< Yoshuwa 24 >

1 Yoshuwa ya tattara dukan kabilan Isra’ila a Shekem. Ya aika a kira dattawa, shugabanni, alƙalai da manyan ma’aikatan Isra’ila, suka kai kansu gaban Allah.
Bangʼe Joshua nochoko dhout Israel duto kama iluongo ni Shekem. Noluongo jodongo, jotelo, jongʼad bura kod jotelo mamoko mag Israel mi gidhi e nyim Nyasaye.
2 Yoshuwa ya ce wa dukan mutanen, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Dā can, kakanninku, Tera mahaifin Ibrahim, da Nahor sun zauna a hayin Kogin Yuferites suka yi wa waɗansu alloli sujada.
Joshua nowachone ji duto niya, “Ma e gima Jehova Nyasaye, ma Nyasach Israel wacho, Chon gi lala kwereu, motingʼo nyaka Tera ma wuon Ibrahim kod Nahor, nodak but Aora Yufrate kendo negilamo nyiseche manono.
3 Amma na ɗauki mahaifinku Ibrahim, daga ƙasar da take can a hayin Kogin Yuferites, na kawo shi ƙasar Kan’ana, na kuma ba shi’ya’ya masu yawa. Na ba shi Ishaku,
Makmana nagolo wuonu Ibrahim oa e pinyno machiegni gi Aora Yufrate mi atelone e piny Kanaan duto kendo amiye nyikwayo mathoth. Ne amiye Isaka,
4 ga Ishaku kuwa na ba shi Yaƙub da Isuwa. Na ba Isuwa ƙasar kan tudu ta Seyir, amma Yaƙub da’ya’yansa maza suka gangara zuwa Masar.
to Isaka namiyo Jakobo kod Esau. Ne awalo piny Seir manie got ne Esau, to Jakobo gi nyithinde nodhi Misri.
5 “‘Sai na aiki Musa da Haruna, na aukar wa Masarawa annobai, ta wurin abin da na yi ne na fitar da ku.
“‘Bangʼe ne aoro Musa gi Harun, kendo ne agoyo jo-Misri gi tuoche kanyo, bangʼe agolou oko.
6 Lokacin da na fitar da iyayenku daga Masar, suka zo teku, sai Masarawa suka fafare su da kekunan yaƙi da dawakai har zuwa Jan Teku.
Kane agolo wuoneu Misri, ne uchopo e nam, kendo jo-Misri nolawou gi geche kod jogo mariambo farese nyaka e Nam Makwar.
7 Amma suka yi kuka ga Ubangiji don taimako, ya kuwa sa duhu ya raba tsakaninsu da Masarawa; ya sa teku ya rufe Masarawa. Kun gani da idanunku abin da na yi wa Masarawa, sa’an nan kuka zauna a jeji na tsawon lokaci.
To ne giywakne Jehova Nyasaye mondo okonygi, omiyo ne oketo mudho e kindu gi jo-Misri; mi nam oimogi. Ne uneno gima ne atimone jo-Misri. Bangʼ mano nudak e thim kuom ndalo marabora.
8 “‘Na kawo ku ƙasar Amoriyawa waɗanda suke gabas da Urdun. Suka yi yaƙi da ku, amma na ba da su a hannunku, na hallaka su a gabanku, kuka kuma mallaki ƙasarsu.
“‘Ne akelou nyaka e piny jo-Amor manodak yo wuok chiengʼ mar aora Jordan. Negikedo kodu, to naketogi e lwetu. Ne atiekogi chuth e nyimu, mi ukawo pinygi.
9 Lokacin da Balak ɗan Ziffor, sarkin Mowab, ya yi shiri yă yaƙi Isra’ila, ya aiki Bala’am ɗan Beyor don yă la’anta ku.
Kane Balak wuod Zipor, ma ruodh Moab, ne ikore mondo oked gi Israel, nooro Balaam wuod Beor mondo okwongʼu.
10 Amma ban saurari Bala’am ba, saboda haka sai ya ma sa muku albarka, na kuɓutar da ku daga hannunsa.
To ne ok anyal chiko ita ne Balaam, omiyo nogwedhou mogundho, mi nagolou oko e lwete.
11 “‘Sai kuka ƙetare Urdun kuka isa Yeriko. Mutanen Yeriko suka yi faɗa da ku, kamar yadda Amoriyawa, Ferizziyawa, Kan’aniyawa, Hittiyawa, Girgashiyawa, Hiwiyawa, da Yebusiyawa suka yi, amma na ba da su a hannunku.
“‘Bangʼe ne ungʼado aora Jordan mi ubiro Jeriko. Joma odak Jeriko, kaka jo-Amor, jo-Perizi, jo-Kanaan, jo-Hiti, jo-Girgash, jo-Hivi, gi jo-Jebus nokedo kodu, to ne achiwogi duto e lwetu.
12 Na aika rina ta kore su a idonku, haka kuma sarakunan Amoriyawan nan. Ba da takobinku ko bakanku ne kuka yi haka ba.
Ne amiyo kibaji omakogi ma giringo e nyimu, kaachiel gi ruodhi jo-Amor ariyo. Ne ok utimo ma gi liganglau uwegi kod atungʼ.
13 Na ba ku ƙasar da ba ku yi wata wahala kafin ku samu ba, na ba ku kuma biranen da ba ku gina ba; kuka kuma zauna a cikinsu, kuka ci daga’ya’yan itacensu da’ya’yan zaitun da ba ku ne kuka shuka ba.’
Omiyo ne amiyou piny mane ok utiyone kod mier madongo mane ok ugero; mi udak kanyo kendo uchamo olemb mzabibu kod zeituni ma bende ne ok upidho.’
14 “Yanzu, sai ku ji tsoron Ubangiji, ku bauta masa da dukan aminci. Ku zubar da allolin da kakanninku suka yi musu sujada a hayin Kogin Yuferites da kuma a Masar, ku bauta wa Ubangiji.
“Omiyo koro luoruru Jehova Nyasaye kendo beduru joratiro kinde duto kutiyone. Wituru oko nyiseche manono mag kwereu mane gilamo yo Aora Yufrate kod e piny Misri, mondo uti ne Jehova Nyasaye.
15 Amma in kuka ga ba za ku iya bauta wa Ubangiji ba, sai ku zaɓa yau wanda za ku bauta masa, ko allolin da kakanninku suka bauta musu a hayin Kogin Yuferites, ko kuma allolin Amoriyawa, waɗanda kuke zama a cikin ƙasarsu. Amma da ni da gidana, Ubangiji ne za mu bauta wa.”
To ka dipo ni tiyone Jehova Nyasaye ok miu mor, to kawuononi yier aneuru ngʼama ubiro tiyone, kata ka en nyiseche manono mane kwereu tiyone e Aora Yufrate, kata en nyiseche manono mag jo-Amor, modak e pinygi. Makmana an gi jooda duto, wabiro tiyone Jehova Nyasaye.”
16 Sai mutanen suka amsa suka ce, “Allah ya kiyashe mu da rabuwa da Ubangiji Allahnmu, har a ce mu bauta wa waɗansu alloli!
Eka ji nodwoko niya, “Mad gima chal kamano kik timrenwa ka wajwangʼo Jehova Nyasaye, mondo watine nyiseche manono!
17 Ubangiji Allahnmu ne da kansa ya fitar da iyayenmu daga Masar, daga ƙasar bauta, ya yi manyan abubuwan al’ajabi, a idanunmu. Ya kiyaye mu cikin dukan hanyar da muka bi, da cikin ƙasashen da muka ratsa;
En Jehova Nyasaye ma Nyasachwa owuon mane ogolowa gi kwerewa e piny Misri, e piny mane wan wasumbini, kendo motimo ranyisi madongo-go ka waneno. Ne oritowa e wuodhwa duto kendo e kind ogendini duto mane wakalo eigi.
18 Ubangiji kuwa ya kore mana dukan Amoriyawa, waɗanda suke zaune a ƙasar. Don haka mu ma za mu bauta wa Ubangiji, gama shi ne Allahnmu.”
Kendo Jehova Nyasaye ne oriembo ogendini duto e nyimwa, kaachiel gi jo-Amor, mane odak e pinyno. Wan bende wabiro tiyone Jehova Nyasaye, nikech en e Nyasachwa.”
19 Yoshuwa ya ce wa mutanen, “Ba za ku iya bauta wa Ubangiji ba gama shi Allah mai tsarki ne; mai kishi kuma. Ba zai gafarta muku zunubin tawaye ba.
Joshua nowachone ji niya, “Ok unyal tiyone Jehova Nyasaye. En Nyasaye maler, en Nyasaye ma janyiego. Ok obi wenu kuom wich teko maru kod richo mutimo.
20 In kuka juya wa Ubangiji baya, kuka bauta wa waɗansu alloli, zai juya yă kawo muku bala’i, yă hallaka ku, yă kawo ƙarshenku.”
Ka ungʼanyo uweyo Jehova Nyasaye mi utiyo ne nyiseche manono, to obiro lokore mi okelnu thagruok kendo enotieku duto, kata obedo ni ne osedoko jakoru kamano.”
21 Amma mutanen suka ce wa Yoshuwa, “Mu dai! Za mu bauta wa Ubangiji.”
To jo-Israel nodwoko Joshua niya, “Ooyo! Wabiro tiyone Jehova Nyasaye.”
22 Yoshuwa kuwa ya ce musu, “Ku ne shaidun kanku cewa kun zaɓi ku bauta wa Ubangiji.” Suka amsa suka ce, “I, mu ne shaidun kanmu.”
Bangʼe Joshua nowacho niya, “Un uwegi usebedo joneno magu kuom yiero mondo uti ne Jehova Nyasaye.” Negidwoko niya, “Ee, wan joneno.”
23 Yoshuwa ya ce musu, “Yanzu sai ku zubar da allolin da suke cikinku, ku miƙa wa Ubangiji, Allah na Isra’ila zuciyarku.”
Joshua nowacho niya, “Koro wituru nyiseche manono manie dieru mondo uchiw chunyu ni tiyo ne Jehova Nyasaye, ma Nyasach Israel.”
24 Mutanen kuma suka ce, “Za mu bauta wa Ubangiji Allahnmu, mu kuma yi masa biyayya.”
To jogo nowachone Joshua niya, “Wabiro tiyone Jehova Nyasaye ma Nyasachwa kendo wanamiye luor.”
25 A wannan rana Yoshuwa ya yi alkawari saboda mutanen, kuma a can Shekem ya tsara musu ƙa’idodi da dokoki.
E odiechiengno Joshua noketo singruok ne jogo, kendo kane gin Shekem nomiyogi chike monego gilu.
26 Yoshuwa kuwa ya rubuta abubuwan nan a cikin Littafin Dokoki na Allah. Sa’an nan ya ɗauki babban dutse ya ajiye a ƙarƙashin itacen oak kusa da tsattsarkan wuri na Ubangiji.
Joshua nondiko gigo duto piny e Kitabu mar Chik mar Nyasaye. Bangʼe nokawo kidi maduongʼ mi okete maber e tiend yiend ober but kama ler mar Jehova Nyasaye.
27 Ya ce wa duka mutanen, “Ku gani! Wannan dutse zai zama mana shaida, ya ji duk maganar da Ubangiji ya yi mana, zai zama muku shaida in ba ku yi wa Allahnku gaskiya ba.”
Nowachone jogo niya, “Neuru! Kidini biro bedo janeno kuomu. Osewinjo weche duto ma Jehova Nyasaye osewachonwa. Obiro bedo janeno kuomu ka ubedo jo-miriambo ne Nyasachu.”
28 Sai Yoshuwa ya sallami mutane, kowa ya tafi ƙasar da aka ba shi gādo.
Bangʼe Joshua nogolo ji duto mondo odhi kuondegi mane opognigi.
29 Bayan waɗannan abubuwa, Yoshuwa ɗan Nun, bawan Ubangiji, ya mutu yana da shekaru ɗari da goma.
Bangʼ mago duto, Joshua wuod Nun, jatich Jehova Nyasaye, notho ka en gi higni mia achiel gapar.
30 Suka kuma binne shi a ƙasarsa ta gādo, a Timnat Sera a ƙasar kan tudu ta Efraim, arewa da Dutsen Ga’ash.
Kendo ne giike e lope mane opogne, mantiere Timnath Sera e piny gode mag Efraim, mantiere yo nyandwat mar Gash.
31 Isra’ilawa kuwa sun bauta wa Ubangiji dukan kwanakin Yoshuwa, da kuma kwanakin dattawan da ya bari, da waɗanda suka ga duk abin da Ubangiji ya yi wa Isra’ila.
Jo-Israel notiyone Jehova Nyasaye e ndalo duto mag ngima Joshua kod jodongo mane osedak higni moloye, kendo mane nigi lony kuom gik moko duto mane Jehova Nyasaye osetimo ni jo-Israel.
32 Aka kuma binne ƙasusuwan Yusuf da aka kawo daga Masar, a Shekem a wurin da Yaƙub ya saya da azurfa ɗari daga’ya’yan Hamor, babban Shekem. Wurin ya zama gādon zuriyar Yusuf.
To choke Josef, mane jo-Israel nobiro godo koa Misri, noiki Shekem e pinyno mane Jakobo ongʼiewo fedha mia achiel koa kuom yawuot Hamor, ma wuon Shekem. Ma nobedo kaka pok mar nyikwa Josef.
33 Eleyazar ɗan Haruna, ya mutu aka binne shi a Gibeya, wurin da aka ba ɗansa Finehas a ƙasar kan tudu ta Efraim.
Eliazar wuod Harun bende notho kendo noyike Gibea, kama nopogne wuode Finehas e piny gode mag Efraim.

< Yoshuwa 24 >