< Yoshuwa 3 >
1 Kashegari Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Shittim suka nufi Urdun inda suka sauka kafin su haye.
Nañaleñale t’Iehosoa te nitroatse, le nienga i Sitime rekets’ o ana’ Israele iabio naho niheo mb’am’ Iardeney mb’eo, vaho nitobe eo aolo’ t’ie hitsake.
2 Bayan kwana uku sai shugabannin suka zazzaga sansani, suna
Ie nimodo ty telo andro, le nimb’eo mb’eo amy tobey o mpiaoloo;
3 ba da umarni ga mutane, suna cewa, “Lokacin da kuka ga akwatin alkawari na Ubangiji Allahnku, da firistoci waɗanda su ne Lawiyawa, suna ɗauke da shi, sai ku tashi daga inda kuke, ku bi shi.
naho linili’ iareo ondatio ami’ty hoe: Naho oni’ areo i vatam-pañina’ Iehovà Andrianañahare’ areoy, naho o mpisoroñe nte-Levy mitarazo azeo, le miavota an-toe’o, vaho oriho.
4 A ta haka za ku san inda za ku bi, gama ba ku taɓa bin hanyar ba. Sai dai ku ɗan ba da rata wajen yadi ɗari tara tsakaninku da akwatin alkawari, kada ku kusace shi.”
Fe engao heba’e mizehe kiho ro’arivo varañe añivo’ areo naho ie, ko harinea’ areo, soa te ho fohi’ areo ty lalan-komba’ areo; fa mboe tsy niary mb’ atoy nahareo.
5 Yoshuwa ya ce wa mutane, “Ku tsarkake kanku, gama gobe Ubangiji zai yi abubuwan al’ajabi a cikinku.”
Le hoe t’Iehosoa am’ ondatio: Miefera fa hanao raha tsitantane añivo’ areo ao t’Iehovà hamaray.
6 Yoshuwa ya ce wa firistoci, “Ku ɗauki akwatin alkawari ku sha gaba.” Sai suka ɗauki akwatin alkawari suka wuce gaban sauran jama’a.
Nisaontsy amo mpisoroñeo t’Iehosoa ami’ty hoe: Rambeso i vatam-pañinay le mitsàha aolo ondatio. Rinambe’ iereo i vatam-pañinay vaho nimb’ aolo ondatio mb’eo.
7 Ubangiji kuwa ya ce wa Yoshuwa, “Yau, zan fara ɗaukaka ka a gaban Isra’ilawa duka don su sani cewa ina tare da kai kamar yadda na kasance tare da Musa.
Le hoe t’Iehovà am’ Iehosoa, Hiorotse hampionjoñe azo ampahaoniña’ Israele iaby iraho te anito, hahafohina’ iareo te, manahake ty nindrezako amy Mosè ty hindrezako ama’o.
8 Ka ce wa firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawari, ‘Sa’ad da kuka kai bakin Urdun, ku shiga cikin ruwan ku tsaya.’”
Aa le afantoho o mpisoroñe mitarazo i vatam-pañinaio, ami’ty hoe: Ie tsatok’ añ’olon-drano’ Iardeney le mijohaña am’ Iardeney.
9 Yoshuwa ya ce wa Isra’ilawa, “Ku zo nan ku ji maganar Ubangiji Allahnku.
Le hoe t’Iehosoa amo ana’ Israeleo: Mb’etoa hijanjiñe ty tsara’ Iehovà Andrianañahare’ areo.
10 Ta haka ne za ku san cewa Allah mai rai yana tare da ku, kuma ba shakka a gabanku za ku gani zai kore Kan’aniyawa, Hittiyawa, Hiwiyawa, Ferizziyawa, Girgashiyawa, Amoriyawa da Yebusiyawa.
Le hoe t’Iehosoa: Ho fohi’ areo henane zao te añivo’ areo ao t’i Andrianañahare veloñe le tsy mete tsy roahe’e aolo’ areo mb’eo o nte-Kanàneo, naho o nte Kiteo, naho o nte-Kiveo, naho o nte-Perizeo, naho o nte-Girgasio, naho o nte-Amoreo vaho o nte-Iebosio.
11 Ku duba, akwatin alkawarin Ubangiji na dukan duniya zai yi gaba cikin Urdun kafin ku.
Hehe te mitsak’ aolo’ areo mb’ am’ Iardeney ty vatam-pañina’ i Talè’ ty tane toy iaby.
12 Yanzu sai ku zaɓi mutum goma sha biyu daga kabilan Isra’ila, ɗaya daga kowace kabila.
Aa le joboño ondaty folo-ro’ amby boak’ amy fifokoa’ Israele rey, songa ondaty raike i fifokoañe rey.
13 Kuma da firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji, Ubangiji dukan duniya, sun sa ƙafa cikin ruwan kogin Urdun, ruwan da yake gudu a rafin zai tsaya cik yă taru a wuri ɗaya.”
Amy te, ie mijohañe an-drano’ Iardeney ty lelam-pandia’ o mpisoroñe mitarazo i vatam-pañina’ Iehovà, Talè’ ty tane bey toiio, le ho tampake ty rano’ Iardeney vaho hivotry ho haboañe o rano mikararake boak’ ambone añeo.
14 Saboda haka sa’ad da mutanen suka tashi don su ƙetare Urdun, firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawarin suka sha gaba.
Aa naho niavotse an-kiboho’e ondatio hitsake Iardeney, le aolo ondatio o mpisoroñe nitarazo i vatam-pañinaio,
15 Da kaka Urdun yakan cika makil da ruwa. Duk da haka da zarar firistoci masu ɗauke da akwatin alkawari suka tsoma ƙafafunsu a gefen ruwa,
le vata’e nivotrak’ añ’ olo-drano’ Iardeney ty fandia’ o mpitarazo i vatam-pañinaio—toe manganahana añ’olo’ Iardeney iaby o rano’ Iardeneio amo hene andro an-tsam-pamokarañeo—
16 sai ruwan da yake gangarowa ya tsaya, ya tattaru a wuri ɗaya ya yi tudu daga nan har zuwa wani garin da ake kira Adam kusa da Zaretan, ruwan da yake gangarowa zuwa Tekun Araba (Tekun Gishiri) kuma ya yanke gaba ɗaya. Sai mutane suka ƙetare kusa da Yeriko.
le nijihetse o rano nizotso boak’ ambone eio naho nionjoñe ho haboañe nitakatse ty atao Adame añe, i rova marine’ i Tsaretàne; le vata’e nitampake o ho nizotso mb’an-dRiak-Arabà naho mb’amy Riake Siray mb’eoo, vaho nitsake tandrife Ierikò ey ondatio.
17 Firistocin kuwa da suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji suka tsaya daram a kan busasshiyar ƙasa a tsakiyar Urdun a lokacin da Isra’ilawa suka ƙetarewa, har sai da dukan mutane suka gama ƙetarewa.
Nijohañe an-tane maik’ anteñateña’ Iardeney o mpisoroñe nitarazo i vatam-pañina’ Iehovàio, le hene nitsak’ an-tane maike t’Israele, ampara’ te tafatsàke Iardeney iaby i valobohòkey.