< Yoshuwa 21 >
1 To, a lokacin, sai shugabannin iyalan Lawiyawa suka je wurin Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun da kuma shugabannin sauran iyalan kabilu na Isra’ila a
And they approached [the] leaders of [the] fathers of the Levites to Eleazar the priest and to Joshua [the] son of Nun and to [the] leaders of [the] fathers of the tribes of [the] people of Israel.
2 Shilo cikin Kan’ana, suka ce musu, “Ubangiji ya yi umarni ta wurin Musa cewa a ba mu garuruwan da za mu zauna a ciki, da wurin kiwo mai kyau don dabbobinmu.”
And they spoke to them at Shiloh in [the] land of Canaan saying Yahweh he commanded by [the] hand of Moses to give to us cities to dwell in and pasture lands their for livestock our.
3 Saboda haka kamar yadda Ubangiji ya umarta, sai Isra’ilawa suka ba wa Lawiyawa waɗannan garuruwa da wuraren kiwo daga cikin gādonsu.
And they gave [the] people of Israel to the Levites some of inheritance their to [the] mouth of Yahweh the cities these and pasture lands their.
4 Ƙuri’a ta farko ta fāɗa a kan Kohatawa bisa ga iyalansu. Sai aka ba wa Lawiyawa waɗanda suke’yan zuriyar Haruna, firist, garuruwa goma sha uku daga kabilan Yahuda, Simeyon da Benyamin.
And it came out the lot of [the] clans of the Kohathite[s] and it belonged to [the] descendants of Aaron the priest of the Levites from [the] tribe of Judah and from [the] tribe of the Simeonite[s] and from [the] tribe of Benjamin by the lot cities thir-teen.
5 Sauran Kohatawan kuma aka ba su garuruwa goma daga iyalan kabilar Efraim, Dan da kuma rabi kabilar Manasse.
And [belonged] to [the] descendants of Kohath which remained from [the] clans of [the] tribe of Ephraim and from [the] tribe of Dan and from [the] half of [the] tribe of Manasseh by the lot cities ten.
6 Aka kuma ba wa zuriyar Gershon garuruwa goma sha uku daga iyalan kabilan Issakar, Asher, Naftali, da kuma rabin kabilar Manasse a Bashan.
And [belonged] to [the] descendants of Gershon from [the] clans of [the] tribe of Issachar and from [the] tribe of Asher and from [the] tribe of Naphtali and from [the] half of [the] tribe of Manasseh in Bashan by the lot cities thir-teen.
7 Aka ba wa zuriyar Merari bisa ga iyalansu, garuruwa goma sha biyu daga kabilan Ruben, Gad da Zebulun.
[and belonged] to [the] descendants of Merari to clans their from [the] tribe of Reuben and from [the] tribe of Gad and from [the] tribe of Zebulun cities two [plus] ten.
8 Haka Isra’ilawa suka ba wa Lawiyawa waɗannan garuruwa da wuraren kiwo masu kyau, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
And they gave [the] people of Israel to the Levites the cities these and pasture lands their just as he had commanded Yahweh by [the] hand of Moses by the lot.
9 Daga kabilan Yahuda da Simeyon ne aka ba su waɗannan garuruwan da aka ambata,
And they gave from [the] tribe of [the] descendants of Judah and from [the] tribe of [the] descendants of Simeon the cities these which he called them by name.
10 (ga garuruwan da aka ba wa zuriyar Haruna waɗanda suke daga iyalan Kohatawa na Lawiyawa, domin ƙuri’a ta farko ta fāɗa a kansu),
And it belonged to [the] descendants of Aaron one of [the] clans of the Kohathite[s] from [the] descendants of Levi for to them it belonged the lot first.
11 an ba su, Kiriyat Arba (wato, Hebron), da wurin kiwon da yake kewaye da ƙasar kan tudu ta Yahuda. (Arba shi ne kakan Anak.)
And they gave to them Kiriath Arba [the] father of Anak that [is] Hebron in [the] hill country of Judah and pasture lands its around it.
12 Amma sai aka ba Kaleb ɗan Yefunne filayen da kuma ƙauyukan da suke kewaye da birnin, su zama nasa.
And [the] field[s] of the city and villages its they gave to Caleb [the] son of Jephunneh possession his.
13 Sai aka ba zuriyar Haruna firist, ƙasar Hebron (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), da Libna,
And to [the] descendants of - Aaron the priest they gave [the] city of refuge of the killer Hebron and pasture lands its and Libnah and pasture lands its.
14 da Yattir, da Eshtemowa,
And Jattir and pasture lands its and Eshtemoa and pasture lands its.
And Holon and pasture lands its and Debir and pasture lands its.
16 da Ayin, da Yutta, da kuma Bet-Shemesh, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa tara ke nan daga kabilun nan biyu, Yahuda da Simeyon.
And Ain and pasture lands its and Juttah and pasture lands its Beth Shemesh and pasture lands its cities nine from with [the] two the tribes these.
17 Daga kabilar Benyamin kuwa aka ba su, Gibeyon, Geba,
And from [the] tribe of Benjamin Gibeon and pasture lands its Geba and pasture lands its.
18 Anatot da Almon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
Anathoth and pasture lands its and Almon and pasture lands its cities four.
19 Duka-duka garuruwan firistoci, zuriyar Haruna, su goma sha uku ne tare da wuraren kiwonsu.
All [the] cities of [the] descendants of Aaron the priests [were] thir-teen cities and pasture lands their.
20 Aka kuma ba wa sauran Kohatawa, iyalan Lawiyawa, garuruwa daga kabilar Efraim.
And to [the] clans of [the] descendants of Kohath the Levites who remained of [the] descendants of Kohath and it was [the] cities of lot their from [the] tribe of Ephraim.
21 A ƙasar kan tudu ta Efraim, aka ba su, Shekem (garin masu neman mafaka don sun yi kisa) da Gezer,
And they gave to them [the] city of refuge of the killer Shechem and pasture lands its in [the] hill country of Ephraim and Gezer and pasture lands its.
22 Kibzayim da Bet-Horon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
And Kibzaim and pasture lands its and Beth Horon and pasture lands its cities four.
23 Haka kuma daga kabilar Dan, aka ba su, Elteke, Gibbeton,
And from [the] tribe of Dan Eltekeh and pasture lands its Gibbethon and pasture lands its.
24 Aiyalon da Gat-Rimmon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
Aijalon and pasture lands its Gath Rimmon and pasture lands its cities four.
25 Daga rabin kabilar Manasse kuwa aka ba su, Ta’anak da Gat-Rimmon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa biyu ke nan.
And from [the] half of [the] tribe of Manasseh Taanach and pasture lands its and Gath Rimmon and pasture lands its cities two.
26 Dukan garuruwan nan goma tare da wuraren kiwonsu ne aka ba sauran iyalan Kohatawa.
All [the] cities ten and pasture lands their [belonged] to [the] clans of [the] descendants of Kohath which remained.
27 Aka ba wa zuriyar Gershon, waɗanda suke Lawiyawa, rabo. Daga rabin kabilar Manasse, Golan a cikin Bashan (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), da Be’eshtera, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa biyu ke nan;
And to [the] descendants of Gershon from [the] clans of the Levites from [the] half of [the] tribe of Manasseh [the] city of refuge of the killer (Golan *Q(K)*) in Bashan and pasture lands its and Beeshtarah and pasture lands its cities two.
28 daga kabilar Issakar kuma aka ba su Kishiyon, Daberat,
And from [the] tribe of Issachar Kishion and pasture lands its Daberath and pasture lands its.
29 Yarmut da En Gannim, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Jarmuth and pasture lands its En Gannim and pasture lands its cities four.
30 daga kabilar Asher kuwa aka ba su, Mishal, Abdon,
And from [the] tribe of Asher Mishal and pasture lands its Abdon and pasture lands its.
31 Helkat da Rehob, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Helkath and pasture lands its and Rehob and pasture lands its cities four.
32 daga kabilar Naftali kuma aka ba su, Kedesh a cikin Galili (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Hammon-Dor da kuma Kartan, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa uku ke nan.
And from [the] tribe of Naphtali [the] city of - refuge of the killer Kedesh in Galilee and pasture lands its and Hammoth Dor and pasture lands its and Kartan and pasture lands its cities three.
33 Duka-duka, garuruwan iyalan Gershonawa goma sha uku ne, tare da wuraren kiwonsu.
All [the] cities of the Gershonite[s] to clans their [were] thir-teen citi[es] and pasture lands their.
34 Aka ba wa iyalan Merari (sauran Lawiyawa) garuruwa, daga kabilar Zebulun, wato, Yokneyam, Karta,
And to [the] clans of [the] descendants of Merari the Levites which remained from with [the] tribe of Zebulun Jokneam and pasture lands its Kartah and pasture lands its.
35 Dimna da kuma Nahalal, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Dimnah and pasture lands its Nahalal and pasture lands its cities four.
36 daga kabilar Ruben kuma aka ba su, Bezer, Yahza,
(And from [the] tribe of Reuben Bezer and pasture lands its and Jahaz and pasture lands its. *R*)
37 Kedemot da kuma Mefa’at, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
(Kedemoth and pasture lands its and Mephaath and pasture lands its cities four. *R*)
38 daga kabilar Gad kuwa aka ba su, Ramot Gileyad (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Mahanayim,
And from [the] tribe of Gad [the] city of refuge of the killer Ramoth in Gilead and pasture lands its and Mahanaim and pasture lands its.
39 Heshbon da kuma Yazer, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
Heshbon and pasture lands its Jazer and pasture lands its all [the] cities [were] four.
40 Duka-duka garuruwan da aka ba iyalan mutanen Merari, waɗanda su ne sauran Lawiyawa, garuruwa goma sha biyu ne.
All the cities of [the] descendants of Merari to clans their which remained of [the] clans of the Levites and it was lot their cities two [plus] ten.
41 Jimillar birane da wurarensu na kiwon da aka ba Lawiyawa daga cikin mallakar jama’ar Isra’ila guda arba’in da takwas ne.
All [the] cities of the Levites in [the] midst of [the] possession of [the] people of Israel [were] cities forty and eight and pasture lands their.
42 Dukan garuruwan nan kowannensu yana kewaye da wurin kiwo.
They were the cities these a city a city and pasture lands its around it thus for all the cities these.
43 Ubangiji kuwa ya ba Isra’ilawa dukan ƙasar da ya yi wa kakanninsu alkawari, suka kuwa mallake ta, suka zauna a cikinta.
And he gave Yahweh to Israel all the land which he had sworn to give to ancestors their and they took possession of it and they dwelt in it.
44 Ubangiji ya ba su hutawa a kowane gefe kamar yadda ya yi wa kakanninsu alkawari, ba ko ɗaya daga cikin abokan gābansu da ya iya cinsu da yaƙi.
And he gave rest Yahweh to them from round about according to all that he had sworn to ancestors their and not he stood anyone in faces their from all enemies their all enemies their he gave Yahweh in hand their.
45 Ubangiji kuwa ya cika kowane alkawarin alherin da ya yi wa mutanen Isra’ila.
Not it fell a word from every word good which he had spoken Yahweh to [the] house of Israel everything it came.