< Yoshuwa 6 >

1 Ƙofofin Yeriko kuwa a kulle suke ciki da waje saboda Isra’ilawa, ba mai fita babu kuma mai shiga.
Cependant, Jéricho était entourée de murs et fermée; et personne n'en sortait, et personne n'y entrait.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ba ka nasara a kan Yeriko, duk da sarkinta da mayaƙanta.
Et le Seigneur dit à Josué: Voilà que je livre à tes mains Jéricho, son roi et ses hommes puissants.
3 Da kai da dukan sojoji, ku zaga birnin sau ɗaya kullum. Ku yi haka har kwana shida.
Fais-la donc investir par tes gens de guerre.
4 Ka sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni raguna su kasance a gaban akwatin alkawari. A rana ta bakwai sai ku zaga birnin sau bakwai, firistocin suna busa ƙahoni.
5 Sa’ad da kuka ji sun ɗauki dogon lokaci suna busa ƙaho, sai mutane gaba ɗaya su tā da murya su yi ihu da ƙarfi; katangar birnin kuwa za tă rushe, sai sojoji su haura, ko wanne yă nufi inda ya fuskanta kai tsaye.”
Et voici ce qui sera: Lorsque vous sonnerez de la trompette, que tout le peuple ensemble jette un cri; à ce cri, les murs de la ville s'écrouleront d'eux-mêmes, et le peuple y entrera, chacun se précipitant droit dans la ville.
6 Yoshuwa ɗan Nun kuwa ya kira firistoci ya ce musu, “Ku ɗauki akwatin alkawari, ku sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni su kasance a gabansa.”
Josué, fils de Nau, alla auprès des prêtres, et il leur parla, disant:
7 Sai ya umarci jama’a ya ce, “Mu je zuwa! Ku zaga birnin, masu tsaro da makamai su shiga gaban akwatin alkawarin Ubangiji.”
Annoncez au peuple qu'il ait à investir la ville. Que les hommes de guerre, bien armés, marchent devant le Seigneur.
8 Da Yoshuwa ya gama yin wa mutane magana, sai firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai a gaban Ubangiji suka sha gaba suna busa ƙahoninsu, akwatin alkawari kuwa yana biye da su.
Que sept prêtres, tenant les sept trompettes sacrées, marchent pareillement devant le Seigneur, et qu'ils sonnent fortement, et que l'arche de l'alliance du Seigneur les suive.
9 Masu tsaro da makamai kuma suna gaban firistoci waɗanda suke busa ƙahoni, masu tsaro daga baya kuma suna bin akwatin alkawari, ana ta busa ƙahoni.
Que les hommes de guerre passent devant, et que derrière eux les prêtres, qui suivront l'arche de l'alliance du Seigneur, sonnent de la trompette.
10 Amma Yoshuwa ya umarci mutane ya ce, “Kada ku yi kururuwar yaƙi, kada ku tā da murya, kada ku ce kome, sai ranar da na ce ku yi ihu, a sa’an nan ne sai ku yi ihu!”
Et Josué donna ces ordres au peuple, disant: Ne criez point, que personne n'entende votre voix jusqu'à ce que le Seigneur vous fasse connaître le jour ou il faudra crier: alors, vous jetterez un grand cri.
11 Sai ya sa aka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji aka kewaye birnin da shi sau ɗaya, sa’an nan mutane suka dawo masauƙinsu suka kwana a can.
Et l'arche de l'alliance de Dieu, ayant fait le tour de la ville, rentra aussitôt dans le camp, où elle passa la nuit.
12 Kashegari, Yoshuwa ya tashi da sassafe, firistoci kuma suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji.
Le second jour, Josué se leva de grand matin, et les prêtres transportèrent l'arche de l'alliance du Seigneur.
13 Firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai suka shiga gaba, suna takawa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji suna kuma busa ƙahoni, masu tsaro ɗauke da makamai suna gabansu, sai masu tsaro da suke baya suna biye da akwatin alkawarin Ubangiji.
Et les sept prêtres, ceux qui tenaient les sept trompettes, marchèrent devant elle, devant le Seigneur; après eux sortirent les hommes de guerre, puis tout le reste du peuple, derrière l'arche de l'alliance du Seigneur. Et les prêtres sonnèrent de la trompette. Et le reste du peuple fit le tour de la ville, en la serrant de près;
14 A rana ta biyu suka sāke zaga birnin sau ɗaya, suka kuma koma masauƙinsu. Haka suka yi har kwana shida.
Puis, on rentra de nouveau dans le camp, et l'on fit la même chose pendant six jours.
15 A rana ta bakwai, suka tashi da sassafe suka zaga birnin sau bakwai yadda suka saba. A wannan rana kaɗai ne suka zaga birnin sau bakwai.
Et le septième jour, de grand matin, le peuple se leva, et ce jour-là il fit sept fois le tour de la ville.
16 A zagawa ta bakwai, da firistoci suka busa ƙahoni, sai Yoshuwa ya ba sojojin umarni ya ce, “Ku yi ihu, gama Ubangiji ya ba ku birnin!
Enfin, au septième tour, les prêtres sonnèrent de la trompette, et Josué dit aux fils d'Israël: Criez, car le Seigneur vous a livré la ville.
17 Birnin da dukan abin da yake cikinta za a miƙa su ga Ubangiji. Rahab karuwan nan kaɗai ce, da dukan waɗanda suke tare da ita a gidanta za a bari da rai domin ta ɓoye’yan leƙen asirin ƙasa da muka aika.
Elle sera anathème pour le Seigneur des armées, elle et tout ce qu'elle contient, hormis Rahab la prostituée; épargnez cette femme et tout ce que vous trouverez dans sa maison.
18 Amma, ba za ku ɗauki wani abin da za a hallaka ba, idan kuka yi haka, za ku jawo masifa da hallaka a kan mutanen Isra’ila a inda kuka sauka.
Cependant, gardez-vous soigneusement de toucher à rien de ce qui est anathème; ne vous laissez pas entraîner à rien prendre de ce qui est anathème, de peur que vous n'attiriez l'anathème sur le camp des fils d'Israël, et que vous ne nous fassiez briser.
19 Dukan azurfa da zinariya, da kwanonin tagulla da na ƙarfe, keɓaɓɓu ne ga Ubangiji, dole a sa su cikin ma’ajin Ubangiji.”
Tout l'argent, tout l'or, l'airain et le fer, seront consacrés au Seigneur; on les portera dans le trésor du Seigneur.
20 Da aka busa ƙahoni, sojoji suka yi ihu, da jin ƙarar ƙahoni, mutane suka kuma yi ihu, sai katangar ta rushe; dukan mutanen kuwa suka shiga birnin kai tsaye, suka yi nasara a kanta.
Alors, les prêtres sonnèrent de la trompette, et des qu'il ouït les trompettes, le peuple tout entier jeta un cri grand et fort, et le mur de l'enceinte s'écroula de toutes parts, et tout le peuple monta dans la ville.
21 Suka miƙa wa Ubangiji birnin, suka hallaka kowane abu mai ran da yake cikin birnin da takobi, maza da mata, yara da tsofaffi, shanu, tumaki da jakuna.
Et Josué la frappa d'anathème, elle et tout ce qu'elle renfermait, depuis l'homme jusqu'à la femme, depuis l'enfant jusqu'au vieillard, avec le bétail et les bêtes de somme; tout fut passé au fil de l'épée.
22 Yoshuwa ya ce wa mutanen nan biyu waɗanda suka je leƙen asirin ƙasar, “Ku shiga gidan karuwan nan ku fitar da ita da duk waɗanda suke nata bisa ga alkawarin da kuka yi mata.”
Cependant, Josué dit aux deux jeunes hommes qu'il avait envoyés à la découverte: Allez à la maison de la femme, faites-l'en sortir, elle et tout ce qui lui appartient.
23 Sai samarin waɗanda suka je leƙen asirin suka shiga suka fitar da Rahab, mahaifinta da mahaifiyarta, da’yan’uwanta da duk abin da yake nata. Suka fitar da iyalinta gaba ɗaya suka sa su a wani wuri, ba a cikin masauƙin Isra’ilawa ba.
Et les deux jeunes hommes, qui avaient été envoyés à la découverte, entrèrent dans la maison de la femme, et ils emmenèrent Rahab, et son père, et sa mère, et ses frères, et toute sa parenté, et tout ce qui lui appartenait, et ils la firent demeurer hors du camp d'Israël.
24 Sa’an nan suka ƙona birnin tare da dukan abin da yake ciki tatas, amma suka sa azurfa da zinariya da kayan tagulla da na ƙarfe a cikin ma’aji na haikalin Ubangiji.
La ville fut consumée par le feu avec tout ce qu'elle renfermait, hormis l'argent, l'or, l'airain et le fer, que l'on transporta dans le trésor du Seigneur.
25 Amma Yoshuwa ya bar Rahab karuwan nan bai kashe ta ba, ita da iyalinta da duk abin da yake nata, domin ita ta ɓoye mutanen da Yoshuwa ya aika Yeriko don su leƙo asirin ƙasar kuma ta zauna tare da Isra’ilawa har wa yau.
Et Josué épargna Rahab la prostituée, avec toute la famille de son père; il les fit demeurer au milieu d'Israël jusqu'à ce jour, parce qu'elle avait caché les jeunes hommes que Josué avait envoyés à la découverte dans Jéricho.
26 A lokacin nan Yoshuwa ya yi wannan alkawari cewa, “Ubangiji zai tsine wa mutumin da zai yi ƙoƙarin sāke gina birnin nan, Yeriko. “A bakin ran ɗan farinsa zai kafa harsashin birnin; a bakin ran ɗan autansa kuma zai sa ƙofofin birnin.”
Josué ce jour-là, devant le Seigneur, adjura le peuple, disant: Maudit soit l'homme qui rebâtira cette ville; c'est dans la mort de son premier-né qu'il en jettera les fondations, et dans celle du dernier de ses fils qu'il en posera les portes. Ainsi arriva-t-il à Hozan de Béthel: c'est en perdant Abiron, son premier-né, qu'il jeta les fondations de cette ville, et dans la mort du seul fils qui lui restait, qu'il en posa les portes.
27 Ubangiji ya kasance tare da Yoshuwa, aka kuma san da shi a duk fāɗin ƙasar.
Or, le Seigneur était avec Josué, et le nom de Josué remplissait toute la terre.

< Yoshuwa 6 >