< Yoshuwa 5 >

1 To, da dukan sarakunan Amoriyawa na yammancin Urdun, da dukan sarakunan Kan’aniyawan da suke bakin teku suka ji yadda Ubangiji ya busar da kogin Urdun a gaban Isra’ilawa, har sai da dukansu suka ƙetare, zuciyarsu ta narke, suka karaya sosai har ma suka rasa samun ƙarfin hali su fuskanci Isra’ilawa.
Da nu alle amoritter-kongene som bodde på vestsiden av Jordan, og alle kana'anitter-kongene som bodde ved havet, hørte at Herren hadde latt Jordans vann tørke bort foran Israels barn inntil vi var kommet over, da blev deres hjerte fullt av angst, og de hadde ikke lenger mot til å møte Israels barn.
2 A lokacin nan Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka yi wuƙaƙe na duwatsu ka yi wa Isra’ilawa kaciya.”
På denne tid sa Herren til Josva: Gjør dig stenkniver og omskjær atter Israels barn, for annen gang!
3 Sai Yoshuwa ya yi wuƙaƙe na duwatsu, ya yi wa Isra’ilawa kaciya a Gibeyat-Ha’aralot.
Da gjorde Josva sig stenkniver og omskar Israels barn ved Ha'aralot-haugen.
4 Dalilin da ya sa ya yi haka shi ne, dukan waɗanda suka fito daga Masar, dukan mazan da suka kai shekarun shiga soja, sun mutu a cikin jeji a hanya bayan sun bar Masar.
Grunnen til at Josva omskar dem, var denne: Alt det folk som drog ut av Egypten - alle mennene, alle krigsfolkene - var død i ørkenen på veien fra Egypten.
5 Dukan mutanen da suka fito daga Masar an yi musu kaciya, amma duk waɗanda aka haifa a jeji a tafiya daga Masar, ba a yi musu ba.
Alt det folk som drog ut, var omskåret; men alt det folk som var født i ørkenen på veien fra Egypten, var ikke blitt omskåret.
6 Isra’ilawa sun yi tafiya a jeji shekaru arba’in, har sai da dukan mazan da suka kai shekarun shiga soja da suka bar Masar suka mutu, domin ba su yi wa Ubangiji biyayya ba. Gama Ubangiji ya rantse cewa ba zai bar su su ga ƙasar da ya yi wa iyayensu alkawari da rantsuwa cewa zai ba su ba, ƙasar da zuma da madara suke kwarara, ƙasar da take cike da albarka.
For i firti år vandret Israels barn i ørkenen, inntil alt folket - krigsfolkene som drog ut av Egypten - var utdød; de hørte ikke på Herrens røst, derfor svor Herren at han ikke vilde la dem se det land Herren hadde tilsvoret deres fedre å ville gi oss, et land som flyter med melk og honning.
7 Sai ya sa yaransu ne suka taso a maimakonsu, su ne waɗanda Yoshuwa ya yi wa kaciya. Sun kasance ba kaciya gama ba a yi musu ba a hanya.
Men deres barn, som han hadde latt vokse op i deres sted, dem omskar Josva; for de hadde forhud, da de ikke var blitt omskåret på veien.
8 Kuma bayan da aka yi wa al’ummar kaciya dukansu, sai suka dakata a nan, sai da suka warke.
Da hele folket således var blitt omskåret, holdt de sig i ro der hvor de var i leiren, til de blev friske igjen.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Yau na kawar muku da zargin Masar.” Saboda haka ake kiran sunan wurin Gilgal har wa yau.
Og Herren sa til Josva: Idag har jeg veltet av eder skammen fra Egypten. Siden har dette sted vært kalt Gilgal like til denne dag.
10 Da yamman rana ta goma sha huɗu ga wata, lokacin da suke a Gilgal a filin Yeriko, Isra’ilawa suka yi Bikin Ƙetarewa.
Mens Israels barn lå i leir ved Gilgal, holdt de påske den fjortende dag i måneden om aftenen på Jerikos ødemarker.
11 A kashegarin Bikin, a wannan rana, sai suka ci daga cikin amfanin ƙasar, burodi marar yisti da hatsin da aka gasa.
Og dagen efter påsken åt de av landets grøde; usyret brød og ristet korn åt de den dag.
12 Kashegari bayan da suka ci amfanin ƙasar kuwa, Manna ta yanke, mutanen Isra’ila kuma ba su ƙara samunta ba. A wannan shekara suka fara cin amfanin ƙasar Kan’ana.
Og mannaen hørte op dagen efter, for nu åt de av landets grøde; Israels barn fikk ikke mere manna, men de åt det år av det som var avlet i Kana'ans land.
13 To, da Yoshuwa ya yi kusa da Yeriko, ya tā da idanunsa ya duba, sai ya ga wani mutum tsaye a gabansa riƙe da takobi, sai Yoshuwa ya je wurinsa ya ce masa, “Kai namu ne ko na abokan gābanmu?”
Mens Josva var ved Jeriko, hendte det at han løftet op sine øine og fikk se en mann som stod foran ham med et draget sverd i sin hånd; og Josva gikk bort til ham og sa: Hører du til oss eller til våre fiender?
14 Mutumin ya ce, “Babu ko ɗaya, na dai zo ne a matsayin shugaban rundunar sojojin Ubangiji.” Sai Yoshuwa ya kwanta da fuskarsa har ƙasa, ya girmama shi, ya ce masa, “Ranka yă daɗe, wane saƙo kake da shi domin bawanka?”
Han svarte: Nei, jeg er høvdingen over Herrens hær; nu er jeg kommet. Da falt Josva på sitt ansikt til jorden og tilbad og sa til ham: Hvad har min herre å si til sin tjener?
15 Shugaban rundunar sojojin Ubangiji ya amsa ya ce, “Ka cire takalmanka, gama wurin da kake tsaye, mai tsarki ne.” Sai Yoshuwa ya cire takalmansa.
Og høvdingen over Herrens hær sa til Josva: Dra skoen av din fot! For det sted du står på, er hellig. Og Josva gjorde så.

< Yoshuwa 5 >