< Yoshuwa 5 >
1 To, da dukan sarakunan Amoriyawa na yammancin Urdun, da dukan sarakunan Kan’aniyawan da suke bakin teku suka ji yadda Ubangiji ya busar da kogin Urdun a gaban Isra’ilawa, har sai da dukansu suka ƙetare, zuciyarsu ta narke, suka karaya sosai har ma suka rasa samun ƙarfin hali su fuskanci Isra’ilawa.
Og det skete, der alle Amoriternes Konger, som boede paa hin Side Jordanen imod Vesten, og alle Kananiternes Konger, som boede ved Havet, hørte, at Herren havde udtørret Jordanens Vande for Israels Børns Ansigt, indtil de kom over, da blev deres Hjerte mistrøstigt, og der var ikke ydermere Mod i dem for Israels Børns Ansigt.
2 A lokacin nan Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka yi wuƙaƙe na duwatsu ka yi wa Isra’ilawa kaciya.”
Paa den Tid sagde Herren til Josva: Gør dig Stenknive og omskær Israels Børn igen anden Gang.
3 Sai Yoshuwa ya yi wuƙaƙe na duwatsu, ya yi wa Isra’ilawa kaciya a Gibeyat-Ha’aralot.
Da gjorde Josva sig Stenknive og omskar Israels Børn ved Araloths Høj.
4 Dalilin da ya sa ya yi haka shi ne, dukan waɗanda suka fito daga Masar, dukan mazan da suka kai shekarun shiga soja, sun mutu a cikin jeji a hanya bayan sun bar Masar.
Og dette er Sagen, hvorfor Josva omskar dem: Alt Folket af Mandkøn, som var udgaaet af Ægypten, alt Krigsfolket var død i Ørken paa Vejen, siden de gik ud af Ægypten.
5 Dukan mutanen da suka fito daga Masar an yi musu kaciya, amma duk waɗanda aka haifa a jeji a tafiya daga Masar, ba a yi musu ba.
Thi alt Folket, som udgik, var omskaaret; men alt Folket, som var født i Ørken paa Vejen, siden de udgik af Ægypten, havde de ikke omskaaret.
6 Isra’ilawa sun yi tafiya a jeji shekaru arba’in, har sai da dukan mazan da suka kai shekarun shiga soja da suka bar Masar suka mutu, domin ba su yi wa Ubangiji biyayya ba. Gama Ubangiji ya rantse cewa ba zai bar su su ga ƙasar da ya yi wa iyayensu alkawari da rantsuwa cewa zai ba su ba, ƙasar da zuma da madara suke kwarara, ƙasar da take cike da albarka.
Thi Israels Børn vandrede fyrretyve Aar i Ørken, indtil alt det Folk, Krigsfolket, som udgik af Ægypten, var uddød, de som ikke havde hørt Herrens Røst, saa at Herren svor dem, at han ikke vilde lade dem se det Land, som Herren havde tilsvoret deres Fædre at give os, et Land, som flyder med Mælk og Honning.
7 Sai ya sa yaransu ne suka taso a maimakonsu, su ne waɗanda Yoshuwa ya yi wa kaciya. Sun kasance ba kaciya gama ba a yi musu ba a hanya.
Og han oprejste deres Børn i deres Sted; dem omskar Josva, thi de havde Forhud, eftersom man ikke havde omskaaret dem paa Vejen.
8 Kuma bayan da aka yi wa al’ummar kaciya dukansu, sai suka dakata a nan, sai da suka warke.
Og det skete, der de vare færdige med at omskære alt Folket, da bleve de paa deres Sted i Lejren, indtil de bleve karske.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Yau na kawar muku da zargin Masar.” Saboda haka ake kiran sunan wurin Gilgal har wa yau.
Og Herren sagde til Josva: I Dag har jeg afvæltet Ægyptens Skændsel fra eder; og man kaldte samme Steds Navn Gilgal indtil denne Dag.
10 Da yamman rana ta goma sha huɗu ga wata, lokacin da suke a Gilgal a filin Yeriko, Isra’ilawa suka yi Bikin Ƙetarewa.
Og Israels Børn lejrede sig i Gilgal, og de holdt Paaske den fjortende Dag i Maaneden om Aftenen, paa Jerikos slette Marker.
11 A kashegarin Bikin, a wannan rana, sai suka ci daga cikin amfanin ƙasar, burodi marar yisti da hatsin da aka gasa.
Og de aade af Landets Grøde fra anden Paaskedag, nemlig usyrede Brød og ristede Aks, paa selvsamme Dag.
12 Kashegari bayan da suka ci amfanin ƙasar kuwa, Manna ta yanke, mutanen Isra’ila kuma ba su ƙara samunta ba. A wannan shekara suka fara cin amfanin ƙasar Kan’ana.
Saa holdt Mannaen op, anden Dag efter at de havde ædt af Landets Grøde, og Israels Børn havde ikke ydermere Manna; men de aade af Kanaans Lands nye Grøde i samme Aar.
13 To, da Yoshuwa ya yi kusa da Yeriko, ya tā da idanunsa ya duba, sai ya ga wani mutum tsaye a gabansa riƙe da takobi, sai Yoshuwa ya je wurinsa ya ce masa, “Kai namu ne ko na abokan gābanmu?”
Og det skete, der Josva var ved Jeriko, at han opløftede sine Øjne og saa, og se, en Mand stod lige imod ham og havde sit dragne Sværd i sin Haand; og Josva gik til ham og sagde til ham: Hører du os til eller vore Fjender?
14 Mutumin ya ce, “Babu ko ɗaya, na dai zo ne a matsayin shugaban rundunar sojojin Ubangiji.” Sai Yoshuwa ya kwanta da fuskarsa har ƙasa, ya girmama shi, ya ce masa, “Ranka yă daɗe, wane saƙo kake da shi domin bawanka?”
Og han sagde: Nej! men jeg er en Fyrste over Herrens Hær, nu kom jeg! Da faldt Josva paa sit Ansigt til Jorden og tilbad og sagde til ham: Hvad taler min Herre til sin Tjener?
15 Shugaban rundunar sojojin Ubangiji ya amsa ya ce, “Ka cire takalmanka, gama wurin da kake tsaye, mai tsarki ne.” Sai Yoshuwa ya cire takalmansa.
Og Fyrsten over Herrens Hær sagde til Josva: Drag din Sko af din Fod, thi det Sted, som du staar paa, det er helligt; og Josva gjorde saa.