< Yoshuwa 23 >
1 An daɗe bayan da Ubangiji ya ba Isra’ilawa hutu daga dukan abokan gāban da suke kewaye da su. Yoshuwa kuwa ya tsufa, shekarunsa sun yi yawa,
Pripetilo se je, dolgo časa po tem, ko je Gospod dal počitek Izraelu pred vsemi njegovimi sovražniki naokoli, da je Józue postal star in zvrhan v starosti.
2 sai ya aika a kira Isra’ilawa duka, dattawansu, shugabanninsu, alƙalansu, da manyan ma’aikatansu, ya ce musu, “Na tsufa, shekaruna kuwa sun yi yawa,
Józue je dal poklicati ves Izrael in po njihove starešine, po njihove poglavarje, po njihove sodnike, po njihove častnike ter jim rekel: »Star sem in zvrhan v starosti.
3 ku kanku kun ga dukan abubuwan da Ubangiji Allahnku ya yi da idanunku wa dukan ƙasashen nan, Ubangiji Allahnku shi ne wanda ya yi yaƙi dominku.
Videli ste vse, kar je Gospod, vaš Bog, zaradi vas storil vsem tem narodom, kajti Gospod, vaš Bog, je ta, ki se je boril za vas.
4 Ku tuna yadda na rarraba wa kabilanku ƙasashen nan su zama naku na gādo, dukan ƙasashen da suka rage, ƙasashen da na ci da yaƙi, tsakanin Urdun da Bahar Rum a yamma.
Glejte, z žrebom sem vam razdelil vse te narode, ki preostajajo, da bodo dediščina za vaše rodove, od Jordana, z vsemi narodi, ki sem jih iztrebil, celo do vélikega morja proti zahodu.
5 Ubangiji Allahnku kansa zai kore su a madadinku. Zai fafare su a gabanku, za ku kuwa mallaki ƙasarsu, yadda Ubangiji Allah ya yi muku alkawari.
Gospod, vaš Bog, jih bo pregnal izpred vas in jih pognal iz vašega pogleda in vi boste vzeli v last njihovo deželo, kakor vam je Gospod, vaš Bog, obljubil.
6 “Ku yi ƙarfin hali, ku yi hankali, ku yi biyayya da dukan abin da aka rubuta a cikin Littafin Dokoki na Musa, ba tare da kun juya hagu ko dama ba.
Bodite torej zelo pogumni, da se držite in da storite vse, kar je zapisano v knjigi Mojzesove postave, da se ne obrnete vstran od tam ne k desni roki ne k levi,
7 Kada ku haɗa kai da mutanen nan da suke zama cikinku; ba ruwanku da sunayen allolinsu, kada ku rantse da su. Kada kuwa ku bauta musu ko kuwa ku rusuna musu.
da ne pridete med te narode, te, ki preostajajo med vami, niti ne omenjajte imena njihovih bogov, niti ne povzročajte, da prisegate pri njih, niti jim ne služite, niti se jim ne priklanjajte,
8 Sai dai ku riƙe Ubangiji Allahnku da kyau, yadda kuka yi har zuwa yanzu.
temveč se trdno pridružite Gospodu, svojemu Bogu, kakor ste storili ta dan.
9 “Ubangiji ya kori manyan ƙasashe masu ƙarfi; har wa yau ba wanda ya iya cin ku da yaƙi.
Kajti Gospod je izpred vas pregnal velike in močne narode, toda glede vas, noben človek ni mogel obstati pred vami do tega dne.
10 Mutum ɗaya a cikinku ya isa yă sa mutane dubu nasu su gudu, domin Ubangiji Allahnku yana yaƙi dominku, kamar yadda ya yi alkawari.
En mož med vami jih bo pregnal tisoč, kajti Gospod, vaš Bog, on je ta, ki se bori za vas, kakor vam je obljubil.
11 Saboda haka sai ku kula da kanku sosai, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku.
Pazite torej nase, da ljubite Gospoda, svojega Boga.
12 “Amma in kuka juya baya kuka zama abokai ga waɗanda suka ragu suke zama a cikinku a ƙasashen nan, har kuka yi auratayya da su, kuka haɗa kai da su,
Sicer če boste na kakršenkoli način šli nazaj in se trdno pridružili preostanku teh narodov, torej tem, ki preostajajo med vami in boste z njimi sklepali poroke in šli noter k njim in oni k vam,
13 ku tabbata cewa Ubangiji Allahnku ba zai kore muku mutanen ƙasashen nan ba, sai ma su zama muku dutsen tuntuɓe da tarko, za su zama bulala a bayanku, ƙayayyuwa a idanunku, har sai kun hallaka daga wannan ƙasa mai kyau wadda Ubangiji Allahnku ya ba ku.
zagotovo vedite, da Gospod, vaš Bog, izpred vas ne bo več pregnal nobenega izmed teh narodov, temveč vam bodo zanke, pasti in nadloge na vaših straneh in trni v vaših očeh, dokler ne izginete iz te dobre dežele, ki vam jo je dal Gospod, vaš Bog.
14 “Yanzu na kusa barin fuskar duniyan nan. Kun sani da dukan zuciyarku, da dukan ranku cewa, Ba ko ɗaya daga cikin alkawuran da Ubangiji Allahnku ya yi, da bai cika ba. Kowane alkawari ya cika; ba ko ɗaya da bai cika ba.
Glejte, ta dan grem pot vse zemlje in vi veste v vseh svojih srcih in v vseh svojih dušah, da se ni izjalovila niti ena od vseh dobrih stvari, ki jih je Gospod, vaš Bog, govoril glede vas. Vse so se vam zgodile in niti ena stvar od tega se ni izjalovila.
15 Kamar yadda Ubangiji Allahnku kuwa ya cika kowane alkawari mai kyau, haka ma ba zai fasa kawo muku bala’in da ya faɗi ba, sai ya hallaka ku daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba ku.
Zato se bo zgodilo, da kakor vse dobre stvari, ki so prišle nad vas, ki vam jih je Gospod, vaš Bog, obljubil, tako bo Gospod nad vas privedel vse zle stvari, dokler vas ne uniči iz te dobre dežele, ki vam jo je dal Gospod, vaš Bog.
16 In kuka karya alkawarin Ubangiji Allahnku wanda ya umarce ku, in kuka je kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka rusuna musu, fushin Ubangiji zai sauko a kanku, za ku kuwa hallaka da sauri daga ƙasan nan mai kyau da ya ba ku.”
Ko ste prekršili zavezo Gospoda, svojega Boga, ki vam jo je zapovedal in šli ter služili drugim bogovom in se jim priklanjali, potem bo zoper vas vžgana Gospodova jeza in hitro boste izginili iz dobre dežele, ki vam jo je dal.«