< Yoshuwa 21 >

1 To, a lokacin, sai shugabannin iyalan Lawiyawa suka je wurin Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun da kuma shugabannin sauran iyalan kabilu na Isra’ila a
Les chefs de famille des Lévites s’approchèrent du prêtre Eléazar, de Josué, fils de Nun, et des chefs de famille des tribus des enfants d’Israël;
2 Shilo cikin Kan’ana, suka ce musu, “Ubangiji ya yi umarni ta wurin Musa cewa a ba mu garuruwan da za mu zauna a ciki, da wurin kiwo mai kyau don dabbobinmu.”
ils leur parlèrent à Silo, dans le pays de Chanaan, en disant: « Yahweh a ordonné par Moïse qu’on nous donnât des villes pour notre habitation, et leurs banlieues pour notre bétail. »
3 Saboda haka kamar yadda Ubangiji ya umarta, sai Isra’ilawa suka ba wa Lawiyawa waɗannan garuruwa da wuraren kiwo daga cikin gādonsu.
Les enfants d’Israël donnèrent aux Lévites, sur leur héritage, selon l’ordre de Yahweh, les villes suivantes et leurs banlieues.
4 Ƙuri’a ta farko ta fāɗa a kan Kohatawa bisa ga iyalansu. Sai aka ba wa Lawiyawa waɗanda suke’yan zuriyar Haruna, firist, garuruwa goma sha uku daga kabilan Yahuda, Simeyon da Benyamin.
Le sort fut tiré d’abord pour les familles des Caathites; et les fils du prêtre Aaron, d’entre les Lévites, obtinrent par le sort treize villes de la tribu de Juda, de la tribu de Siméon et de la tribu de Benjamin;
5 Sauran Kohatawan kuma aka ba su garuruwa goma daga iyalan kabilar Efraim, Dan da kuma rabi kabilar Manasse.
les autres fils de Caath obtinrent par le sort dix villes des familles de la tribu d’Ephraïm, de la tribu de Dan et de la demi-tribu de Manassé.
6 Aka kuma ba wa zuriyar Gershon garuruwa goma sha uku daga iyalan kabilan Issakar, Asher, Naftali, da kuma rabin kabilar Manasse a Bashan.
Les fils de Gerson obtinrent par le sort treize villes des familles de la tribu d’Issachar, de la tribu d’Aser, de la tribu de Nephthali et de la demi-tribu de Manassé en Basan.
7 Aka ba wa zuriyar Merari bisa ga iyalansu, garuruwa goma sha biyu daga kabilan Ruben, Gad da Zebulun.
Les fils de Mérari, selon leurs familles, obtinrent douze villes de la tribu de Ruben, de la tribu de Gad et de la tribu de Zabulon.
8 Haka Isra’ilawa suka ba wa Lawiyawa waɗannan garuruwa da wuraren kiwo masu kyau, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
Les enfants d’Israël donnèrent par le sort aux Lévites, ces villes et leurs banlieues, comme Yahweh l’avait ordonné par Moïse.
9 Daga kabilan Yahuda da Simeyon ne aka ba su waɗannan garuruwan da aka ambata,
Ils donnèrent de la tribu des fils de Juda et de la tribu des fils de Siméon les villes suivantes désignées par leurs noms;
10 (ga garuruwan da aka ba wa zuriyar Haruna waɗanda suke daga iyalan Kohatawa na Lawiyawa, domin ƙuri’a ta farko ta fāɗa a kansu),
ce fut pour les fils d’Aaron, d’entre les familles des Caathites, d’entre les fils de Lévi, car le sort fut d’abord tiré pour eux.
11 an ba su, Kiriyat Arba (wato, Hebron), da wurin kiwon da yake kewaye da ƙasar kan tudu ta Yahuda. (Arba shi ne kakan Anak.)
Ils leurs donnèrent, dans la montagne de Juda, la ville d’Arbé, père d’Enac, laquelle est Hébron, et sa banlieue tout autour.
12 Amma sai aka ba Kaleb ɗan Yefunne filayen da kuma ƙauyukan da suke kewaye da birnin, su zama nasa.
Mais la campagne de cette ville et ses villages, ils les donnèrent en possession à Caleb, fils de Jéphoné.
13 Sai aka ba zuriyar Haruna firist, ƙasar Hebron (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), da Libna,
Ils donnèrent aux fils du prêtre Aaron la ville de refuge pour le meurtrier, Hébron et sa banlieue, ainsi que Lebna avec sa banlieue,
14 da Yattir, da Eshtemowa,
Jéther et sa banlieue, Estémo et sa banlieue,
15 da Holon, da Debir,
Holon et sa banlieue, Dabir et sa banlieue,
16 da Ayin, da Yutta, da kuma Bet-Shemesh, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa tara ke nan daga kabilun nan biyu, Yahuda da Simeyon.
Aïn et sa banlieue, Jéta et sa banlieue, Bethsamès et sa banlieue: neuf villes de ces deux tribus.
17 Daga kabilar Benyamin kuwa aka ba su, Gibeyon, Geba,
De la tribu de Benjamin: Gabaon et sa banlieue, Gabaa et sa banlieue,
18 Anatot da Almon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
Anathoth et sa banlieue, Almon et sa banlieue: quatre villes.
19 Duka-duka garuruwan firistoci, zuriyar Haruna, su goma sha uku ne tare da wuraren kiwonsu.
Total des villes des prêtres, fils d’Aaron: treize villes et leurs banlieues.
20 Aka kuma ba wa sauran Kohatawa, iyalan Lawiyawa, garuruwa daga kabilar Efraim.
Quant aux familles des fils de Caath, Lévites, aux autres fils de Caath, les villes qui leur échurent par le sort furent de la tribu d’Ephraïm.
21 A ƙasar kan tudu ta Efraim, aka ba su, Shekem (garin masu neman mafaka don sun yi kisa) da Gezer,
Les enfants d’Israël leur donnèrent la ville de refuge pour le meurtrier, Sichem et sa banlieue, dans la montagne d’Ephraïm, ainsi que Gazer et sa banlieue,
22 Kibzayim da Bet-Horon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
Cibsaïm et sa banlieue, Beth-Horon et sa banlieue: quatre villes.
23 Haka kuma daga kabilar Dan, aka ba su, Elteke, Gibbeton,
De la tribu de Dan: Elthéco et sa banlieue, Gabathon et sa banlieue,
24 Aiyalon da Gat-Rimmon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
Ajalon et sa banlieue, Geth-Remmon et sa banlieue: quatre villes.
25 Daga rabin kabilar Manasse kuwa aka ba su, Ta’anak da Gat-Rimmon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa biyu ke nan.
De la demi-tribu de Manassé: Thanach et sa banlieue, et Geth-Remmon et sa banlieue: deux villes.
26 Dukan garuruwan nan goma tare da wuraren kiwonsu ne aka ba sauran iyalan Kohatawa.
Total: dix villes avec leurs banlieues, pour les familles des autres fils de Caath.
27 Aka ba wa zuriyar Gershon, waɗanda suke Lawiyawa, rabo. Daga rabin kabilar Manasse, Golan a cikin Bashan (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), da Be’eshtera, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa biyu ke nan;
Aux fils de Gerson, d’entre les familles des Lévites, ils donnèrent, de la demi-tribu de Manassé, la ville de refuge pour le meurtrier, Gaulon, en Basan, et sa banlieue, ainsi que Bosra et sa banlieue: deux villes.
28 daga kabilar Issakar kuma aka ba su Kishiyon, Daberat,
De la tribu d’Issachar: Césion et sa banlieue, Dabéreth et sa banlieue,
29 Yarmut da En Gannim, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Jaramoth et sa banlieue, En-Gannim et sa banlieue: quatre villes.
30 daga kabilar Asher kuwa aka ba su, Mishal, Abdon,
De la tribu d’Aser: Masal et sa banlieue, Abdon et sa banlieue,
31 Helkat da Rehob, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Helcath et sa banlieue, Rohob et sa banlieue: quatre villes.
32 daga kabilar Naftali kuma aka ba su, Kedesh a cikin Galili (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Hammon-Dor da kuma Kartan, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa uku ke nan.
De la tribu de Nephthali: la ville de refuge pour le meurtrier, Cédès en Galilée et sa banlieue, ainsi que Hamoth-Dor et sa banlieue, Carthan et sa banlieue: trois villes.
33 Duka-duka, garuruwan iyalan Gershonawa goma sha uku ne, tare da wuraren kiwonsu.
Total des villes des Gersonites, selon leurs familles: treize villes et leurs banlieues.
34 Aka ba wa iyalan Merari (sauran Lawiyawa) garuruwa, daga kabilar Zebulun, wato, Yokneyam, Karta,
Aux familles des fils de Mérari, au reste des Lévites, ils donnèrent, de la tribu de Zabulon: Jecnam et sa banlieue, Cartha et sa banlieue,
35 Dimna da kuma Nahalal, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Damna et sa banlieue, Naalol et sa banlieue: quatre villes.
36 daga kabilar Ruben kuma aka ba su, Bezer, Yahza,
Et de la tribu de Ruben, Bosor et sa banlieue, Jassa et sa banlieue,
37 Kedemot da kuma Mefa’at, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Cédémoth et sa banlieue, Méphaath et sa banlieue: quatre villes.
38 daga kabilar Gad kuwa aka ba su, Ramot Gileyad (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Mahanayim,
Et de la tribu de Gad: la ville de refuge pour le meurtrier, Ramoth en Galaad et sa banlieue, ainsi que Manaïm et sa banlieue,
39 Heshbon da kuma Yazer, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
Hésebon et sa banlieue, Jaser et sa banlieue: en tout quatre villes.
40 Duka-duka garuruwan da aka ba iyalan mutanen Merari, waɗanda su ne sauran Lawiyawa, garuruwa goma sha biyu ne.
Total des villes assignées par le sort aux fils de Mérari, selon leurs familles, formant le reste des familles des Lévites: douze villes.
41 Jimillar birane da wurarensu na kiwon da aka ba Lawiyawa daga cikin mallakar jama’ar Isra’ila guda arba’in da takwas ne.
Total des villes des Lévites au milieu des possessions des enfants d’Israël: quarante-huit villes et leurs banlieues.
42 Dukan garuruwan nan kowannensu yana kewaye da wurin kiwo.
Chacune de ces villes avait sa banlieue tout autour; il en était ainsi pour toutes ces villes.
43 Ubangiji kuwa ya ba Isra’ilawa dukan ƙasar da ya yi wa kakanninsu alkawari, suka kuwa mallake ta, suka zauna a cikinta.
C’est ainsi que Yahweh donna à Israël tout le pays qu’il avait juré de donner à leurs pères; ils en prirent possession et s’y établirent.
44 Ubangiji ya ba su hutawa a kowane gefe kamar yadda ya yi wa kakanninsu alkawari, ba ko ɗaya daga cikin abokan gābansu da ya iya cinsu da yaƙi.
Yahweh leur accorda du repos tout autour d’eux, comme il l’avait juré à leurs pères; aucun de leurs ennemis ne put leur résister, et Yahweh les livra tous entre leurs mains.
45 Ubangiji kuwa ya cika kowane alkawarin alherin da ya yi wa mutanen Isra’ila.

< Yoshuwa 21 >