< Yoshuwa 21 >

1 To, a lokacin, sai shugabannin iyalan Lawiyawa suka je wurin Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun da kuma shugabannin sauran iyalan kabilu na Isra’ila a
Et les Chefs de famille des Lévites s'approchèrent du Prêtre Eléazar et de Josué, fils de Nun, et des Chefs de famille des Tribus des enfants d'Israël,
2 Shilo cikin Kan’ana, suka ce musu, “Ubangiji ya yi umarni ta wurin Musa cewa a ba mu garuruwan da za mu zauna a ciki, da wurin kiwo mai kyau don dabbobinmu.”
et leur parlèrent à Silo, dans le pays de Canaan, en ces termes: L'Éternel a ordonné par l'organe de Moïse qu'on nous donne des villes pour nous loger, avec leurs banlieues pour notre bétail.
3 Saboda haka kamar yadda Ubangiji ya umarta, sai Isra’ilawa suka ba wa Lawiyawa waɗannan garuruwa da wuraren kiwo daga cikin gādonsu.
Alors les enfants d'Israël donnèrent aux Lévites, sur leur propriété, d'après l'ordre de l'Éternel, ces villes et leurs banlieues.
4 Ƙuri’a ta farko ta fāɗa a kan Kohatawa bisa ga iyalansu. Sai aka ba wa Lawiyawa waɗanda suke’yan zuriyar Haruna, firist, garuruwa goma sha uku daga kabilan Yahuda, Simeyon da Benyamin.
Et le sort fut tiré pour les familles des Kahathites. Et les fils du Prêtre Aaron d'entre les Lévites obtinrent par le sort, de la Tribu de Juda et de la Tribu de Siméon et de la Tribu de Benjamin, treize villes.
5 Sauran Kohatawan kuma aka ba su garuruwa goma daga iyalan kabilar Efraim, Dan da kuma rabi kabilar Manasse.
Et les fils de Kahath restants obtinrent par le sort, des familles de la Tribu d'Ephraïm et de la Tribu de Dan et de la demi-Tribu de Manassé, dix villes.
6 Aka kuma ba wa zuriyar Gershon garuruwa goma sha uku daga iyalan kabilan Issakar, Asher, Naftali, da kuma rabin kabilar Manasse a Bashan.
Et les fils de Gerson obtinrent par le sort, des familles de la Tribu d'Issaschar et de la Tribu d'Asser et de la Tribu de Nephthali et de la [seconde] moitié de la Tribu de Manassé en Basan, treize villes.
7 Aka ba wa zuriyar Merari bisa ga iyalansu, garuruwa goma sha biyu daga kabilan Ruben, Gad da Zebulun.
Les fils de Merari, en raison de leurs familles, obtinrent de la Tribu de Ruben et de la Tribu de Gad et de la Tribu de Zabulon, douze villes.
8 Haka Isra’ilawa suka ba wa Lawiyawa waɗannan garuruwa da wuraren kiwo masu kyau, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
Ainsi les enfants d'Israël donnèrent par le sort aux Lévites ces villes-là et leurs banlieues, comme l'Éternel l'avait ordonné par l'organe de Moïse.
9 Daga kabilan Yahuda da Simeyon ne aka ba su waɗannan garuruwan da aka ambata,
Et de la Tribu des fils de Juda, et de la Tribu des fils de Siméon ils donnèrent ces villes qui vont être indiquées nominativement.
10 (ga garuruwan da aka ba wa zuriyar Haruna waɗanda suke daga iyalan Kohatawa na Lawiyawa, domin ƙuri’a ta farko ta fāɗa a kansu),
Aux fils d'Aaron, familles des Kahathites, enfants de Lévi (car ils eurent le premier lot)
11 an ba su, Kiriyat Arba (wato, Hebron), da wurin kiwon da yake kewaye da ƙasar kan tudu ta Yahuda. (Arba shi ne kakan Anak.)
ils donnèrent la ville d'Arba (celui-ci est le père des Anakites), c'est-à-dire, Hébron dans la montagne de Juda et sa banlieue d'alentour.
12 Amma sai aka ba Kaleb ɗan Yefunne filayen da kuma ƙauyukan da suke kewaye da birnin, su zama nasa.
Quant à la campagne de la ville et à ses villages, ils les donnèrent à Caleb, fils de Jéphuné, en propriété.
13 Sai aka ba zuriyar Haruna firist, ƙasar Hebron (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), da Libna,
Et aux fils du Prêtre Aaron ils donnèrent la ville de refuge pour l'homicide, Hébron et sa banlieue, et Libna et sa banlieue
14 da Yattir, da Eshtemowa,
et Jatkthir et sa banlieue, et Esthmoa et sa banlieue,
15 da Holon, da Debir,
et Holon et sa banlieue, et Débir et sa banlieue,
16 da Ayin, da Yutta, da kuma Bet-Shemesh, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa tara ke nan daga kabilun nan biyu, Yahuda da Simeyon.
et Aïn et sa banlieue, et Jutta et sa banlieue, et Beth-Semès et sa banlieue: neuf villes de ces deux Tribus;
17 Daga kabilar Benyamin kuwa aka ba su, Gibeyon, Geba,
et de la Tribu de Benjamin, Gabaon et sa banlieue,
18 Anatot da Almon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
et Geba et sa banlieue: et Anathoth et sa banlieue, et Almon et sa banlieue, quatre villes.
19 Duka-duka garuruwan firistoci, zuriyar Haruna, su goma sha uku ne tare da wuraren kiwonsu.
Total des villes des Prêtres, fils d'Aaron: treize villes avec leurs banlieues.
20 Aka kuma ba wa sauran Kohatawa, iyalan Lawiyawa, garuruwa daga kabilar Efraim.
Et quant aux familles des fils de Kahath, Lévites restants des fils de Kahath, les villes de leur lot étaient de la Tribu d'Ephraïm.
21 A ƙasar kan tudu ta Efraim, aka ba su, Shekem (garin masu neman mafaka don sun yi kisa) da Gezer,
Et ils leur donnèrent la ville de refuge pour l'homicide, Sichem et sa banlieue dans la montagne d'Ephraïm, et Gézer et sa banlieue,
22 Kibzayim da Bet-Horon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
et Kibtsaïm et sa banlieue, et Beth-Horon et sa banlieue: quatre villes;
23 Haka kuma daga kabilar Dan, aka ba su, Elteke, Gibbeton,
et de la Tribu de Dan, Elthékê et sa banlieue, Gibthon et sa banlieue,
24 Aiyalon da Gat-Rimmon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
Ajalon et sa banlieue, Gath-Rimmon et sa banlieue: quatre villes;
25 Daga rabin kabilar Manasse kuwa aka ba su, Ta’anak da Gat-Rimmon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa biyu ke nan.
et de la demi-Tribu de Manassé, Thaënach et sa banlieue, et Gath-Rimmon et sa banlieue: deux villes;
26 Dukan garuruwan nan goma tare da wuraren kiwonsu ne aka ba sauran iyalan Kohatawa.
total, dix villes avec leurs banlieues pour les familles des fils de Kahath restants.
27 Aka ba wa zuriyar Gershon, waɗanda suke Lawiyawa, rabo. Daga rabin kabilar Manasse, Golan a cikin Bashan (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), da Be’eshtera, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa biyu ke nan;
Et aux fils de Gerson, des familles des Lévites, de la demi-Tribu de Manassé, la ville de refuge pour l'homicide, Golan en Basan et sa banlieue, et Béesthra et sa banlieue: deux villes;
28 daga kabilar Issakar kuma aka ba su Kishiyon, Daberat,
et de la Tribu d'Issaschar, Kisjon et sa banlieue,
29 Yarmut da En Gannim, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Dabrath et sa banlieue, Jarmuth et sa banlieue, Ein-Gannim et sa banlieue: quatre villes;
30 daga kabilar Asher kuwa aka ba su, Mishal, Abdon,
et de la Tribu d'Asser, Miseal et sa banlieue, Abdon et sa banlieue,
31 Helkat da Rehob, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Helkath et sa banlieue, et Rehob et sa banlieue: quatre villes;
32 daga kabilar Naftali kuma aka ba su, Kedesh a cikin Galili (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Hammon-Dor da kuma Kartan, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa uku ke nan.
et de la Tribu de Nephthali, la ville de refuge pour l'homicide, Kédès en Galilée et sa banlieue, et Hammoth-Dor et sa banlieue, et Karthan et sa banlieue: trois villes.
33 Duka-duka, garuruwan iyalan Gershonawa goma sha uku ne, tare da wuraren kiwonsu.
Total des villes des Gersonites, en raison de leurs familles: treize villes avec leurs banlieues.
34 Aka ba wa iyalan Merari (sauran Lawiyawa) garuruwa, daga kabilar Zebulun, wato, Yokneyam, Karta,
Et aux familles des fils de Merari, Lévites restants, de la Tribu de Zabulon, Jockneam et sa banlieue, Kartha et sa banlieue,
35 Dimna da kuma Nahalal, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Dimna et sa banlieue, Nahalal et sa banlieue: quatre villes;
36 daga kabilar Ruben kuma aka ba su, Bezer, Yahza,
et de la Tribu de Ruben, Betser, et sa banlieue, et Jahtsah et sa banlieue,
37 Kedemot da kuma Mefa’at, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Kedémoth et sa banlieue, et Mephaath et sa banlieue: quatre villes;
38 daga kabilar Gad kuwa aka ba su, Ramot Gileyad (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Mahanayim,
et de la Tribu de Gad, la ville de refuge pour l'homicide, Ramoth en Galaad et sa banlieue,
39 Heshbon da kuma Yazer, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
et Mahanaïm et sa banlieue, Hesbon et sa banlieue, Jaëzer et sa banlieue; total des villes: quatre.
40 Duka-duka garuruwan da aka ba iyalan mutanen Merari, waɗanda su ne sauran Lawiyawa, garuruwa goma sha biyu ne.
Total des villes des fils de Merari, selon leurs familles, du reste des familles des Lévites, lot qui leur échut: douze villes.
41 Jimillar birane da wurarensu na kiwon da aka ba Lawiyawa daga cikin mallakar jama’ar Isra’ila guda arba’in da takwas ne.
Total des villes des Lévites enclavées dans la propriété des enfants d'Israël, quarante-huit villes avec leurs banlieues.
42 Dukan garuruwan nan kowannensu yana kewaye da wurin kiwo.
Et ces villes avaient chacune sa banlieue qui l'entourait; ainsi en était-il de toutes ces villes-là.
43 Ubangiji kuwa ya ba Isra’ilawa dukan ƙasar da ya yi wa kakanninsu alkawari, suka kuwa mallake ta, suka zauna a cikinta.
C'est ainsi que l'Éternel donna aux Israélites tout le pays qu'il avait juré de donner à leurs pères, et ils en prirent possession et s'y établirent.
44 Ubangiji ya ba su hutawa a kowane gefe kamar yadda ya yi wa kakanninsu alkawari, ba ko ɗaya daga cikin abokan gābansu da ya iya cinsu da yaƙi.
Et l'Éternel leur donna repos de tous les côtés conformément à la totalité du serment qu'il avait fait à leurs pères. Et aucun de leurs ennemis ne tint devant eux; l'Éternel livra tous leurs ennemis entre leurs mains.
45 Ubangiji kuwa ya cika kowane alkawarin alherin da ya yi wa mutanen Isra’ila.
Et de toutes les excellentes promesses que l'Éternel avait faites à la maison d'Israël, aucune ne tomba, tout s'accomplit.

< Yoshuwa 21 >