< Yoshuwa 24 >
1 Yoshuwa ya tattara dukan kabilan Isra’ila a Shekem. Ya aika a kira dattawa, shugabanni, alƙalai da manyan ma’aikatan Isra’ila, suka kai kansu gaban Allah.
And Joshua assembled all the tribes of Israel to Shechem; and he called for the elders of Israel, and for their heads, and for their judges, and for their officers, and they presented themselves before God.
2 Yoshuwa ya ce wa dukan mutanen, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Dā can, kakanninku, Tera mahaifin Ibrahim, da Nahor sun zauna a hayin Kogin Yuferites suka yi wa waɗansu alloli sujada.
And Joshua said unto all the people, Thus hath said the Lord the God of Israel, On the other side of the river did your fathers dwell in old time, even Terach, the father of Abraham, and the father of Nachor; and they served other gods.
3 Amma na ɗauki mahaifinku Ibrahim, daga ƙasar da take can a hayin Kogin Yuferites, na kawo shi ƙasar Kan’ana, na kuma ba shi’ya’ya masu yawa. Na ba shi Ishaku,
And I took your father Abraham from the other side of the river, and I led him throughout all the land of Canaan; and I multiplied his seed, and gave him Isaac.
4 ga Ishaku kuwa na ba shi Yaƙub da Isuwa. Na ba Isuwa ƙasar kan tudu ta Seyir, amma Yaƙub da’ya’yansa maza suka gangara zuwa Masar.
And I gave unto Isaac, Jacob and Esau: and I gave unto Esau mount Seir, to possess it; but Jacob and his children went down into Egypt.
5 “‘Sai na aiki Musa da Haruna, na aukar wa Masarawa annobai, ta wurin abin da na yi ne na fitar da ku.
And I sent Moses and Aaron, and I plagued Egypt in the manner as I have done among them; and after that I brought you out.
6 Lokacin da na fitar da iyayenku daga Masar, suka zo teku, sai Masarawa suka fafare su da kekunan yaƙi da dawakai har zuwa Jan Teku.
And I brought your fathers out of Egypt; and ye came unto the sea; and the Egyptians pursued after your fathers with chariots and horsemen unto the Red Sea.
7 Amma suka yi kuka ga Ubangiji don taimako, ya kuwa sa duhu ya raba tsakaninsu da Masarawa; ya sa teku ya rufe Masarawa. Kun gani da idanunku abin da na yi wa Masarawa, sa’an nan kuka zauna a jeji na tsawon lokaci.
And they cried unto the Lord, and he put darkness between you and the Egyptians, and he brought the sea over them, and covered them; and your eyes saw what I had done on Egypt; and ye dwelt in the wilderness many days.
8 “‘Na kawo ku ƙasar Amoriyawa waɗanda suke gabas da Urdun. Suka yi yaƙi da ku, amma na ba da su a hannunku, na hallaka su a gabanku, kuka kuma mallaki ƙasarsu.
And I brought you into the land of the Emorites, that dwelt on the other side of the Jordan; and they fought with you: and I gave them into your hand, and ye took possession of their land; and I destroyed them from before you.
9 Lokacin da Balak ɗan Ziffor, sarkin Mowab, ya yi shiri yă yaƙi Isra’ila, ya aiki Bala’am ɗan Beyor don yă la’anta ku.
Then Balak the son of Zippor, the king of Moab, arose and warred against Israel; and he sent and called Bil'am the son of Beor to curse you;
10 Amma ban saurari Bala’am ba, saboda haka sai ya ma sa muku albarka, na kuɓutar da ku daga hannunsa.
And I would not hearken unto Bil'am; but he had to bless you instead: and I delivered you out of his hand.
11 “‘Sai kuka ƙetare Urdun kuka isa Yeriko. Mutanen Yeriko suka yi faɗa da ku, kamar yadda Amoriyawa, Ferizziyawa, Kan’aniyawa, Hittiyawa, Girgashiyawa, Hiwiyawa, da Yebusiyawa suka yi, amma na ba da su a hannunku.
And ye passed over the Jordan, and came unto Jericho; and then fought the men of Jericho against you, the Emorites, and the Perizzites, and the Canaanites, and the Hittites, and the Girgashites, the Hivites, and the Jebusites: and I gave them up into your hand.
12 Na aika rina ta kore su a idonku, haka kuma sarakunan Amoriyawan nan. Ba da takobinku ko bakanku ne kuka yi haka ba.
And I sent before you the hornet which drove them out from before you, even the two kings of the Emorites: not with thy sword, and not with thy bow.
13 Na ba ku ƙasar da ba ku yi wata wahala kafin ku samu ba, na ba ku kuma biranen da ba ku gina ba; kuka kuma zauna a cikinsu, kuka ci daga’ya’yan itacensu da’ya’yan zaitun da ba ku ne kuka shuka ba.’
And I gave you a land for which ye had not toiled, and cities which ye had not built, and ye dwell in them; of vineyards and oliveyards which ye planted not do ye eat.
14 “Yanzu, sai ku ji tsoron Ubangiji, ku bauta masa da dukan aminci. Ku zubar da allolin da kakanninku suka yi musu sujada a hayin Kogin Yuferites da kuma a Masar, ku bauta wa Ubangiji.
Now therefore fear the Lord, and serve him in sincerity and truth; and put away the gods which your fathers served on the other side of the river and in Egypt, and serve the Lord.
15 Amma in kuka ga ba za ku iya bauta wa Ubangiji ba, sai ku zaɓa yau wanda za ku bauta masa, ko allolin da kakanninku suka bauta musu a hayin Kogin Yuferites, ko kuma allolin Amoriyawa, waɗanda kuke zama a cikin ƙasarsu. Amma da ni da gidana, Ubangiji ne za mu bauta wa.”
And if it be displeasing in your eyes to serve the Lord, choose for yourselves this day whom ye will serve: whether the gods which your fathers that were on the other side of the river served, or the gods of the Emorites, in whose land ye dwell; but as for me and my house, we will serve the Lord.
16 Sai mutanen suka amsa suka ce, “Allah ya kiyashe mu da rabuwa da Ubangiji Allahnmu, har a ce mu bauta wa waɗansu alloli!
And the people answered and said, Far be it from us to forsake the Lord, to serve other gods;
17 Ubangiji Allahnmu ne da kansa ya fitar da iyayenmu daga Masar, daga ƙasar bauta, ya yi manyan abubuwan al’ajabi, a idanunmu. Ya kiyaye mu cikin dukan hanyar da muka bi, da cikin ƙasashen da muka ratsa;
For the Lord our God it is that hath brought us and our fathers up out of the land of Egypt, from the house of slavery, and who hath done those great signs before our eyes, and preserved us upon all the way whereon we have gone, and among all the people through the midst of whom we have passed:
18 Ubangiji kuwa ya kore mana dukan Amoriyawa, waɗanda suke zaune a ƙasar. Don haka mu ma za mu bauta wa Ubangiji, gama shi ne Allahnmu.”
And the Lord hath driven out all the nations, and the Emorites who dwelt in the land, from before us; therefore also will we serve the Lord; for he is our God.
19 Yoshuwa ya ce wa mutanen, “Ba za ku iya bauta wa Ubangiji ba gama shi Allah mai tsarki ne; mai kishi kuma. Ba zai gafarta muku zunubin tawaye ba.
And Joshua said unto the people, Ye will not be able to serve the Lord; for he is a holy God; he is a watchful God; he will not have any indulgence for your transgressions and for your sins;
20 In kuka juya wa Ubangiji baya, kuka bauta wa waɗansu alloli, zai juya yă kawo muku bala’i, yă hallaka ku, yă kawo ƙarshenku.”
If ye forsake the Lord, and serve strange gods, then will he again do ye evil, and consume ye, after that he hath done you good.
21 Amma mutanen suka ce wa Yoshuwa, “Mu dai! Za mu bauta wa Ubangiji.”
And the people said unto Joshua, No; nevertheless the Lord will we serve.
22 Yoshuwa kuwa ya ce musu, “Ku ne shaidun kanku cewa kun zaɓi ku bauta wa Ubangiji.” Suka amsa suka ce, “I, mu ne shaidun kanmu.”
And Joshua said unto the people, Ye are witnesses against yourselves that ye yourselves have chosen for you the Lord, to serve him. And they said, We are witnesses.
23 Yoshuwa ya ce musu, “Yanzu sai ku zubar da allolin da suke cikinku, ku miƙa wa Ubangiji, Allah na Isra’ila zuciyarku.”
And now put away the strange gods which are in the midst of you, and incline your heart unto the Lord the God of Israel.
24 Mutanen kuma suka ce, “Za mu bauta wa Ubangiji Allahnmu, mu kuma yi masa biyayya.”
And the people said unto Joshua, The Lord our God will we serve, and his voice will we obey.
25 A wannan rana Yoshuwa ya yi alkawari saboda mutanen, kuma a can Shekem ya tsara musu ƙa’idodi da dokoki.
And Joshua made a covenant with the people on that day, and set them a statute and an ordinance in Shechem.
26 Yoshuwa kuwa ya rubuta abubuwan nan a cikin Littafin Dokoki na Allah. Sa’an nan ya ɗauki babban dutse ya ajiye a ƙarƙashin itacen oak kusa da tsattsarkan wuri na Ubangiji.
And Joshua wrote these words in the book of the law of God; and he took a great stone, and set it up there under the oak, that was by the sanctuary of the Lord.
27 Ya ce wa duka mutanen, “Ku gani! Wannan dutse zai zama mana shaida, ya ji duk maganar da Ubangiji ya yi mana, zai zama muku shaida in ba ku yi wa Allahnku gaskiya ba.”
And Joshua said unto all the people, Behold, this stone shall be among us as a witness; for it hath heard all the words of the Lord which he spoke unto us: it shall be therefore as a witness against you, that ye may not deny your God.
28 Sai Yoshuwa ya sallami mutane, kowa ya tafi ƙasar da aka ba shi gādo.
And Joshua let the people depart, every man unto his inheritance.
29 Bayan waɗannan abubuwa, Yoshuwa ɗan Nun, bawan Ubangiji, ya mutu yana da shekaru ɗari da goma.
And it came to pass after these things, that Joshua the son of Nun, the servant of the Lord, died, one hundred and ten years old.
30 Suka kuma binne shi a ƙasarsa ta gādo, a Timnat Sera a ƙasar kan tudu ta Efraim, arewa da Dutsen Ga’ash.
And they buried him on the border of his inheritance at Timnath-serach, which is on the mountain of Ephraim, on the north side of mount Ga'ash.
31 Isra’ilawa kuwa sun bauta wa Ubangiji dukan kwanakin Yoshuwa, da kuma kwanakin dattawan da ya bari, da waɗanda suka ga duk abin da Ubangiji ya yi wa Isra’ila.
And Israel served the Lord all the days of Joshua, and all the days of the elders who lived many days after Joshua, and who had known all the deeds of the Lord, that he had done for Israel.
32 Aka kuma binne ƙasusuwan Yusuf da aka kawo daga Masar, a Shekem a wurin da Yaƙub ya saya da azurfa ɗari daga’ya’yan Hamor, babban Shekem. Wurin ya zama gādon zuriyar Yusuf.
And the bones of Joseph, which the children of Israel had brought up out of Egypt, they buried in Shechem, in a parcel of the field which Jacob had bought of the sons of Chamor the father of Shechem for one hundred kessitah: and it remained the inheritance of the children of Joseph.
33 Eleyazar ɗan Haruna, ya mutu aka binne shi a Gibeya, wurin da aka ba ɗansa Finehas a ƙasar kan tudu ta Efraim.
And Elazar the son of Aaron died; and they buried him on the hill of Phinehas his son, which was given him in the mountain of Ephraim.