< Yoshuwa 23 >

1 An daɗe bayan da Ubangiji ya ba Isra’ilawa hutu daga dukan abokan gāban da suke kewaye da su. Yoshuwa kuwa ya tsufa, shekarunsa sun yi yawa,
Bertahun-tahun telah berlalu, dan TUHAN sudah membuat bangsa Israel aman dari semua musuh mereka. Ketika Yosua sudah sangat tua,
2 sai ya aika a kira Isra’ilawa duka, dattawansu, shugabanninsu, alƙalansu, da manyan ma’aikatansu, ya ce musu, “Na tsufa, shekaruna kuwa sun yi yawa,
dia mengumpulkan para tua-tua, kepala suku, hakim, dan pengatur pasukan seluruh bangsa Israel, lalu berkata kepada mereka, “Saya sudah sangat tua.
3 ku kanku kun ga dukan abubuwan da Ubangiji Allahnku ya yi da idanunku wa dukan ƙasashen nan, Ubangiji Allahnku shi ne wanda ya yi yaƙi dominku.
Selama ini kalian sudah melihat segala yang TUHAN lakukan bagi kita. TUHAN Allah kita, Dialah yang berperang melawan semua bangsa di sini demi kita.
4 Ku tuna yadda na rarraba wa kabilanku ƙasashen nan su zama naku na gādo, dukan ƙasashen da suka rage, ƙasashen da na ci da yaƙi, tsakanin Urdun da Bahar Rum a yamma.
Ingatlah, saya sudah membagi dengan undian seluruh daerah di sebelah barat sungai Yordan sampai ke Laut Tengah sebagai tanah warisan suku-suku kalian, baik daerah yang masih ditinggali bangsa-bangsa setempat, maupun daerah yang bangsa-bangsanya sudah kita kalahkan.
5 Ubangiji Allahnku kansa zai kore su a madadinku. Zai fafare su a gabanku, za ku kuwa mallaki ƙasarsu, yadda Ubangiji Allah ya yi muku alkawari.
TUHANlah yang akan mengusir mereka dari hadapan kalian, sehingga kalian dapat menguasai tanah mereka seperti yang TUHAN janjikan kepadamu.
6 “Ku yi ƙarfin hali, ku yi hankali, ku yi biyayya da dukan abin da aka rubuta a cikin Littafin Dokoki na Musa, ba tare da kun juya hagu ko dama ba.
“Karena itu, kalian harus benar-benar kuat dan taat dalam melakukan semua yang ditulis dalam kitab Taurat. Janganlah menyimpang dari semuanya itu.
7 Kada ku haɗa kai da mutanen nan da suke zama cikinku; ba ruwanku da sunayen allolinsu, kada ku rantse da su. Kada kuwa ku bauta musu ko kuwa ku rusuna musu.
Jangan bercampur dengan bangsa-bangsa yang masih tinggal di antaramu. Kalian tidak boleh bersumpah memakai nama dewa mereka, bahkan jangan menyebut nama dewa mereka sama sekali! Kalian tidak boleh mengabdi ataupun bersujud menyembah dewa mereka!
8 Sai dai ku riƙe Ubangiji Allahnku da kyau, yadda kuka yi har zuwa yanzu.
Kalian harus setia kepada TUHAN Allahmu, seperti yang selama ini kalian lakukan sampai sekarang.
9 “Ubangiji ya kori manyan ƙasashe masu ƙarfi; har wa yau ba wanda ya iya cin ku da yaƙi.
“TUHAN sudah mengusir dari hadapan kalian bangsa-bangsa yang besar dan kuat. Sampai hari ini, tidak ada satu pun bangsa yang dapat bertahan melawan kalian.
10 Mutum ɗaya a cikinku ya isa yă sa mutane dubu nasu su gudu, domin Ubangiji Allahnku yana yaƙi dominku, kamar yadda ya yi alkawari.
Satu orang dari kalian dapat mengalahkan seribu orang, karena TUHAN Allahmu berperang bagi kalian, seperti yang Dia janjikan kepadamu.
11 Saboda haka sai ku kula da kanku sosai, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku.
Karena itu, pastikanlah baik-baik untuk mengasihi TUHAN Allahmu!
12 “Amma in kuka juya baya kuka zama abokai ga waɗanda suka ragu suke zama a cikinku a ƙasashen nan, har kuka yi auratayya da su, kuka haɗa kai da su,
“Kalau kalian tidak setia kepada-Nya dan berbaur dengan bangsa-bangsa lain yang tersisa di antara kalian, menikah dengan mereka, dan bergaul dengan mereka,
13 ku tabbata cewa Ubangiji Allahnku ba zai kore muku mutanen ƙasashen nan ba, sai ma su zama muku dutsen tuntuɓe da tarko, za su zama bulala a bayanku, ƙayayyuwa a idanunku, har sai kun hallaka daga wannan ƙasa mai kyau wadda Ubangiji Allahnku ya ba ku.
ketahuilah, TUHAN Allahmu pasti tidak akan mengusir bangsa-bangsa ini dari hadapan kalian lagi. Mereka akan menjadi jerat atau perangkap bagi kalian. Mereka akan membuat kalian menderita, seperti cambuk pada punggung dan duri pada mata, hingga kalian binasa dari tanah yang baik ini, yang diberikan TUHAN kepada kalian.
14 “Yanzu na kusa barin fuskar duniyan nan. Kun sani da dukan zuciyarku, da dukan ranku cewa, Ba ko ɗaya daga cikin alkawuran da Ubangiji Allahnku ya yi, da bai cika ba. Kowane alkawari ya cika; ba ko ɗaya da bai cika ba.
“Sebentar lagi saya akan mati. Kalian semua tahu benar bahwa TUHAN Allahmu sudah memenuhi semua hal baik yang Dia janjikan kepadamu. Tidak ada satu pun yang tidak dipenuhi.
15 Kamar yadda Ubangiji Allahnku kuwa ya cika kowane alkawari mai kyau, haka ma ba zai fasa kawo muku bala’in da ya faɗi ba, sai ya hallaka ku daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba ku.
Tetapi sebagaimana TUHAN Allahmu sudah memberikan segala yang baik kepada kalian, Dia pasti juga akan menggenapi kutukan-Nya bila kalian melanggar perjanjian-Nya dengan menyembah dewa-dewa. Dia akan sangat marah dan segera membinasakan kalian dari negeri yang baik ini, yang sudah Dia berikan kepadamu.”
16 In kuka karya alkawarin Ubangiji Allahnku wanda ya umarce ku, in kuka je kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka rusuna musu, fushin Ubangiji zai sauko a kanku, za ku kuwa hallaka da sauri daga ƙasan nan mai kyau da ya ba ku.”

< Yoshuwa 23 >