< Yoshuwa 5 >

1 To, da dukan sarakunan Amoriyawa na yammancin Urdun, da dukan sarakunan Kan’aniyawan da suke bakin teku suka ji yadda Ubangiji ya busar da kogin Urdun a gaban Isra’ilawa, har sai da dukansu suka ƙetare, zuciyarsu ta narke, suka karaya sosai har ma suka rasa samun ƙarfin hali su fuskanci Isra’ilawa.
Therefore, after all the kings of the Amorites, who were living across the Jordan toward the western region, and all the kings of Canaan, who possessed the places beside the great sea, had heard that the Lord had dried up the waters of the Jordan before the sons of Israel, until they crossed over it, their heart was broken, and there remained in them no spirit, out of fear at the entrance of the sons of Israel.
2 A lokacin nan Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka yi wuƙaƙe na duwatsu ka yi wa Isra’ilawa kaciya.”
So at that time, the Lord said to Joshua: “Make for yourself knives of stone, and circumcise the sons of Israel a second time.”
3 Sai Yoshuwa ya yi wuƙaƙe na duwatsu, ya yi wa Isra’ilawa kaciya a Gibeyat-Ha’aralot.
He did what the Lord had commanded, and he circumcised the sons of Israel at the hill of the foreskins.
4 Dalilin da ya sa ya yi haka shi ne, dukan waɗanda suka fito daga Masar, dukan mazan da suka kai shekarun shiga soja, sun mutu a cikin jeji a hanya bayan sun bar Masar.
Now this is the reason for the second circumcision: All the people who departed from Egypt of the male gender, all the men fit for war, died in the desert during the very long wandering way;
5 Dukan mutanen da suka fito daga Masar an yi musu kaciya, amma duk waɗanda aka haifa a jeji a tafiya daga Masar, ba a yi musu ba.
all these had been circumcised. But the people who were born in the desert,
6 Isra’ilawa sun yi tafiya a jeji shekaru arba’in, har sai da dukan mazan da suka kai shekarun shiga soja da suka bar Masar suka mutu, domin ba su yi wa Ubangiji biyayya ba. Gama Ubangiji ya rantse cewa ba zai bar su su ga ƙasar da ya yi wa iyayensu alkawari da rantsuwa cewa zai ba su ba, ƙasar da zuma da madara suke kwarara, ƙasar da take cike da albarka.
throughout the forty years of the journey in the very broad wilderness, were uncircumcised, until the ones who had not listened to the voice of the Lord were consumed. For he had sworn to them before, that he would not reveal to them the land flowing with milk and honey.
7 Sai ya sa yaransu ne suka taso a maimakonsu, su ne waɗanda Yoshuwa ya yi wa kaciya. Sun kasance ba kaciya gama ba a yi musu ba a hanya.
The sons of these ones succeeded to the place of their fathers, and they were circumcised by Joshua. For they were uncircumcised, just as they had been born, and no one had circumcised them along the way.
8 Kuma bayan da aka yi wa al’ummar kaciya dukansu, sai suka dakata a nan, sai da suka warke.
Then, after they were all circumcised, they remained in the same place of the camp until they were healed.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Yau na kawar muku da zargin Masar.” Saboda haka ake kiran sunan wurin Gilgal har wa yau.
And the Lord said to Joshua, “Today I have taken away from you the disgrace of Egypt.” And the name of that place was called Gilgal, even to the present day.
10 Da yamman rana ta goma sha huɗu ga wata, lokacin da suke a Gilgal a filin Yeriko, Isra’ilawa suka yi Bikin Ƙetarewa.
And the sons of Israel stayed at Gilgal, and they kept the Passover, on the fourteenth day of the month at evening, in the plains of Jericho.
11 A kashegarin Bikin, a wannan rana, sai suka ci daga cikin amfanin ƙasar, burodi marar yisti da hatsin da aka gasa.
And on the following day, they ate unleavened bread from the grain of the land, and cooked grain, of the same year.
12 Kashegari bayan da suka ci amfanin ƙasar kuwa, Manna ta yanke, mutanen Isra’ila kuma ba su ƙara samunta ba. A wannan shekara suka fara cin amfanin ƙasar Kan’ana.
And the manna ceased after they ate from the grain of the land. And the sons of Israel no longer made use of that food. Instead, they ate from the grain of the present year, from the land of Canaan.
13 To, da Yoshuwa ya yi kusa da Yeriko, ya tā da idanunsa ya duba, sai ya ga wani mutum tsaye a gabansa riƙe da takobi, sai Yoshuwa ya je wurinsa ya ce masa, “Kai namu ne ko na abokan gābanmu?”
And when Joshua was in the field of the city of Jericho, he lifted up his eyes, and he saw a man standing opposite him, holding a drawn sword. And he went to him and said, “Are you one of ours, or one of our adversaries?”
14 Mutumin ya ce, “Babu ko ɗaya, na dai zo ne a matsayin shugaban rundunar sojojin Ubangiji.” Sai Yoshuwa ya kwanta da fuskarsa har ƙasa, ya girmama shi, ya ce masa, “Ranka yă daɗe, wane saƙo kake da shi domin bawanka?”
And he responded: “Not at all. Instead, I am a prince of the host of the Lord, and now I have arrived.” Joshua fell prone on the ground. And reverencing, he said, “What does my lord say to his servant?”
15 Shugaban rundunar sojojin Ubangiji ya amsa ya ce, “Ka cire takalmanka, gama wurin da kake tsaye, mai tsarki ne.” Sai Yoshuwa ya cire takalmansa.
He said: “Remove your shoes from your feet. For the place on which you stand is holy.” And Joshua did just as he had been commanded.

< Yoshuwa 5 >