< Yoshuwa 23 >

1 An daɗe bayan da Ubangiji ya ba Isra’ilawa hutu daga dukan abokan gāban da suke kewaye da su. Yoshuwa kuwa ya tsufa, shekarunsa sun yi yawa,
After many days, when Yahweh had given rest to Israel from all their enemies that around them, and Joshua was old and well advanced in years.
2 sai ya aika a kira Isra’ilawa duka, dattawansu, shugabanninsu, alƙalansu, da manyan ma’aikatansu, ya ce musu, “Na tsufa, shekaruna kuwa sun yi yawa,
Joshua called for all Israel—for their elders, for their leaders, for their judges, and for their officers—and he said to them, “I am very old.
3 ku kanku kun ga dukan abubuwan da Ubangiji Allahnku ya yi da idanunku wa dukan ƙasashen nan, Ubangiji Allahnku shi ne wanda ya yi yaƙi dominku.
You have seen everything that Yahweh your God has done to all these nations for your sake, for it is Yahweh your God who has fought for you.
4 Ku tuna yadda na rarraba wa kabilanku ƙasashen nan su zama naku na gādo, dukan ƙasashen da suka rage, ƙasashen da na ci da yaƙi, tsakanin Urdun da Bahar Rum a yamma.
Look! I have assigned to you the nations that remain to be conquered as an inheritance for your tribes, along with all the nations I have already destroyed, from the Jordan to the Great Sea in the west.
5 Ubangiji Allahnku kansa zai kore su a madadinku. Zai fafare su a gabanku, za ku kuwa mallaki ƙasarsu, yadda Ubangiji Allah ya yi muku alkawari.
Yahweh your God will drive them out. He will push them out from you. He will seize their land, and you will take possession of their land, just as Yahweh your God promised to you.
6 “Ku yi ƙarfin hali, ku yi hankali, ku yi biyayya da dukan abin da aka rubuta a cikin Littafin Dokoki na Musa, ba tare da kun juya hagu ko dama ba.
So be very strong, so that you keep and do all that is written in the Book of the Law of Moses, turning aside from it neither to the right hand nor to the left,
7 Kada ku haɗa kai da mutanen nan da suke zama cikinku; ba ruwanku da sunayen allolinsu, kada ku rantse da su. Kada kuwa ku bauta musu ko kuwa ku rusuna musu.
so you may not mix with these nations that remain among you or mention the names of their gods, swear by them, worship them, or bow down to them.
8 Sai dai ku riƙe Ubangiji Allahnku da kyau, yadda kuka yi har zuwa yanzu.
Instead, you must cling to Yahweh your God just as you have done to this day.
9 “Ubangiji ya kori manyan ƙasashe masu ƙarfi; har wa yau ba wanda ya iya cin ku da yaƙi.
For Yahweh has driven out before you large, strong nations. As for you, no one has been able to stand before you to this present day.
10 Mutum ɗaya a cikinku ya isa yă sa mutane dubu nasu su gudu, domin Ubangiji Allahnku yana yaƙi dominku, kamar yadda ya yi alkawari.
Any single man of your number will make a thousand run away, for Yahweh your God, is the one who fights for you, just as he promised you.
11 Saboda haka sai ku kula da kanku sosai, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku.
Pay particular attention, so that you love Yahweh your God.
12 “Amma in kuka juya baya kuka zama abokai ga waɗanda suka ragu suke zama a cikinku a ƙasashen nan, har kuka yi auratayya da su, kuka haɗa kai da su,
But if you turn back and cling to the survivors of these nations who remain among you, or if you intermarry with them, or if you come together with them and they with you,
13 ku tabbata cewa Ubangiji Allahnku ba zai kore muku mutanen ƙasashen nan ba, sai ma su zama muku dutsen tuntuɓe da tarko, za su zama bulala a bayanku, ƙayayyuwa a idanunku, har sai kun hallaka daga wannan ƙasa mai kyau wadda Ubangiji Allahnku ya ba ku.
then know for certain that Yahweh your God will no longer drive these nations out from among you. Instead, they will become a snare and a trap for you, whips on your backs and thorns in your eyes, until you perish from this good land that Yahweh your God has given you.
14 “Yanzu na kusa barin fuskar duniyan nan. Kun sani da dukan zuciyarku, da dukan ranku cewa, Ba ko ɗaya daga cikin alkawuran da Ubangiji Allahnku ya yi, da bai cika ba. Kowane alkawari ya cika; ba ko ɗaya da bai cika ba.
Now I am going the way of all the earth, and you know with all your hearts and souls that not one word has failed to come true of all the good things that Yahweh your God promised about you. All these things have come about for you. Not one of them has failed.
15 Kamar yadda Ubangiji Allahnku kuwa ya cika kowane alkawari mai kyau, haka ma ba zai fasa kawo muku bala’in da ya faɗi ba, sai ya hallaka ku daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba ku.
But just as every word Yahweh your God promised you has been fulfilled, so Yahweh will bring on you all the evil things until he has destroyed you from this good land that Yahweh your God has given you.
16 In kuka karya alkawarin Ubangiji Allahnku wanda ya umarce ku, in kuka je kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka rusuna musu, fushin Ubangiji zai sauko a kanku, za ku kuwa hallaka da sauri daga ƙasan nan mai kyau da ya ba ku.”
He will do this if you break the covenant of Yahweh your God, which he commanded you to keep. If you go and worship other gods and bow down to them, then the anger of Yahweh will be kindled against you, and you will quickly perish from the good land that he has given you.”

< Yoshuwa 23 >