< Yoshuwa 6 >
1 Ƙofofin Yeriko kuwa a kulle suke ciki da waje saboda Isra’ilawa, ba mai fita babu kuma mai shiga.
Now Jericho was close shut up and fenced, for fear of the children of Israel, and no man durst go out or come in.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ba ka nasara a kan Yeriko, duk da sarkinta da mayaƙanta.
And the Lord said to Josue: Behold I have given into thy hands Jericho, and the king thereof, and all the valiant men.
3 Da kai da dukan sojoji, ku zaga birnin sau ɗaya kullum. Ku yi haka har kwana shida.
Go round about the city, all ye fighting men, once a day: so shall ye do for six days.
4 Ka sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni raguna su kasance a gaban akwatin alkawari. A rana ta bakwai sai ku zaga birnin sau bakwai, firistocin suna busa ƙahoni.
And on the seventh day the priests shall take the seven trumpets, which are used in the jubilee, and shall go before the ark of the covenant: and you shall go about the city seven times, and the priests shall sound the trumpets.
5 Sa’ad da kuka ji sun ɗauki dogon lokaci suna busa ƙaho, sai mutane gaba ɗaya su tā da murya su yi ihu da ƙarfi; katangar birnin kuwa za tă rushe, sai sojoji su haura, ko wanne yă nufi inda ya fuskanta kai tsaye.”
And when the voice of the trumpet shall give a longer and broken tune, and shall sound in your ears, all the people shall shout together with a very great shout, and the walls of the city shall fall to the ground, and they shall enter in every one at the place against which they shall stand.
6 Yoshuwa ɗan Nun kuwa ya kira firistoci ya ce musu, “Ku ɗauki akwatin alkawari, ku sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni su kasance a gabansa.”
Then Josue the son of Nun called the priests, and said to them: Take the ark of the covenant: and let seven other priests take the seven trumpets of the jubilee, and march before the ark of the Lord.
7 Sai ya umarci jama’a ya ce, “Mu je zuwa! Ku zaga birnin, masu tsaro da makamai su shiga gaban akwatin alkawarin Ubangiji.”
And he said to the people: Go, and compass the city, armed, marching before the ark of the Lord.
8 Da Yoshuwa ya gama yin wa mutane magana, sai firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai a gaban Ubangiji suka sha gaba suna busa ƙahoninsu, akwatin alkawari kuwa yana biye da su.
And when Josue had ended his words, and the seven priests blew the seven trumpets before the ark of the covenant of the Lord,
9 Masu tsaro da makamai kuma suna gaban firistoci waɗanda suke busa ƙahoni, masu tsaro daga baya kuma suna bin akwatin alkawari, ana ta busa ƙahoni.
And all the armed men went before, the rest of the common people followed the ark, and the sound of the trumpets was heard on all sides.
10 Amma Yoshuwa ya umarci mutane ya ce, “Kada ku yi kururuwar yaƙi, kada ku tā da murya, kada ku ce kome, sai ranar da na ce ku yi ihu, a sa’an nan ne sai ku yi ihu!”
But Josue had commanded the people, saying: You shall not shout, nor shall your voice be heard, nor any word go out of your mouth: until the day come wherein I shall say to you: Cry, and shout.
11 Sai ya sa aka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji aka kewaye birnin da shi sau ɗaya, sa’an nan mutane suka dawo masauƙinsu suka kwana a can.
So the ark of the Lord went about the city once a day, and returning into the camp, abode there.
12 Kashegari, Yoshuwa ya tashi da sassafe, firistoci kuma suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji.
And Josue rising before day, the priests took the ark of the Lord,
13 Firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai suka shiga gaba, suna takawa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji suna kuma busa ƙahoni, masu tsaro ɗauke da makamai suna gabansu, sai masu tsaro da suke baya suna biye da akwatin alkawarin Ubangiji.
And seven of them seven trumpets, which are used in the jubilee: and they went before the ark of the Lord walking and sounding the trumpets: and the armed men went before them, and the rest of the common people followed the ark, and they blew the trumpets.
14 A rana ta biyu suka sāke zaga birnin sau ɗaya, suka kuma koma masauƙinsu. Haka suka yi har kwana shida.
And they went round about the city the second day once, and returned into the camp. So they did six days.
15 A rana ta bakwai, suka tashi da sassafe suka zaga birnin sau bakwai yadda suka saba. A wannan rana kaɗai ne suka zaga birnin sau bakwai.
But the seventh day, rising up early, they went about the city, as it was ordered, seven times.
16 A zagawa ta bakwai, da firistoci suka busa ƙahoni, sai Yoshuwa ya ba sojojin umarni ya ce, “Ku yi ihu, gama Ubangiji ya ba ku birnin!
And when in the seventh going about the priests sounded with the trumpets, Josue said to all Israel: Shout: for the Lord hath delivered the city to you:
17 Birnin da dukan abin da yake cikinta za a miƙa su ga Ubangiji. Rahab karuwan nan kaɗai ce, da dukan waɗanda suke tare da ita a gidanta za a bari da rai domin ta ɓoye’yan leƙen asirin ƙasa da muka aika.
And let this city be an anathema, and all things that are in it, to the Lord. Let only Rahab the harlot live, with all that are with her in the house: for she hid the messengers whom we sent.
18 Amma, ba za ku ɗauki wani abin da za a hallaka ba, idan kuka yi haka, za ku jawo masifa da hallaka a kan mutanen Isra’ila a inda kuka sauka.
But beware ye lest you touch ought of those things that are forbidden, and you be guilty of transgression, and all the camp of Israel be under sin, and be troubled.
19 Dukan azurfa da zinariya, da kwanonin tagulla da na ƙarfe, keɓaɓɓu ne ga Ubangiji, dole a sa su cikin ma’ajin Ubangiji.”
But whatsoever gold or silver there shall be, or vessels of brass and iron, let it be consecrated to the Lord, laid up in his treasures.
20 Da aka busa ƙahoni, sojoji suka yi ihu, da jin ƙarar ƙahoni, mutane suka kuma yi ihu, sai katangar ta rushe; dukan mutanen kuwa suka shiga birnin kai tsaye, suka yi nasara a kanta.
So all the people making a shout, and the trumpets sounding, when the voice and the sound thundered in the ears of the multitude, the walls forthwith fell down: and every man went up by the place that was over against him: and they took the city,
21 Suka miƙa wa Ubangiji birnin, suka hallaka kowane abu mai ran da yake cikin birnin da takobi, maza da mata, yara da tsofaffi, shanu, tumaki da jakuna.
And killed all that were in it, man and woman, young and old. The oxen also and the sheep, and the asses, they slew with the edge of the sword.
22 Yoshuwa ya ce wa mutanen nan biyu waɗanda suka je leƙen asirin ƙasar, “Ku shiga gidan karuwan nan ku fitar da ita da duk waɗanda suke nata bisa ga alkawarin da kuka yi mata.”
But Josue said to the two men that had been sent for spies: Go into the harlot’s house, and bring her out, and all things that are hers, as you assured her by oath.
23 Sai samarin waɗanda suka je leƙen asirin suka shiga suka fitar da Rahab, mahaifinta da mahaifiyarta, da’yan’uwanta da duk abin da yake nata. Suka fitar da iyalinta gaba ɗaya suka sa su a wani wuri, ba a cikin masauƙin Isra’ilawa ba.
And the young men went in and brought out Rahab, and her parents, her brethren also and all her goods and her kindred, and made them to stay without the camp.
24 Sa’an nan suka ƙona birnin tare da dukan abin da yake ciki tatas, amma suka sa azurfa da zinariya da kayan tagulla da na ƙarfe a cikin ma’aji na haikalin Ubangiji.
But they burned the city, and all things that were therein; except the gold and silver, and vessels of brass and iron, which they consecrated into the treasury of the Lord.
25 Amma Yoshuwa ya bar Rahab karuwan nan bai kashe ta ba, ita da iyalinta da duk abin da yake nata, domin ita ta ɓoye mutanen da Yoshuwa ya aika Yeriko don su leƙo asirin ƙasar kuma ta zauna tare da Isra’ilawa har wa yau.
But Josue saved Rahab the harlot and her father’s house, and all she had, and they dwelt in the midst of Israel until this present day: because she hid the messengers whom he had sent to spy out Jericho. At that time, Josue made an imprecation, saying:
26 A lokacin nan Yoshuwa ya yi wannan alkawari cewa, “Ubangiji zai tsine wa mutumin da zai yi ƙoƙarin sāke gina birnin nan, Yeriko. “A bakin ran ɗan farinsa zai kafa harsashin birnin; a bakin ran ɗan autansa kuma zai sa ƙofofin birnin.”
Cursed be the man before the Lord, that shall raise up and build the city of Jericho. In his firstborn may he lay the foundation thereof, and in the last of his children set up its gates.
27 Ubangiji ya kasance tare da Yoshuwa, aka kuma san da shi a duk fāɗin ƙasar.
And the Lord was with Josue, and his name was noised throughout all the land.