< Yoshuwa 24 >
1 Yoshuwa ya tattara dukan kabilan Isra’ila a Shekem. Ya aika a kira dattawa, shugabanni, alƙalai da manyan ma’aikatan Isra’ila, suka kai kansu gaban Allah.
And Josue gaderide alle the lynagis of Israel in to Sechem; and he clepide the grettere men in birthe, and the princes, and iugis, and maistris; and thei stoden in the siyt of the Lord.
2 Yoshuwa ya ce wa dukan mutanen, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Dā can, kakanninku, Tera mahaifin Ibrahim, da Nahor sun zauna a hayin Kogin Yuferites suka yi wa waɗansu alloli sujada.
And he spak thus to the puple, The Lord God of Israel seith these thingis, Youre fadris dwelliden at the bigynnyng biyende the flood Eufrates, Thare, the fadir of Abraham, and Nachor, and thei serueden alien goddis.
3 Amma na ɗauki mahaifinku Ibrahim, daga ƙasar da take can a hayin Kogin Yuferites, na kawo shi ƙasar Kan’ana, na kuma ba shi’ya’ya masu yawa. Na ba shi Ishaku,
Therfor Y took youre fadir Abraham fro the coostis of Mesopotanye, and Y brouyte hym in to the lond of Canaan; and Y multipliede `the seed of hym,
4 ga Ishaku kuwa na ba shi Yaƙub da Isuwa. Na ba Isuwa ƙasar kan tudu ta Seyir, amma Yaƙub da’ya’yansa maza suka gangara zuwa Masar.
and Y yaf Isaac to hym; and eft Y yaf to Isaac, Jacob, and Esau, of whiche Y yaf to Esau the hil of Seir, to `haue in possessioun; forsothe Jacob and hise sones yeden doun in to Egipt.
5 “‘Sai na aiki Musa da Haruna, na aukar wa Masarawa annobai, ta wurin abin da na yi ne na fitar da ku.
And Y sente Moises and Aaron, and Y smoot Egipt with many signes and wondris,
6 Lokacin da na fitar da iyayenku daga Masar, suka zo teku, sai Masarawa suka fafare su da kekunan yaƙi da dawakai har zuwa Jan Teku.
and Y ledde you and youre fadris out of Egipt. And ye camen to the see, and Egipcians pursueden youre fadris with charis, and multitude of knyytis, `til to the Reed See.
7 Amma suka yi kuka ga Ubangiji don taimako, ya kuwa sa duhu ya raba tsakaninsu da Masarawa; ya sa teku ya rufe Masarawa. Kun gani da idanunku abin da na yi wa Masarawa, sa’an nan kuka zauna a jeji na tsawon lokaci.
Forsothe the sones of Israel crieden to the Lord, and he settide derknessis bitwixe you and Egipcians; and he brouyte the see on hem, and hilide hem. Youre iyen sien alle thingis, whiche Y dide in Egipt. And ye dwelliden in wildirnesse in myche tyme.
8 “‘Na kawo ku ƙasar Amoriyawa waɗanda suke gabas da Urdun. Suka yi yaƙi da ku, amma na ba da su a hannunku, na hallaka su a gabanku, kuka kuma mallaki ƙasarsu.
And Y brouyte you in to the lond of Ammorrei, that dwellide biyende Jordan; and whanne thei fouyten ayens you, Y bitook hem in to youre hondis, and ye hadden in possessioun `the lond of hem, and ye killiden hem.
9 Lokacin da Balak ɗan Ziffor, sarkin Mowab, ya yi shiri yă yaƙi Isra’ila, ya aiki Bala’am ɗan Beyor don yă la’anta ku.
Sotheli Balach, the sone of Sephor, the king of Moab, roos, and fauyt ayens Israel; and he sente, and clepide Balaam, the sone of Beor, that he schulde curse you.
10 Amma ban saurari Bala’am ba, saboda haka sai ya ma sa muku albarka, na kuɓutar da ku daga hannunsa.
And Y nolde here hym, but ayenward bi hym Y blesside you, and delyuerede you fro hise hondis.
11 “‘Sai kuka ƙetare Urdun kuka isa Yeriko. Mutanen Yeriko suka yi faɗa da ku, kamar yadda Amoriyawa, Ferizziyawa, Kan’aniyawa, Hittiyawa, Girgashiyawa, Hiwiyawa, da Yebusiyawa suka yi, amma na ba da su a hannunku.
And ye passiden Jordan, and camen to Jerico; and men of that citee fouyten ayens you, Ammorrei, and Feresei, and Cananei, Ethei, and Gergesei, and Euei, and Jebusei; and Y bitook hem in to youre hondis.
12 Na aika rina ta kore su a idonku, haka kuma sarakunan Amoriyawan nan. Ba da takobinku ko bakanku ne kuka yi haka ba.
And Y sente flies with venemouse tongis bifor you, and Y castide hem out of her places; Y kyllide twei kyngis of Ammorreis, not in thi swerd and bowe.
13 Na ba ku ƙasar da ba ku yi wata wahala kafin ku samu ba, na ba ku kuma biranen da ba ku gina ba; kuka kuma zauna a cikinsu, kuka ci daga’ya’yan itacensu da’ya’yan zaitun da ba ku ne kuka shuka ba.’
And Y yaf to you the lond in which ye traueiliden not, and citees whiche ye bildiden not, that ye schulden dwelle in tho, and vyneris, and places of olyue trees, whiche ye plauntiden not.
14 “Yanzu, sai ku ji tsoron Ubangiji, ku bauta masa da dukan aminci. Ku zubar da allolin da kakanninku suka yi musu sujada a hayin Kogin Yuferites da kuma a Masar, ku bauta wa Ubangiji.
Now therfor drede ye the Lord, and serue ye hym with perfite herte and moost trewe; and do ye awei the goddis, to whiche youre fadris seruyden in Mesopotanye, and in Egipt; and serue ye the Lord.
15 Amma in kuka ga ba za ku iya bauta wa Ubangiji ba, sai ku zaɓa yau wanda za ku bauta masa, ko allolin da kakanninku suka bauta musu a hayin Kogin Yuferites, ko kuma allolin Amoriyawa, waɗanda kuke zama a cikin ƙasarsu. Amma da ni da gidana, Ubangiji ne za mu bauta wa.”
But if it semeth yuel to you, `that ye serue the Lord, chesyng is youun to you; chese ye to you to dai that, that plesith, whom ye owen most to serue; whether to goddis, whiche youre fadris serueden in Mesopotanye, whether to the goddis of Ammorreis, in whose lond ye dwellen; forsothe Y, and myn hows schulen serue the Lord.
16 Sai mutanen suka amsa suka ce, “Allah ya kiyashe mu da rabuwa da Ubangiji Allahnmu, har a ce mu bauta wa waɗansu alloli!
And al the puple answeride and seide, Fer be it fro vs that we forsake the Lord, and serue alien goddis.
17 Ubangiji Allahnmu ne da kansa ya fitar da iyayenmu daga Masar, daga ƙasar bauta, ya yi manyan abubuwan al’ajabi, a idanunmu. Ya kiyaye mu cikin dukan hanyar da muka bi, da cikin ƙasashen da muka ratsa;
`Oure Lord God hym silf ledde vs and oure fadris out of the lond of Egipt, fro the hows of seruage, and dide grete signes in oure siyt; and he kepte vs in al the weie, bi which we yeden, and in alle puplis, bi whiche we passiden; and he castide out alle folkis,
18 Ubangiji kuwa ya kore mana dukan Amoriyawa, waɗanda suke zaune a ƙasar. Don haka mu ma za mu bauta wa Ubangiji, gama shi ne Allahnmu.”
Ammorrei, the dwellere of the lond, in to which we entriden. Therfor we schulen serue the Lord, for he is `oure Lord God.
19 Yoshuwa ya ce wa mutanen, “Ba za ku iya bauta wa Ubangiji ba gama shi Allah mai tsarki ne; mai kishi kuma. Ba zai gafarta muku zunubin tawaye ba.
And Josue seide to the puple, Ye moun not serue the Lord; for God is hooli, and a strong feruent louyere, and he foryyueth not youre trespassis and synnes.
20 In kuka juya wa Ubangiji baya, kuka bauta wa waɗansu alloli, zai juya yă kawo muku bala’i, yă hallaka ku, yă kawo ƙarshenku.”
If ye forsaken the Lord, and seruen alien goddis, the Lord schal turne `hym silf, and schal turment you, and schal distrie, after that he hath youe goodis to you.
21 Amma mutanen suka ce wa Yoshuwa, “Mu dai! Za mu bauta wa Ubangiji.”
And the puple seide to Josue, It schal not be so, as thou spekist, but we schulen serue the Lord.
22 Yoshuwa kuwa ya ce musu, “Ku ne shaidun kanku cewa kun zaɓi ku bauta wa Ubangiji.” Suka amsa suka ce, “I, mu ne shaidun kanmu.”
And Josue seide to the puple, Ye ben witnessis, that ye han chose the Lord to you, that ye serue him. And thei answeriden, We ben witnessis.
23 Yoshuwa ya ce musu, “Yanzu sai ku zubar da allolin da suke cikinku, ku miƙa wa Ubangiji, Allah na Isra’ila zuciyarku.”
Therfor, he seide, Now do ye awei alien goddis fro the myddis of you, and bowe ye youre hertis to the Lord God of Israel.
24 Mutanen kuma suka ce, “Za mu bauta wa Ubangiji Allahnmu, mu kuma yi masa biyayya.”
And the puple seide to Josue, We schulen serue `oure Lord God, and we schulen be obedient to hise heestis.
25 A wannan rana Yoshuwa ya yi alkawari saboda mutanen, kuma a can Shekem ya tsara musu ƙa’idodi da dokoki.
Therfor Josue smoot a boond of pees in that dai, and settide forth to the puple comaundementis and domes in Sichen.
26 Yoshuwa kuwa ya rubuta abubuwan nan a cikin Littafin Dokoki na Allah. Sa’an nan ya ɗauki babban dutse ya ajiye a ƙarƙashin itacen oak kusa da tsattsarkan wuri na Ubangiji.
And he wroot alle these wordis in the book of Goddis lawe. And he took a greet stoon, and puttide it vndur an ook, that was in the seyntuarie of the Lord.
27 Ya ce wa duka mutanen, “Ku gani! Wannan dutse zai zama mana shaida, ya ji duk maganar da Ubangiji ya yi mana, zai zama muku shaida in ba ku yi wa Allahnku gaskiya ba.”
And he seide to al the puple, Lo! this stoon schal be to you in to witnessing, that ye herden alle the wordis of the Lord, whiche he spak to you, lest perauenture ye wolden denye aftirward, and lye to youre Lord God.
28 Sai Yoshuwa ya sallami mutane, kowa ya tafi ƙasar da aka ba shi gādo.
And he lefte the puple, ech man in to his possessioun.
29 Bayan waɗannan abubuwa, Yoshuwa ɗan Nun, bawan Ubangiji, ya mutu yana da shekaru ɗari da goma.
And after these thingis Josue, the sone of Nun, the `seruaunt of the Lord, diede, an hundride yeer eld and ten.
30 Suka kuma binne shi a ƙasarsa ta gādo, a Timnat Sera a ƙasar kan tudu ta Efraim, arewa da Dutsen Ga’ash.
And thei birieden hym in the costis of his possessioun, in Thannath of Sare, which is set in the hil of Effraym, fro the north part of the hil Gaas.
31 Isra’ilawa kuwa sun bauta wa Ubangiji dukan kwanakin Yoshuwa, da kuma kwanakin dattawan da ya bari, da waɗanda suka ga duk abin da Ubangiji ya yi wa Isra’ila.
And Israel seruede the Lord in alle the daies of Josue, and of the eldre men, that lyueden in long tyme aftir Josue, and whiche eldre men knewen alle the werkis of the Lord, whiche he hadde do in Israel.
32 Aka kuma binne ƙasusuwan Yusuf da aka kawo daga Masar, a Shekem a wurin da Yaƙub ya saya da azurfa ɗari daga’ya’yan Hamor, babban Shekem. Wurin ya zama gādon zuriyar Yusuf.
Also `the sones of Israel birieden the boonys of Joseph, whiche thei baren fro Egipt in Sichen, in the part of the feeld, which feeld Jacob bouyte of the sones of Emor, fadir of Sichen, for an hundrid yonge scheep; and it was in to possessioun of the sones of Joseph.
33 Eleyazar ɗan Haruna, ya mutu aka binne shi a Gibeya, wurin da aka ba ɗansa Finehas a ƙasar kan tudu ta Efraim.
Also Eliazar, sone of Aaron, preest, diede; and Fynees and hise sones biryden hym in Gabaa, which was youun to hym in the hil of Efraym.