< Yoshuwa 23 >

1 An daɗe bayan da Ubangiji ya ba Isra’ilawa hutu daga dukan abokan gāban da suke kewaye da su. Yoshuwa kuwa ya tsufa, shekarunsa sun yi yawa,
Or il arriva plusieurs jours après, que l'Eternel ayant donné du repos à Israël de tous leurs ennemis à l'environ, Josué était vieux, fort avancé en âge.
2 sai ya aika a kira Isra’ilawa duka, dattawansu, shugabanninsu, alƙalansu, da manyan ma’aikatansu, ya ce musu, “Na tsufa, shekaruna kuwa sun yi yawa,
Et Josué appela tout Israël, ses Anciens, et ses chefs, et ses juges, et ses officiers, et leur dit: Je suis devenu vieux, fort avancé en âge.
3 ku kanku kun ga dukan abubuwan da Ubangiji Allahnku ya yi da idanunku wa dukan ƙasashen nan, Ubangiji Allahnku shi ne wanda ya yi yaƙi dominku.
Vous avez vu aussi tout ce que l'Eternel votre Dieu a fait à toutes ces nations, à cause de vous; car l'Eternel votre Dieu est celui qui combat pour vous.
4 Ku tuna yadda na rarraba wa kabilanku ƙasashen nan su zama naku na gādo, dukan ƙasashen da suka rage, ƙasashen da na ci da yaƙi, tsakanin Urdun da Bahar Rum a yamma.
Voyez, je vous ai partagé par sort en héritage selon vos Tribus, [le pays de] ces nations qui sont restées, depuis le Jourdain, et [le pays de] toutes les nations que j'ai exterminées, jusqu'à la grande mer, vers le soleil couchant.
5 Ubangiji Allahnku kansa zai kore su a madadinku. Zai fafare su a gabanku, za ku kuwa mallaki ƙasarsu, yadda Ubangiji Allah ya yi muku alkawari.
Et l'Eternel votre Dieu les chassera de devant vous, et les dépossédera; et vous posséderez leur pays en héritage, comme l'Eternel votre Dieu vous [en] a parlé.
6 “Ku yi ƙarfin hali, ku yi hankali, ku yi biyayya da dukan abin da aka rubuta a cikin Littafin Dokoki na Musa, ba tare da kun juya hagu ko dama ba.
Fortifiez-vous donc de plus en plus, pour garder et faire tout ce qui est écrit au livre de la Loi de Moïse; afin que vous ne vous en détourniez ni à droite ni à gauche;
7 Kada ku haɗa kai da mutanen nan da suke zama cikinku; ba ruwanku da sunayen allolinsu, kada ku rantse da su. Kada kuwa ku bauta musu ko kuwa ku rusuna musu.
Et que vous ne vous mêliez point avec ces nations qui sont restées parmi vous; que vous ne fassiez point mention du nom de leurs dieux; et que vous ne fassiez jurer personne [par eux], et que vous ne les serviez point, et ne vous prosterniez point devant eux.
8 Sai dai ku riƙe Ubangiji Allahnku da kyau, yadda kuka yi har zuwa yanzu.
Mais attachez-vous à l'Eternel votre Dieu, comme vous avez fait jusqu'à ce jour.
9 “Ubangiji ya kori manyan ƙasashe masu ƙarfi; har wa yau ba wanda ya iya cin ku da yaƙi.
C'est pour cela que l'Eternel a dépossédé de devant vous des nations grandes et fortes; et quant à vous, nul n'a subsisté devant vous jusqu'à ce jour.
10 Mutum ɗaya a cikinku ya isa yă sa mutane dubu nasu su gudu, domin Ubangiji Allahnku yana yaƙi dominku, kamar yadda ya yi alkawari.
Un seul homme d'entre vous en poursuivra mille; car l'Eternel votre Dieu est celui qui combat pour vous, comme il vous en a parlé.
11 Saboda haka sai ku kula da kanku sosai, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku.
Prenez donc garde soigneusement sur vos âmes, que vous aimiez l'Eternel votre Dieu.
12 “Amma in kuka juya baya kuka zama abokai ga waɗanda suka ragu suke zama a cikinku a ƙasashen nan, har kuka yi auratayya da su, kuka haɗa kai da su,
Autrement si vous vous en détournez en aucune manière et que vous vous attachiez au reste de ces nations, [savoir] à ceux qui sont demeurés de reste avec vous, et que vous fassiez alliance avec eux, et que vous vous mêliez avec eux, et eux avec vous;
13 ku tabbata cewa Ubangiji Allahnku ba zai kore muku mutanen ƙasashen nan ba, sai ma su zama muku dutsen tuntuɓe da tarko, za su zama bulala a bayanku, ƙayayyuwa a idanunku, har sai kun hallaka daga wannan ƙasa mai kyau wadda Ubangiji Allahnku ya ba ku.
Sachez certainement que l'Eternel votre Dieu ne continuera plus à déposséder ces nations devant vous; mais elles vous seront en pièges, et en filet, et comme un fléau à vos côtés, et comme des épines à vos yeux, jusqu'à ce que vous périssiez de dessus cette bonne terre que l'Eternel votre Dieu vous a donnée.
14 “Yanzu na kusa barin fuskar duniyan nan. Kun sani da dukan zuciyarku, da dukan ranku cewa, Ba ko ɗaya daga cikin alkawuran da Ubangiji Allahnku ya yi, da bai cika ba. Kowane alkawari ya cika; ba ko ɗaya da bai cika ba.
Or voici, je m'en vais aujourd'hui par le chemin de toute la terre; et vous connaîtrez dans tout votre cœur, et dans toute votre âme qu'il n'est point tombé un seul mot de toutes les bonnes paroles que l'Eternel votre Dieu a dites de vous; tout vous est arrivé, il n'en est pas tombé un seul mot.
15 Kamar yadda Ubangiji Allahnku kuwa ya cika kowane alkawari mai kyau, haka ma ba zai fasa kawo muku bala’in da ya faɗi ba, sai ya hallaka ku daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba ku.
Et il arrivera que comme toutes les bonnes paroles que l'Eternel votre Dieu vous avait dites vous sont arrivées; ainsi l'Eternel fera venir sur vous toutes les mauvaises paroles, jusqu'à ce qu'il vous ait exterminés de dessus cette bonne terre que l'Eternel votre Dieu vous a donnée.
16 In kuka karya alkawarin Ubangiji Allahnku wanda ya umarce ku, in kuka je kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka rusuna musu, fushin Ubangiji zai sauko a kanku, za ku kuwa hallaka da sauri daga ƙasan nan mai kyau da ya ba ku.”
Quand vous aurez transgressé l'alliance de l'Eternel votre Dieu, qu'il vous a commandée, et que vous serez allés servir d'autres dieux, et vous serez prosternés devant eux, la colère de l'Eternel s'enflammera contre vous, et vous périrez incontinent de dessus cette bonne terre qu'il vous a donnée.

< Yoshuwa 23 >