< Yoshuwa 6 >
1 Ƙofofin Yeriko kuwa a kulle suke ciki da waje saboda Isra’ilawa, ba mai fita babu kuma mai shiga.
Jéricho était fermée hermétiquement à cause des enfants d'Israël. Personne ne sortait, et personne n'entrait.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ba ka nasara a kan Yeriko, duk da sarkinta da mayaƙanta.
Yahvé dit à Josué: « Voici, je livre Jéricho entre tes mains, avec son roi et ses vaillants hommes.
3 Da kai da dukan sojoji, ku zaga birnin sau ɗaya kullum. Ku yi haka har kwana shida.
Tous vos hommes de guerre marcheront autour de la ville, en faisant une fois le tour de la ville. Vous ferez cela pendant six jours.
4 Ka sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni raguna su kasance a gaban akwatin alkawari. A rana ta bakwai sai ku zaga birnin sau bakwai, firistocin suna busa ƙahoni.
Sept prêtres porteront sept trompettes en corne de bélier devant l'arche. Le septième jour, vous ferez sept fois le tour de la ville, et les prêtres sonneront des trompettes.
5 Sa’ad da kuka ji sun ɗauki dogon lokaci suna busa ƙaho, sai mutane gaba ɗaya su tā da murya su yi ihu da ƙarfi; katangar birnin kuwa za tă rushe, sai sojoji su haura, ko wanne yă nufi inda ya fuskanta kai tsaye.”
Lorsqu'ils sonneront longuement de la corne de bélier et que vous entendrez le son de la trompette, tout le peuple poussera de grands cris; alors la muraille de la ville s'effondrera et le peuple montera, chacun droit devant soi. »
6 Yoshuwa ɗan Nun kuwa ya kira firistoci ya ce musu, “Ku ɗauki akwatin alkawari, ku sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni su kasance a gabansa.”
Josué, fils de Nun, appela les prêtres et leur dit: « Faites monter l'arche de l'alliance, et que sept prêtres portent sept trompettes en cornes de bélier devant l'arche de Yahvé. »
7 Sai ya umarci jama’a ya ce, “Mu je zuwa! Ku zaga birnin, masu tsaro da makamai su shiga gaban akwatin alkawarin Ubangiji.”
Ils dirent au peuple: « Avancez! Faites le tour de la ville, et laissez passer les hommes armés devant l'arche de Yahvé. »
8 Da Yoshuwa ya gama yin wa mutane magana, sai firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai a gaban Ubangiji suka sha gaba suna busa ƙahoninsu, akwatin alkawari kuwa yana biye da su.
Lorsque Josué eut parlé au peuple, les sept prêtres portant les sept trompettes en corne de bélier devant Yahvé s'avancèrent et sonnèrent des trompettes, et l'arche de l'alliance de Yahvé les suivit.
9 Masu tsaro da makamai kuma suna gaban firistoci waɗanda suke busa ƙahoni, masu tsaro daga baya kuma suna bin akwatin alkawari, ana ta busa ƙahoni.
Les hommes armés marchaient devant les prêtres qui sonnaient des trompettes, et l'arche les suivait. Les trompettes sonnaient pendant qu'ils avançaient.
10 Amma Yoshuwa ya umarci mutane ya ce, “Kada ku yi kururuwar yaƙi, kada ku tā da murya, kada ku ce kome, sai ranar da na ce ku yi ihu, a sa’an nan ne sai ku yi ihu!”
Josué donna cet ordre au peuple: « Vous ne crierez pas, vous ne ferez pas entendre votre voix, et aucune parole ne sortira de votre bouche jusqu'au jour où je vous dirai de crier. Alors vous crierez. »
11 Sai ya sa aka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji aka kewaye birnin da shi sau ɗaya, sa’an nan mutane suka dawo masauƙinsu suka kwana a can.
Et il fit faire à l'arche de Yahvé le tour de la ville, en la contournant une fois. Puis ils entrèrent dans le camp, et restèrent dans le camp.
12 Kashegari, Yoshuwa ya tashi da sassafe, firistoci kuma suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji.
Josué se leva tôt le matin, et les prêtres portèrent l'arche de Yahvé.
13 Firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai suka shiga gaba, suna takawa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji suna kuma busa ƙahoni, masu tsaro ɗauke da makamai suna gabansu, sai masu tsaro da suke baya suna biye da akwatin alkawarin Ubangiji.
Les sept prêtres qui portaient les sept trompettes en corne de bélier devant l'arche de l'Éternel marchaient sans cesse et sonnaient des trompettes. Les hommes armés marchaient devant eux. L'arrière-garde suivait l'arche de Yahvé. Les trompettes sonnaient pendant leur marche.
14 A rana ta biyu suka sāke zaga birnin sau ɗaya, suka kuma koma masauƙinsu. Haka suka yi har kwana shida.
Le deuxième jour, ils firent une fois le tour de la ville et rentrèrent au camp. Ils firent cela pendant six jours.
15 A rana ta bakwai, suka tashi da sassafe suka zaga birnin sau bakwai yadda suka saba. A wannan rana kaɗai ne suka zaga birnin sau bakwai.
Le septième jour, ils se levèrent tôt, à l'aube, et firent sept fois le tour de la ville de la même manière. Ce jour-là seulement, ils firent sept fois le tour de la ville.
16 A zagawa ta bakwai, da firistoci suka busa ƙahoni, sai Yoshuwa ya ba sojojin umarni ya ce, “Ku yi ihu, gama Ubangiji ya ba ku birnin!
A la septième fois, lorsque les prêtres sonnèrent des trompettes, Josué dit au peuple: « Criez, car Yahvé vous a donné la ville!
17 Birnin da dukan abin da yake cikinta za a miƙa su ga Ubangiji. Rahab karuwan nan kaɗai ce, da dukan waɗanda suke tare da ita a gidanta za a bari da rai domin ta ɓoye’yan leƙen asirin ƙasa da muka aika.
La ville sera consacrée à Yahvé, elle et tout ce qu'elle contient. Seule Rahab la prostituée vivra, elle et tous ceux qui sont avec elle dans la maison, car elle a caché les messagers que nous avons envoyés.
18 Amma, ba za ku ɗauki wani abin da za a hallaka ba, idan kuka yi haka, za ku jawo masifa da hallaka a kan mutanen Isra’ila a inda kuka sauka.
Mais vous, gardez-vous seulement de ce qui est consacré à la destruction, de peur qu'après l'avoir consacré, vous ne vous empariez de ce qui est consacré; ainsi vous rendriez le camp d'Israël maudit et le troubleriez.
19 Dukan azurfa da zinariya, da kwanonin tagulla da na ƙarfe, keɓaɓɓu ne ga Ubangiji, dole a sa su cikin ma’ajin Ubangiji.”
Mais tout l'argent, l'or, les objets de bronze et de fer sont consacrés à l'Éternel. Ils entreront dans le trésor de Yahvé. »
20 Da aka busa ƙahoni, sojoji suka yi ihu, da jin ƙarar ƙahoni, mutane suka kuma yi ihu, sai katangar ta rushe; dukan mutanen kuwa suka shiga birnin kai tsaye, suka yi nasara a kanta.
Alors le peuple poussa des cris et les prêtres sonnèrent des trompettes. Lorsque le peuple entendit le son de la trompette, il poussa de grands cris, et la muraille s'écroula. Le peuple monta dans la ville, chacun droit devant soi, et il prit la ville.
21 Suka miƙa wa Ubangiji birnin, suka hallaka kowane abu mai ran da yake cikin birnin da takobi, maza da mata, yara da tsofaffi, shanu, tumaki da jakuna.
Ils dévouèrent par interdit tout ce qui se trouvait dans la ville, hommes et femmes, jeunes et vieux, bœufs, moutons et ânes, au fil de l'épée.
22 Yoshuwa ya ce wa mutanen nan biyu waɗanda suka je leƙen asirin ƙasar, “Ku shiga gidan karuwan nan ku fitar da ita da duk waɗanda suke nata bisa ga alkawarin da kuka yi mata.”
Josué dit aux deux hommes qui avaient espionné le pays: « Allez dans la maison de la prostituée, et faites-en sortir la femme et tout ce qu'elle a, comme vous le lui avez juré. »
23 Sai samarin waɗanda suka je leƙen asirin suka shiga suka fitar da Rahab, mahaifinta da mahaifiyarta, da’yan’uwanta da duk abin da yake nata. Suka fitar da iyalinta gaba ɗaya suka sa su a wani wuri, ba a cikin masauƙin Isra’ilawa ba.
Les jeunes gens qui étaient des espions entrèrent et firent sortir Rahab avec son père, sa mère, ses frères et tout ce qui lui appartenait. Ils firent aussi sortir tous les membres de sa famille, et ils les placèrent en dehors du camp d'Israël.
24 Sa’an nan suka ƙona birnin tare da dukan abin da yake ciki tatas, amma suka sa azurfa da zinariya da kayan tagulla da na ƙarfe a cikin ma’aji na haikalin Ubangiji.
Ils brûlèrent la ville par le feu, avec tout ce qu'elle contenait. Ils mirent seulement l'argent, l'or et les objets de bronze et de fer dans le trésor de la maison de Yahvé.
25 Amma Yoshuwa ya bar Rahab karuwan nan bai kashe ta ba, ita da iyalinta da duk abin da yake nata, domin ita ta ɓoye mutanen da Yoshuwa ya aika Yeriko don su leƙo asirin ƙasar kuma ta zauna tare da Isra’ilawa har wa yau.
Mais Rahab la prostituée, la maison de son père et tout ce qu'elle possédait, Josué les a sauvés vivants. Elle vit encore aujourd'hui au milieu d'Israël, car elle a caché les messagers que Josué avait envoyés pour espionner Jéricho.
26 A lokacin nan Yoshuwa ya yi wannan alkawari cewa, “Ubangiji zai tsine wa mutumin da zai yi ƙoƙarin sāke gina birnin nan, Yeriko. “A bakin ran ɗan farinsa zai kafa harsashin birnin; a bakin ran ɗan autansa kuma zai sa ƙofofin birnin.”
En ce temps-là, Josué leur donna un ordre avec serment, en disant: « Maudit soit devant Yahvé l'homme qui se lèvera et bâtira cette ville de Jéricho. C'est par la perte de son premier-né qu'il en posera les fondations, et par la perte de son plus jeune fils qu'il en dressera les portes. »
27 Ubangiji ya kasance tare da Yoshuwa, aka kuma san da shi a duk fāɗin ƙasar.
Yahvé fut donc avec Josué, et sa renommée se répandit dans tout le pays.