< Yoshuwa 5 >

1 To, da dukan sarakunan Amoriyawa na yammancin Urdun, da dukan sarakunan Kan’aniyawan da suke bakin teku suka ji yadda Ubangiji ya busar da kogin Urdun a gaban Isra’ilawa, har sai da dukansu suka ƙetare, zuciyarsu ta narke, suka karaya sosai har ma suka rasa samun ƙarfin hali su fuskanci Isra’ilawa.
When all the Amorite kings west of the Jordan and all the Canaanite kings of the Mediterranean coast heard how the Lord had dried up the waters of the River Jordan so that the Israelites could cross over, their courage melted and they no longer had any fighting spirit to face the Israelites.
2 A lokacin nan Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka yi wuƙaƙe na duwatsu ka yi wa Isra’ilawa kaciya.”
At that time the Lord told Joshua, “Make flint knives and circumcise the new generation of Israelites.”
3 Sai Yoshuwa ya yi wuƙaƙe na duwatsu, ya yi wa Isra’ilawa kaciya a Gibeyat-Ha’aralot.
Joshua had flint knives made and all male Israelites were circumcised at the place that became known as “the hill of foreskins.”
4 Dalilin da ya sa ya yi haka shi ne, dukan waɗanda suka fito daga Masar, dukan mazan da suka kai shekarun shiga soja, sun mutu a cikin jeji a hanya bayan sun bar Masar.
This is the reason why Joshua had them all circumcised: all those who left Egypt—the men of fighting age—had died on the journey through the wilderness after the Exodus.
5 Dukan mutanen da suka fito daga Masar an yi musu kaciya, amma duk waɗanda aka haifa a jeji a tafiya daga Masar, ba a yi musu ba.
They had all been circumcised when they left Egypt, but those born on the journey since then had not.
6 Isra’ilawa sun yi tafiya a jeji shekaru arba’in, har sai da dukan mazan da suka kai shekarun shiga soja da suka bar Masar suka mutu, domin ba su yi wa Ubangiji biyayya ba. Gama Ubangiji ya rantse cewa ba zai bar su su ga ƙasar da ya yi wa iyayensu alkawari da rantsuwa cewa zai ba su ba, ƙasar da zuma da madara suke kwarara, ƙasar da take cike da albarka.
For forty years the Israelites traveled through the wilderness until all the men of fighting age when they left Egypt had died, because they had not done what the Lord had told them to do. So the Lord had vowed that he would not let them see the land he had promised their forefathers to give us, a land flowing with milk and honey.
7 Sai ya sa yaransu ne suka taso a maimakonsu, su ne waɗanda Yoshuwa ya yi wa kaciya. Sun kasance ba kaciya gama ba a yi musu ba a hanya.
The Lord replaced them with their children, and these were the ones that Joshua circumcised. They were uncircumcised since they hadn't been circumcised on the way.
8 Kuma bayan da aka yi wa al’ummar kaciya dukansu, sai suka dakata a nan, sai da suka warke.
Once they had all been circumcised, they stayed in the camp until they recovered.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Yau na kawar muku da zargin Masar.” Saboda haka ake kiran sunan wurin Gilgal har wa yau.
The Lord said to Joshua, “Today I have removed from all of you the disgrace of Egypt.” So that place has been called Gilgal to this day.
10 Da yamman rana ta goma sha huɗu ga wata, lokacin da suke a Gilgal a filin Yeriko, Isra’ilawa suka yi Bikin Ƙetarewa.
The Israelites camped at Gilgal and celebrated Passover there on the evening of the fourteenth day of the first month.
11 A kashegarin Bikin, a wannan rana, sai suka ci daga cikin amfanin ƙasar, burodi marar yisti da hatsin da aka gasa.
From the very next day they began to eat produce from the land: unleavened bread and roasted grain.
12 Kashegari bayan da suka ci amfanin ƙasar kuwa, Manna ta yanke, mutanen Isra’ila kuma ba su ƙara samunta ba. A wannan shekara suka fara cin amfanin ƙasar Kan’ana.
On the same day when they began eating produce from the land there was no more manna. No longer did the Israelites have manna; after that they ate the produce of the land of Canaan.
13 To, da Yoshuwa ya yi kusa da Yeriko, ya tā da idanunsa ya duba, sai ya ga wani mutum tsaye a gabansa riƙe da takobi, sai Yoshuwa ya je wurinsa ya ce masa, “Kai namu ne ko na abokan gābanmu?”
One day when Joshua was near Jericho, he looked up and saw a man standing in front of him with a drawn sword in his hand. Joshua went up to him and asked, “Are you for us or against us?” “Neither,” said the man. “I am the commander of the Lord's army. Now I'm here!”
14 Mutumin ya ce, “Babu ko ɗaya, na dai zo ne a matsayin shugaban rundunar sojojin Ubangiji.” Sai Yoshuwa ya kwanta da fuskarsa har ƙasa, ya girmama shi, ya ce masa, “Ranka yă daɗe, wane saƙo kake da shi domin bawanka?”
Joshua fell down with his face to the ground in awe. Then he said, “What orders does my lord have for his servant?”
15 Shugaban rundunar sojojin Ubangiji ya amsa ya ce, “Ka cire takalmanka, gama wurin da kake tsaye, mai tsarki ne.” Sai Yoshuwa ya cire takalmansa.
The commander of the Lord's army told Joshua, “Take off your sandals, for the place where you're standing is holy ground.” Joshua did so.

< Yoshuwa 5 >