievas, tās maukas, namā, un izvediet no turienes to sievu un visu, kas tai pieder, kā jūs tai esat zvērējuši.
23 Sai samarin waɗanda suka je leƙen asirin suka shiga suka fitar da Rahab, mahaifinta da mahaifiyarta, da’yan’uwanta da duk abin da yake nata. Suka fitar da iyalinta gaba ɗaya suka sa su a wani wuri, ba a cikin masauƙin Isra’ilawa ba.
Tad tie jaunekļi, tie izlūki, gāja un izveda Rahabu un viņas tēvu un viņas māti un viņas brāļus un visu, kas tai piederēja; tie izveda arī visus viņas radus un lika tiem palikt ārā priekš Israēla lēģera.
24 Sa’an nan suka ƙona birnin tare da dukan abin da yake ciki tatas, amma suka sa azurfa da zinariya da kayan tagulla da na ƙarfe a cikin ma’aji na haikalin Ubangiji.
Un to pilsētu tie sadedzināja ar uguni, un visu, kas tur bija; bet to sudrabu un zeltu līdz ar tiem vara un dzelzs rīkiem, to tie lika pie Tā Kunga nama mantas.
25 Amma Yoshuwa ya bar Rahab karuwan nan bai kashe ta ba, ita da iyalinta da duk abin da yake nata, domin ita ta ɓoye mutanen da Yoshuwa ya aika Yeriko don su leƙo asirin ƙasar kuma ta zauna tare da Isra’ilawa har wa yau.
Bet to mauku Rahabu un viņas tēva namu, un visu, kas tai piederēja, Jozuas pameta dzīvu, un tā dzīvo Israēla vidū līdz šai dienai, tāpēc ka viņa bija paslēpusi tos vīrus, ko Jozuas bija izsūtījis, Jēriku izlūkot.
26 A lokacin nan Yoshuwa ya yi wannan alkawari cewa, “Ubangiji zai tsine wa mutumin da zai yi ƙoƙarin sāke gina birnin nan, Yeriko. “A bakin ran ɗan farinsa zai kafa harsashin birnin; a bakin ran ɗan autansa kuma zai sa ƙofofin birnin.”
Un tanī laikā Jozuas zvērēja un sacīja: nolādēts lai ir tas vīrs Tā Kunga priekšā, kas celsies un uztaisīs šo pilsētu Jēriku! Pamatu tas lai liek par savu pirmdzimto un vārtus lai ceļ par savu jaunāko!
27 Ubangiji ya kasance tare da Yoshuwa, aka kuma san da shi a duk fāɗin ƙasar.
Tā Tas Kungs bija ar Jozua, un viņa slava izpaudās pa visu zemi.