< Yoshuwa 23 >

1 An daɗe bayan da Ubangiji ya ba Isra’ilawa hutu daga dukan abokan gāban da suke kewaye da su. Yoshuwa kuwa ya tsufa, shekarunsa sun yi yawa,
Efter længere Tids Forløb, da HERREN havde skaffet Israel Ro for alle dets Fjender rundt om, og Josua var blevet gammel og til Års,
2 sai ya aika a kira Isra’ilawa duka, dattawansu, shugabanninsu, alƙalansu, da manyan ma’aikatansu, ya ce musu, “Na tsufa, shekaruna kuwa sun yi yawa,
lod Josua hele Israel, de Ældste, Overhovederne, Dommerne og Tilsynsmændene kalde til sig og sagde til dem: "Jeg er blevet gammel og til Års.
3 ku kanku kun ga dukan abubuwan da Ubangiji Allahnku ya yi da idanunku wa dukan ƙasashen nan, Ubangiji Allahnku shi ne wanda ya yi yaƙi dominku.
I har selv set alt, hvad HERREN eders Gud har gjort ved alle disse Folkeslag foran eder; thi det var HERREN eders Gud, som kæmpede for eder.
4 Ku tuna yadda na rarraba wa kabilanku ƙasashen nan su zama naku na gādo, dukan ƙasashen da suka rage, ƙasashen da na ci da yaƙi, tsakanin Urdun da Bahar Rum a yamma.
Se, jeg har tildelt eders Stammer som Arvelod disse Folk, som er tilbage af alle de Folkeslag, jeg udryddede fra Jordan til det store Hav vestpå;
5 Ubangiji Allahnku kansa zai kore su a madadinku. Zai fafare su a gabanku, za ku kuwa mallaki ƙasarsu, yadda Ubangiji Allah ya yi muku alkawari.
og HERREN eders Gud vil trænge dem tilbage foran eder og drive dem bort foran eder, og I skal tage deres Land i Besiddelse, som HERREN eders Gud lovede eder.
6 “Ku yi ƙarfin hali, ku yi hankali, ku yi biyayya da dukan abin da aka rubuta a cikin Littafin Dokoki na Musa, ba tare da kun juya hagu ko dama ba.
Vær nu stærke og faste, så I giver Agt på og handler efter alt, hvad der står skrevet i Moses's Lovbog, og ikke viger derfra til højre eller venstre
7 Kada ku haɗa kai da mutanen nan da suke zama cikinku; ba ruwanku da sunayen allolinsu, kada ku rantse da su. Kada kuwa ku bauta musu ko kuwa ku rusuna musu.
og ikke indlader eder med disse Folk, som er tilbage iblandt eder; I må ikke påkalde deres Guders Navne eller sværge ved dem, ikke dyrke eller tilbede dem,
8 Sai dai ku riƙe Ubangiji Allahnku da kyau, yadda kuka yi har zuwa yanzu.
men I skal holde fast ved HERREN eders Gud som hidtil.
9 “Ubangiji ya kori manyan ƙasashe masu ƙarfi; har wa yau ba wanda ya iya cin ku da yaƙi.
Derfor drev jo HERREN store og mægtige Folkeslag bort foran eder. Ingen har kunnet holde Stand over for eder til denne Dag;
10 Mutum ɗaya a cikinku ya isa yă sa mutane dubu nasu su gudu, domin Ubangiji Allahnku yana yaƙi dominku, kamar yadda ya yi alkawari.
een Mand iblandt eder jog tusinde på Flugt; thi det var HERREN eders Gud, som kæmpede for eder, som han havde lovet eder.
11 Saboda haka sai ku kula da kanku sosai, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku.
Våg da for eders Livs Skyld omhyggeligt over, at I elsker HERREN eders Gud!
12 “Amma in kuka juya baya kuka zama abokai ga waɗanda suka ragu suke zama a cikinku a ƙasashen nan, har kuka yi auratayya da su, kuka haɗa kai da su,
Thi dersom I falder fra og slutter eder til Levningerne af disse Folk, som er tilbage iblandt eder, og, besvogrer eder med dem eller, indlader eder i Forbindelse med dem,
13 ku tabbata cewa Ubangiji Allahnku ba zai kore muku mutanen ƙasashen nan ba, sai ma su zama muku dutsen tuntuɓe da tarko, za su zama bulala a bayanku, ƙayayyuwa a idanunku, har sai kun hallaka daga wannan ƙasa mai kyau wadda Ubangiji Allahnku ya ba ku.
så skal I vide for vist, at HERREN eders Gud ikke mere vil drive disse Folkeslag bort fra eder, men de skal blive eder en Snare og en Fælde, en Svøbe i eders Sider og Torne i eders Øjne, indtil I selv bliver udryddet fra dette herlige Land, som HERREN eders Gud gav eder.
14 “Yanzu na kusa barin fuskar duniyan nan. Kun sani da dukan zuciyarku, da dukan ranku cewa, Ba ko ɗaya daga cikin alkawuran da Ubangiji Allahnku ya yi, da bai cika ba. Kowane alkawari ya cika; ba ko ɗaya da bai cika ba.
Se, jeg går nu al Støvets Gang; så betænk da med hele eders Hjerte og hele eders Sjæl, at ikke eet af alle de gode Ord, HERREN eders Gud talede til eder, faldt til Jorden; alle sammen er de gået i Opfyldelse for eder; ikke eet Ord deraf faldt til Jorden.
15 Kamar yadda Ubangiji Allahnku kuwa ya cika kowane alkawari mai kyau, haka ma ba zai fasa kawo muku bala’in da ya faɗi ba, sai ya hallaka ku daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba ku.
Men ligesom alle de gode Ord, HERREN eders Gud talede til eder, gik i Opfyldelse på eder, således vil HERREN også lade alle sine Trusler gå i Opfyldelse på eder, indtil han har udryddet eder fra dette herlige Land, som HERREN eders Gud gav eder.
16 In kuka karya alkawarin Ubangiji Allahnku wanda ya umarce ku, in kuka je kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka rusuna musu, fushin Ubangiji zai sauko a kanku, za ku kuwa hallaka da sauri daga ƙasan nan mai kyau da ya ba ku.”
Når I overtræder HERREN eders Guds Pagt, som han pålagde eder, og går hen og Dyrker andre Guder og tilbeder dem, så vil HERRENs Vrede blusse op imod eder, og I vil hastelig blive udryddet fra det herlige Land, han gav eder!"

< Yoshuwa 23 >