< Yoshuwa 6 >

1 Ƙofofin Yeriko kuwa a kulle suke ciki da waje saboda Isra’ilawa, ba mai fita babu kuma mai shiga.
U A pani paa loa ia o Ieriko, no na mamo a Iseraela, aohe mea i puka aku iwaho, aole hoi he mea i komo mai iloko.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ba ka nasara a kan Yeriko, duk da sarkinta da mayaƙanta.
Olelo mai la o Iehova ia Iosna, E nana, ua haawi aku au ia Ieriko i kou lima, a me kona alii, a me na mea koa nui.
3 Da kai da dukan sojoji, ku zaga birnin sau ɗaya kullum. Ku yi haka har kwana shida.
E poai oukou i ua kulanakauhale la, o na kanaka kaua a pau, hookahi no ka poai ana ia kulanakauhale; pela e hana'i oe i na la eono.
4 Ka sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni raguna su kasance a gaban akwatin alkawari. A rana ta bakwai sai ku zaga birnin sau bakwai, firistocin suna busa ƙahoni.
Na na kahuna ehiku e lawe i na pu kiwi hipa ehiku, mamua o ka pahu; a i ka hiku o ka la, ehiku ko oukou poai ana i ua kulanakauhale nei, a e puhi no na kahuna i ka pu.
5 Sa’ad da kuka ji sun ɗauki dogon lokaci suna busa ƙaho, sai mutane gaba ɗaya su tā da murya su yi ihu da ƙarfi; katangar birnin kuwa za tă rushe, sai sojoji su haura, ko wanne yă nufi inda ya fuskanta kai tsaye.”
A hiki i ka wa e puhi loihi ai lakou i ke kiwi hipa, a lohe oukou i ke kani ana o ua mau pu nei, alaila, e hooho na kanaka a pau i ka hooho nui. Alaila e hiolo loa ilalo ka pa o ua kulanakauhale la, a e pii no kela kanaka keia kanaka ma kona alo iho.
6 Yoshuwa ɗan Nun kuwa ya kira firistoci ya ce musu, “Ku ɗauki akwatin alkawari, ku sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni su kasance a gabansa.”
Hea aku la o Iosua, ke keiki a Nuna i na kahuna, i aku la ia lakou, E hapai i ka pahuberita; a na na kahuna ehiku e lawe i na pu kiwi hipa ehiku, mamua o ka pahu o Iehova.
7 Sai ya umarci jama’a ya ce, “Mu je zuwa! Ku zaga birnin, masu tsaro da makamai su shiga gaban akwatin alkawarin Ubangiji.”
I mai la ia i kanaka, O haele, a e poai i ke kulanakauhale, a o ka mea i makaukau i ke kaua, e hele ia mamua o ka pahu o Iehova.
8 Da Yoshuwa ya gama yin wa mutane magana, sai firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai a gaban Ubangiji suka sha gaba suna busa ƙahoninsu, akwatin alkawari kuwa yana biye da su.
A pau ka Iosua olelo ana i kanaka, alaila, hele ae la imua o Iehova, na kahuna ehiku, e lawe ana i na pu kiwi hipa ehiku, a puhi iho la lakou i ka pu; a hele ae la ka pahu o Iehova mahope o lakou.
9 Masu tsaro da makamai kuma suna gaban firistoci waɗanda suke busa ƙahoni, masu tsaro daga baya kuma suna bin akwatin alkawari, ana ta busa ƙahoni.
A o ka poe i makaukau i ke kaua, hele lakou mamua o na kahuna, ka poe i puhi i ka pu, a hele ka hunapaa mahope o ka pahu, a hele lakou me ke puhi i ka pu.
10 Amma Yoshuwa ya umarci mutane ya ce, “Kada ku yi kururuwar yaƙi, kada ku tā da murya, kada ku ce kome, sai ranar da na ce ku yi ihu, a sa’an nan ne sai ku yi ihu!”
Ua kauoha no o Iosua i kanaka, me ka i aku, mai hooho oukou, aole hoi e uwalaau iki aku. Mai puka aku kekahi olelo, mailoko aku o ko oukou waha, a hiki i ka la a'u e olelo aku ai ia oukou, e hooho, alaila, e hooho oukou.
11 Sai ya sa aka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji aka kewaye birnin da shi sau ɗaya, sa’an nan mutane suka dawo masauƙinsu suka kwana a can.
Poai aku la ka pahu o Iehova ia kulanakauhale, hookahi no ko lakou poai ana; a hoi mai lakou i kahi i hoomoana'i, a malaila lakou i moe ai.
12 Kashegari, Yoshuwa ya tashi da sassafe, firistoci kuma suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji.
Ala mai la o Iosua i ke kakahiaka nui, a hapai ae la na kahuna i ka pahu o Iehova.
13 Firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai suka shiga gaba, suna takawa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji suna kuma busa ƙahoni, masu tsaro ɗauke da makamai suna gabansu, sai masu tsaro da suke baya suna biye da akwatin alkawarin Ubangiji.
A o na kahuna ehiku e lawe ana i na pu kiwi hipa ehiku, mamua o ka pahu o Iehova, hele ae la lakou me ke puhi i ka pu; a o ka poe i makaukau i ke kaua, hele ae la lakou mamua o na kahuna, a o ka hunapaa, hele ae la ia mahope o ka pahu o Iehova, a hele lakou me ke puhi i ka pu.
14 A rana ta biyu suka sāke zaga birnin sau ɗaya, suka kuma koma masauƙinsu. Haka suka yi har kwana shida.
Hookahi no ko lakou poai ana i ua kulanakauhale la, i ka lua o ka la; a hoi mai la lakou i kahi i hoomoana'i; a pela lakou i hana'i i na la eono.
15 A rana ta bakwai, suka tashi da sassafe suka zaga birnin sau bakwai yadda suka saba. A wannan rana kaɗai ne suka zaga birnin sau bakwai.
A i ka hiku o ka la, ala lakou i ka wanaao, a ehiku ko lakou poai ana i ke kulanakauhale, e like me ka mea mamua; ehiku hoi ko lakou poai ana ia la.
16 A zagawa ta bakwai, da firistoci suka busa ƙahoni, sai Yoshuwa ya ba sojojin umarni ya ce, “Ku yi ihu, gama Ubangiji ya ba ku birnin!
A i ka hiku o ka poai ana, i ka wa i puhi na kahuna i ka pu, alaila, olelo ae la o Iosua i kanaka, E hooho oukou; no ka mea, na haawi mai o Iehova i ke kulanakauhale no oukou.
17 Birnin da dukan abin da yake cikinta za a miƙa su ga Ubangiji. Rahab karuwan nan kaɗai ce, da dukan waɗanda suke tare da ita a gidanta za a bari da rai domin ta ɓoye’yan leƙen asirin ƙasa da muka aika.
A e laa kela kulanakauhale ia Iehova, oia, a me na mea a pau iloko. O Rahaba, o ka wahine hookamakama, oia wale no ke ola, oia a me na mea a pau iloko o ka hale me ia, no ka mea, nana no i huna i na elele a kakou i hoouna aku ai.
18 Amma, ba za ku ɗauki wani abin da za a hallaka ba, idan kuka yi haka, za ku jawo masifa da hallaka a kan mutanen Isra’ila a inda kuka sauka.
E malama hoi oukou ia oukou iho i na mea i laa, o laa oukou i ko oukou lawe ana i na mea laa, a hoolilo oukou i ka Iseraela i mea laa, a hoopilikia hoi ia lakou.
19 Dukan azurfa da zinariya, da kwanonin tagulla da na ƙarfe, keɓaɓɓu ne ga Ubangiji, dole a sa su cikin ma’ajin Ubangiji.”
A o ke kala a pau, a me ke gula, a me na ipu keleawe a pau, a me ka hao, e kapu no ia mau mea no Iehova. E komo no ia iloko o ka waihona kala o Iehova.
20 Da aka busa ƙahoni, sojoji suka yi ihu, da jin ƙarar ƙahoni, mutane suka kuma yi ihu, sai katangar ta rushe; dukan mutanen kuwa suka shiga birnin kai tsaye, suka yi nasara a kanta.
A i ko lakou puhi ana i ka pu, hooho aku la na kanaka; a lohe na kanaka i ke kani ana o ka pu, a me ka hooho nui ana a kanaka i hooho ai, alaila hiolo ka pa ilalo, a pii aku la lakou i ke kulanakauhale, o kela kanaka keia kanaka ma kona alo iho, a pio ke kulanakauhale ia lakou.
21 Suka miƙa wa Ubangiji birnin, suka hallaka kowane abu mai ran da yake cikin birnin da takobi, maza da mata, yara da tsofaffi, shanu, tumaki da jakuna.
Me ka maka o ka pahi kaua lakou i luku loa ai i na mea a pau iloko o ke kulanakauhale, o na kane a me na wahine, o na mea opiopio, a me na mea kahiko, o ka bipi, a me ka hipa a me ka hoki.
22 Yoshuwa ya ce wa mutanen nan biyu waɗanda suka je leƙen asirin ƙasar, “Ku shiga gidan karuwan nan ku fitar da ita da duk waɗanda suke nata bisa ga alkawarin da kuka yi mata.”
Olelo aku la o Iosua i ua mau kanaka la nana i makai i ka aina, E komo olua iloko o ka hale o ka wahine hookipa, a e lawe mai iwaho i ka wahine a me kana mea a pau, e like me ka olua i hoohiki ai nona.
23 Sai samarin waɗanda suka je leƙen asirin suka shiga suka fitar da Rahab, mahaifinta da mahaifiyarta, da’yan’uwanta da duk abin da yake nata. Suka fitar da iyalinta gaba ɗaya suka sa su a wani wuri, ba a cikin masauƙin Isra’ilawa ba.
Komo aku la ua mau kanaka ui la o na kiu, a lawe mai la iwaho ia Rahaba, a me kona makuakane, a me kona makuwahine, a me na kaikunane ona, a me kona mau mea a pau; a lawe mai la no hoi lakou i kona poe hoahanau a pau, a waiho iho la ia lakou mawaho o kahi i hoomoana'i ka Iseraela.
24 Sa’an nan suka ƙona birnin tare da dukan abin da yake ciki tatas, amma suka sa azurfa da zinariya da kayan tagulla da na ƙarfe a cikin ma’aji na haikalin Ubangiji.
Puhi iho la lakou i ke kulanakauhale i ke ahi, a me na mea a pau iloko; aka, o ke kala, a me ke gula, a me na ipu keleawe melemele, a me na ipu hao, waiho iho la lakou iloko o ka waihona kala o ka hale o Iehova.
25 Amma Yoshuwa ya bar Rahab karuwan nan bai kashe ta ba, ita da iyalinta da duk abin da yake nata, domin ita ta ɓoye mutanen da Yoshuwa ya aika Yeriko don su leƙo asirin ƙasar kuma ta zauna tare da Isra’ilawa har wa yau.
Hoola aku la o Iosua ia Rahaba, ka wahine hookipa, a me ka poe o kona makuakane, a me kona mea a pau, aia no hoi ia e noho la i neia la, me ka Iseraela; no ka mea, nana no i huna i na elele a Iosua i hoouna aku ai e makai ia Ieriko.
26 A lokacin nan Yoshuwa ya yi wannan alkawari cewa, “Ubangiji zai tsine wa mutumin da zai yi ƙoƙarin sāke gina birnin nan, Yeriko. “A bakin ran ɗan farinsa zai kafa harsashin birnin; a bakin ran ɗan autansa kuma zai sa ƙofofin birnin.”
Ia manawa kauoha no o Iosua ia lakou, me ka hoohiki a me ka i ana aku, E poino auanei imua o Iehova, ke kanaka nana e ku ae a kukulu hou i keia kulanakauhale ia Ieriko. Me kana hiapo ia e hookumu ai, a me kana muli loa e hoopaa ai ia i na puka ona.
27 Ubangiji ya kasance tare da Yoshuwa, aka kuma san da shi a duk fāɗin ƙasar.
Aia no o Iehova me Iosua, a kaulana loa kona inoa ma na aina a pau.

< Yoshuwa 6 >