< Yoshuwa 4 >

1 Da al’umma gaba ɗaya suka ƙetare Urdun, Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
وقتی همۀ افراد قوم اسرائیل به سلامت از رودخانه گذشتند، خداوند به یوشع فرمود:
2 “Ka zaɓi mutum goma sha biyu daga cikin mutane, ɗaya daga kowace kabila,
«اکنون به آن دوازده نفر که از دوازده قبیله انتخاب شده‌اند
3 ka ce musu kowa yă ɗauki dutse ɗaya daga tsakiyar Urdun daidai inda firistoci suka tsaya, ku kai su, ku ajiye a inda za ku sauka yau.”
بگو که بروند و دوازده سنگ از وسط رودخانه، جایی که کاهنان آنجا ایستاده‌اند، بیرون بیاورند و آن سنگها را با خود به همان مکانی ببرند که امشب اردو می‌زنند تا به عنوان یادبود، آنها را روی هم قرار دهند.»
4 Sai Yoshuwa ya kira mutum goma sha biyu da ya zaɓa daga cikin Isra’ilawa, ɗaya daga kowace kabila
پس یوشع آن دوازده نفر را که از میان بنی‌اسرائیل انتخاب کرده بود، فرا خواند
5 ya ce musu, “Ku je tsakiyar Urdun inda akwatin alkawari na Ubangiji Allahnku yake. Kowannenku yă ɗauki dutse ɗaya a kafaɗarsa, bisa ga yawan kabilan Isra’ila,
و به ایشان گفت: «به میان رودخانه، جایی که کاهنان با صندوق عهد یهوه خدایتان ایستاده‌اند، بروید و هر یک از شما یک سنگ بر دوش خود بگذارید و بیاورید، یعنی دوازده سنگ به تعداد دوازده قبیلهٔ اسرائیل.
6 yă zama muku alama. Nan gaba in yaranku suka tambaye ku suka ce, ‘Mece ce ma’anar kasancewar duwatsun nan a nan?’
ما آنها را به عنوان یادبود در اینجا می‌گذاریم تا وقتی در آینده فرزندانتان بپرسند: این سنگها چیست؟
7 Sai ku ce musu, ruwan Urdun ya yanke a gaban akwatin alkawari na Ubangiji, a lokacin da akwatin alkawarin ya ƙetare Urdun. Waɗannan duwatsu za su zama abin tuni ga Isra’ilawa har abada.”
به آنها بگویید که این یادگار روزی است که جریان آب رود اردن قطع شد و در میان آن، راه خشکی پدید آمد تا صندوق عهد خداوند از آن عبور کند! این سنگها برای قوم اسرائیل یادگاری جاودانه از این معجزهٔ بزرگ خواهند بود.»
8 Isra’ilawa kuwa suka yi yadda Yoshuwa ya umarce su. Suka ɗauki duwatsu guda goma sha biyu bisa ga yawan kabilan Isra’ila, yadda Ubangiji ya gaya wa Yoshuwa; suka tafi da su masauƙinsu, a can suka ajiye su.
آن دوازده نفر طبق دستور یوشع عمل نمودند و دوازده سنگ از وسط رودخانه آوردند، درست همان‌گونه که خداوند به یوشع فرموده بود، یعنی برای هر قبیلۀ اسرائیل یک سنگ. سنگها را به محلی که در آنجا توقف نموده بودند بردند و یادبودی بنا کردند.
9 Yoshuwa ya ɗora duwatsu goma sha biyun a tsakiyar Urdun daidai inda firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji suka tsaya. Suna nan a can har wa yau.
یوشع در وسط رودخانه، جایی که کاهنان ایستاده بودند نیز دوازده سنگ دیگر به عنوان یادگار روی هم گذاشت که تا به امروز باقیست.
10 Firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawari suka tsaya a tsakiyar Urdun, har aka gama dukan abin da Ubangiji ya umarci Yoshuwa yă gaya wa mutane, kamar yadda Musa ya ce Yoshuwa yă yi. Mutanen suka wuce da sauri.
کاهنان با صندوق عهد آنقدر در وسط رودخانه ماندند تا قوم اسرائیل آنچه را که خداوند به یوشع فرموده بود به انجام رساندند، درست همان‌گونه که موسی به یوشع توصیه کرده بود. پس قوم اسرائیل با شتاب از رود اردن گذشتند،
11 Sai da dukan mutanen suka wuce sa’an nan akwatin alkawari da firistoci suka sha gaba.
و پس از آنکه به آن سوی رودخانه رسیدند، کاهنان هم با صندوق عهد خداوند از رودخانه بیرون آمدند.
12 Mutanen Ruben, Gad da rabin kabilar Manasse suka ƙetare da shirin yaƙi, suka wuce gaban Isra’ila kamar yadda Musa ya ce su yi.
مردان جنگی قبایل رئوبین، جاد و نصف قبیلهٔ منسی که چهل هزار نفر بودند مسلح شدند و چنانکه موسی پیش از فوت خود به ایشان گفته بود، پیشاپیش بقیهٔ قوم عبور کرده، در حضور خداوند، به سوی دشت اریحا پیش رفتند.
13 Wajen mutum dubu arba’in shirye domin yaƙi, suka wuce a gaban Ubangiji zuwa filayen Yeriko.
14 A ranan nan Ubangiji ya ɗaukaka Yoshuwa a gaban Isra’ilawa; suka kuma ba shi girma dukan kwanakin ransa, kamar yadda suka girmama Musa.
در آن روز، خداوند یوشع را در نظر تمام قوم اسرائیل سرافراز نمود. قوم اسرائیل، یوشع را در تمام مدت عمرش مانند موسی احترام می‌کردند.
15 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
یوشع به امر خداوند به کاهنانی که صندوق عهد را حمل می‌کردند گفت: «از بستر رود اردن بیرون بیایید.»
16 “Ka umarci firistocin da suke ɗauke da akwatin Shaida su fito daga cikin Urdun.”
17 Sai Yoshuwa ya umarci firistoci ya ce, “Ku fito daga cikin Urdun.”
18 Firistocin kuwa suka fito daga kogin ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji. Nan da nan da ƙafafunsu suka taɓa busasshiyar ƙasa, sai ruwan Urdun ya gangaro ya cika kogin kamar yadda yake a dā.
به محض اینکه کاهنان بیرون آمدند، آب رودخانه دوباره به جریان افتاد و مانند قبل بر کناره‌هایش نیز جاری شد.
19 A rana ta goma ga wata na farko, mutane suka haura daga Urdun suka sauka a Gilgal a gabashin iyakar Yeriko.
این معجزه در روز دهم ماه اول اتفاق افتاد. آن روز، تمام مردم اسرائیل از رود اردن گذشتند و در جلجال، در سمت شرقی شهر اریحا اردو زدند.
20 Sai Yoshuwa ya kafa duwatsu goma sha biyun nan da suka ɗauko daga Urdun.
آنجا در جلجال یوشع دوازده سنگی را که از وسط رودخانه آورده بود، به عنوان یادبود روی هم گذاشت.
21 Ya ce wa Isra’ilawa, “Nan gaba in yaranku suka tambayi iyayensu suka ce, ‘Mece ce ma’anar waɗannan duwatsun?’
بار دیگر یوشع مفهوم آن سنگها را برای قوم اسرائیل بیان کرد: «در آینده اگر فرزندانتان بپرسند: این تودۀ سنگها در اینجا برای چیست؟
22 Ku ce musu, ‘Isra’ilawa sun ƙetare kogin Urdun a kan busasshiyar ƙasa.’
به آنها بگویید که این سنگها یادآور عبور معجزآسای قوم اسرائیل از میان رود اردن است!»
23 Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruwan Urdun ya yanke a gabanku, har sai da kuka gama wucewa, kamar yadda ya yi a Jan Teku, a lokacin da ya busar da shi a gabanmu har sai da muka gama wucewa.
برای ایشان توضیح دهید که چگونه خداوند جریان آب را قطع کرد و از وسط رودخانه، راه خشکی پدید آورد تا همهٔ شما عبور کنید! این شبیه معجزه‌ای است که خداوند چهل سال قبل انجام داد، وقتی دریای سرخ را شکافت و از وسط آن، راه خشکی برای عبور بنی‌اسرائیل پدید آورد.
24 Ya yi wannan ne domin dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji mai iko ne, domin kuma ku zama masu tsoron Ubangiji Allahnku.”
خداوند این معجزه را انجام داد تا همهٔ مردم جهان بدانند که قدرت او عظیم است و همچنین شما نیز همیشه او را اطاعت کنید.

< Yoshuwa 4 >