< Yoshuwa 4 >

1 Da al’umma gaba ɗaya suka ƙetare Urdun, Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
And it was just when they had finished all the nation to pass over the Jordan. And he said Yahweh to Joshua saying.
2 “Ka zaɓi mutum goma sha biyu daga cikin mutane, ɗaya daga kowace kabila,
Take for yourselves from the people two [plus] ten men a man one a man one from a tribe.
3 ka ce musu kowa yă ɗauki dutse ɗaya daga tsakiyar Urdun daidai inda firistoci suka tsaya, ku kai su, ku ajiye a inda za ku sauka yau.”
And command them saying take up for yourselves from here from [the] middle of the Jordan from [the] standing-place of [the] feet of the priests to make firm two [plus] ten stones and you will take over them with you and you will set down them at the lodging place which you will stay at it this night.
4 Sai Yoshuwa ya kira mutum goma sha biyu da ya zaɓa daga cikin Isra’ilawa, ɗaya daga kowace kabila
And he called Joshua to two [plus] the ten man whom he had appointed from [the] people of Israel a man one a man one from a tribe.
5 ya ce musu, “Ku je tsakiyar Urdun inda akwatin alkawari na Ubangiji Allahnku yake. Kowannenku yă ɗauki dutse ɗaya a kafaɗarsa, bisa ga yawan kabilan Isra’ila,
And he said to them Joshua pass over before [the] ark of Yahweh God your into [the] middle of the Jordan and take up for yourselves each a stone one on shoulder his to [the] number of [the] tribes of [the] people of Israel.
6 yă zama muku alama. Nan gaba in yaranku suka tambaye ku suka ce, ‘Mece ce ma’anar kasancewar duwatsun nan a nan?’
So that it may be this a sign in midst your if they will ask! children your tomorrow saying what? [are] the stones these to you.
7 Sai ku ce musu, ruwan Urdun ya yanke a gaban akwatin alkawari na Ubangiji, a lokacin da akwatin alkawarin ya ƙetare Urdun. Waɗannan duwatsu za su zama abin tuni ga Isra’ilawa har abada.”
And you will say to them that they were cut off [the] waters of the Jordan from before [the] ark of [the] covenant of Yahweh when passed on it in the Jordan they were cut off [the] waters of the Jordan and they will become the stones these a reminder to [the] people of Israel until perpetuity.
8 Isra’ilawa kuwa suka yi yadda Yoshuwa ya umarce su. Suka ɗauki duwatsu guda goma sha biyu bisa ga yawan kabilan Isra’ila, yadda Ubangiji ya gaya wa Yoshuwa; suka tafi da su masauƙinsu, a can suka ajiye su.
And they did thus [the] people of Israel just as he had commanded Joshua and they took up two [plus] ten stones from [the] middle of the Jordan just as he had said Yahweh to Joshua to [the] number of [the] tribes of [the] people of Israel and they took over them with them to the lodging place and they set down them there.
9 Yoshuwa ya ɗora duwatsu goma sha biyun a tsakiyar Urdun daidai inda firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji suka tsaya. Suna nan a can har wa yau.
And two [plus] ten stones he set up Joshua in [the] middle of the Jordan in [the] standing-place of [the] feet of the priests [the] bearers of [the] ark of the covenant and they have been there until the day this.
10 Firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawari suka tsaya a tsakiyar Urdun, har aka gama dukan abin da Ubangiji ya umarci Yoshuwa yă gaya wa mutane, kamar yadda Musa ya ce Yoshuwa yă yi. Mutanen suka wuce da sauri.
And the priests [the] bearers of the ark [were] standing in [the] middle of the Jordan until was finished every thing which he had commanded Yahweh Joshua to speak to the people according to all that he had commanded Moses Joshua and they hurried the people and they passed over.
11 Sai da dukan mutanen suka wuce sa’an nan akwatin alkawari da firistoci suka sha gaba.
And it was just when it had finished all the people to pass over and it passed over [the] ark of Yahweh and the priests before the people.
12 Mutanen Ruben, Gad da rabin kabilar Manasse suka ƙetare da shirin yaƙi, suka wuce gaban Isra’ila kamar yadda Musa ya ce su yi.
And they passed over [the] descendants of Reuben and [the] descendants of Gad and [the] half of [the] tribe of Manasseh arrayed for battle before [the] people of Israel just as he had spoken to them Moses.
13 Wajen mutum dubu arba’in shirye domin yaƙi, suka wuce a gaban Ubangiji zuwa filayen Yeriko.
About forty thousand armed [men] of war they passed over before Yahweh for battle to [the] plains of Jericho.
14 A ranan nan Ubangiji ya ɗaukaka Yoshuwa a gaban Isra’ilawa; suka kuma ba shi girma dukan kwanakin ransa, kamar yadda suka girmama Musa.
On the day that he made great Yahweh Joshua in [the] eyes of all Israel and they feared him just as they had feared Moses all [the] days of life his.
15 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
And he said Yahweh to Joshua saying.
16 “Ka umarci firistocin da suke ɗauke da akwatin Shaida su fito daga cikin Urdun.”
Command the priests [the] bearers of [the] ark of the testimony so they may come up from the Jordan.
17 Sai Yoshuwa ya umarci firistoci ya ce, “Ku fito daga cikin Urdun.”
And he commanded Joshua the priests saying come up from the Jordan.
18 Firistocin kuwa suka fito daga kogin ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji. Nan da nan da ƙafafunsu suka taɓa busasshiyar ƙasa, sai ruwan Urdun ya gangaro ya cika kogin kamar yadda yake a dā.
And it was (just as came up *Q(K)*) the priests [the] bearers of [the] ark of [the] covenant of Yahweh from [the] middle of the Jordan they were drawn out [the] soles of [the] feet of the priests to the dry ground and they returned [the] waters of the Jordan to place their and they went as yesterday three days ago over all banks its.
19 A rana ta goma ga wata na farko, mutane suka haura daga Urdun suka sauka a Gilgal a gabashin iyakar Yeriko.
And the people they went up from the Jordan on the ten of the month first and they encamped at Gilgal on [the] edge of [the] east of Jericho.
20 Sai Yoshuwa ya kafa duwatsu goma sha biyun nan da suka ɗauko daga Urdun.
And two [plus] ten the stones these which they had taken from the Jordan he set up Joshua at Gilgal.
21 Ya ce wa Isra’ilawa, “Nan gaba in yaranku suka tambayi iyayensu suka ce, ‘Mece ce ma’anar waɗannan duwatsun?’
And he said to [the] people of Israel saying that they will ask! children your tomorrow fathers their saying what? [are] the stones these.
22 Ku ce musu, ‘Isra’ilawa sun ƙetare kogin Urdun a kan busasshiyar ƙasa.’
And you will make known to children your saying on the dry ground it passed over Israel the Jordan this.
23 Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruwan Urdun ya yanke a gabanku, har sai da kuka gama wucewa, kamar yadda ya yi a Jan Teku, a lokacin da ya busar da shi a gabanmu har sai da muka gama wucewa.
That he dried up Yahweh God your [the] waters of the Jordan from before you until had passed over you just as he did Yahweh God your to [the] sea of reed[s] which he dried up from before us until had passed over we.
24 Ya yi wannan ne domin dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji mai iko ne, domin kuma ku zama masu tsoron Ubangiji Allahnku.”
So as to know all [the] peoples of the earth [the] hand of Yahweh that [is] mighty it so that you may fear Yahweh God your all the days.

< Yoshuwa 4 >