< Yoshuwa 21 >
1 To, a lokacin, sai shugabannin iyalan Lawiyawa suka je wurin Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun da kuma shugabannin sauran iyalan kabilu na Isra’ila a
Then came near the ancestral heads of the Levites, unto Eleazar, the priest, and unto Joshua son of Nun, —and unto the ancestral heads of the tribes, of the sons of Israel;
2 Shilo cikin Kan’ana, suka ce musu, “Ubangiji ya yi umarni ta wurin Musa cewa a ba mu garuruwan da za mu zauna a ciki, da wurin kiwo mai kyau don dabbobinmu.”
and spake unto them in Shiloh in the land of Canaan, saying: Yahweh himself, commanded, by the hand of Moses, that there should be given unto us cities to dwell in, —with their pasture-lands for our cattle.
3 Saboda haka kamar yadda Ubangiji ya umarta, sai Isra’ilawa suka ba wa Lawiyawa waɗannan garuruwa da wuraren kiwo daga cikin gādonsu.
So the sons of Israel gave unto the Levites, out of their own inheritance, at the bidding of Yahweh, —these cities, with their pasture-lands.
4 Ƙuri’a ta farko ta fāɗa a kan Kohatawa bisa ga iyalansu. Sai aka ba wa Lawiyawa waɗanda suke’yan zuriyar Haruna, firist, garuruwa goma sha uku daga kabilan Yahuda, Simeyon da Benyamin.
And, when the lot came out for the families of the Kohathites, then had the sons of Aaron the priest, from among the Levites—out of the tribe of Judah and out of the tribe of the Simeonites and out of the tribe of Benjamin—by lot, thirteen cities.
5 Sauran Kohatawan kuma aka ba su garuruwa goma daga iyalan kabilar Efraim, Dan da kuma rabi kabilar Manasse.
And, the sons of Kohath that remained, had—out of the families of the tribe of Ephraim and out of the tribe of Dan and out of the half tribe of Manasseh—by lot, ten cities.
6 Aka kuma ba wa zuriyar Gershon garuruwa goma sha uku daga iyalan kabilan Issakar, Asher, Naftali, da kuma rabin kabilar Manasse a Bashan.
And, the sons of Gershon, had—out of families of the tribe of Issachar and out of the tribe of Asher and out of the tribe of Naphtali and out of the half tribe of Manasseh in Bashan—by lot, thirteen cities.
7 Aka ba wa zuriyar Merari bisa ga iyalansu, garuruwa goma sha biyu daga kabilan Ruben, Gad da Zebulun.
The sons of Merari, by their families, had—out of the tribe of Reuben and out of the tribe of Gad and out of the tribe of Zebulun, twelve cities.
8 Haka Isra’ilawa suka ba wa Lawiyawa waɗannan garuruwa da wuraren kiwo masu kyau, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
So the sons of Israel gave unto the Levites these cities, with their pasture lands, —as Yahweh commanded, by the hand of Moses, by lot.
9 Daga kabilan Yahuda da Simeyon ne aka ba su waɗannan garuruwan da aka ambata,
Thus then they gave—out of the tribe of the sons of Judah and out of the tribe of the sons of Simeon—these cities which are mentioned by name.
10 (ga garuruwan da aka ba wa zuriyar Haruna waɗanda suke daga iyalan Kohatawa na Lawiyawa, domin ƙuri’a ta farko ta fāɗa a kansu),
And the sons of Aaron, from among the sons of Kohath, from among the sons of Levi, had them, —because, theirs, was the first lot;
11 an ba su, Kiriyat Arba (wato, Hebron), da wurin kiwon da yake kewaye da ƙasar kan tudu ta Yahuda. (Arba shi ne kakan Anak.)
yea there was given unto them, the city of Arba, the father of Anak, the same, is Hebron, in the hill country of Judah, —with the pasture land thereof, round about it;
12 Amma sai aka ba Kaleb ɗan Yefunne filayen da kuma ƙauyukan da suke kewaye da birnin, su zama nasa.
whereas, the fields of the city, and the villages thereof, gave they unto Caleb son of Jephunneh, as his possession.
13 Sai aka ba zuriyar Haruna firist, ƙasar Hebron (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), da Libna,
But, unto the sons of Aaron the priest, gave they the city of refuge for the manslayer, even Hebron, with the pasture lands thereof, —Libnah also, with her pasture lands;
14 da Yattir, da Eshtemowa,
and Jattir with her pasture land, and Eshtemoa with her pasture land;
and Holon, with her pasture land, and Debir, with her pasture land;
16 da Ayin, da Yutta, da kuma Bet-Shemesh, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa tara ke nan daga kabilun nan biyu, Yahuda da Simeyon.
and Ain, with her pasture land, and Juttah, with her pasture land, Beth-shemesh, with her pasture land, —nine cities, out of these two tribes.
17 Daga kabilar Benyamin kuwa aka ba su, Gibeyon, Geba,
And, out of the tribe of Benjamin, Gibeon, with her pasture land, —Geba, with her pasture land;
18 Anatot da Almon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
Anathoth, with her pasture land, and Almon, with her pasture land, —four cities.
19 Duka-duka garuruwan firistoci, zuriyar Haruna, su goma sha uku ne tare da wuraren kiwonsu.
All the cities of the sons of Aaron, the priests, were thirteen cities, with their pasture lands.
20 Aka kuma ba wa sauran Kohatawa, iyalan Lawiyawa, garuruwa daga kabilar Efraim.
And, as for the families of the sons of Kohath, the Levites, which remained of the sons of Kohath, the cities of their lot were out of the tribe of Ephraim.
21 A ƙasar kan tudu ta Efraim, aka ba su, Shekem (garin masu neman mafaka don sun yi kisa) da Gezer,
So they gave unto them a city of refuge for the manslayer, even Shechem with her pasture land, in the hill country of Ephraim, —also Gezer, with her pasture land;
22 Kibzayim da Bet-Horon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
and Kibzaim, with her pasture land, and Beth-horon, with her pasture land, —four cities.
23 Haka kuma daga kabilar Dan, aka ba su, Elteke, Gibbeton,
And, out of the tribe of Dan, Elteke, with her pasture land, —Gibbethon, with her pasture land;
24 Aiyalon da Gat-Rimmon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
Aijalon, with her pasture land, Gath-rimmon, with her pasture land, —four cities.
25 Daga rabin kabilar Manasse kuwa aka ba su, Ta’anak da Gat-Rimmon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa biyu ke nan.
And, out of the half tribe of Manasseh, Taanach, with her pasture land, and Gath-rimmon, with her pasture land, —two cities.
26 Dukan garuruwan nan goma tare da wuraren kiwonsu ne aka ba sauran iyalan Kohatawa.
All the cities, were ten, with their pasture lands: for the families of the sons of Kohath which remained.
27 Aka ba wa zuriyar Gershon, waɗanda suke Lawiyawa, rabo. Daga rabin kabilar Manasse, Golan a cikin Bashan (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), da Be’eshtera, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa biyu ke nan;
And, the sons of Gershon, of the families of the Levites, had, out of the half tribe of Manasseh, a city of refuge for the manslayer, even Golan in Bashan, with her pasture land, and Be-eshterah, with her pasture land, —two cities.
28 daga kabilar Issakar kuma aka ba su Kishiyon, Daberat,
And, out of the tribe of Issachar, Kishion, with her pasture land, —Daberath, with her pasture land;
29 Yarmut da En Gannim, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Jarmuth, with her pasture land, En-gannim, with her pasture land, —four cities.
30 daga kabilar Asher kuwa aka ba su, Mishal, Abdon,
And, out of the tribe of Asher, Mishal, with her pasture land, Abdon, with her pasture land;
31 Helkat da Rehob, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Helkath, with her pasture land, and Rehob, with her pasture land, —four cities.
32 daga kabilar Naftali kuma aka ba su, Kedesh a cikin Galili (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Hammon-Dor da kuma Kartan, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa uku ke nan.
And, out of the tribe of Naphtali, a city of refuge for the manslayer—even Kedesh in Galilee, with her pasture land, and Hammoth-dor, with her pasture land, and Kartan, with her pasture land, —three cities.
33 Duka-duka, garuruwan iyalan Gershonawa goma sha uku ne, tare da wuraren kiwonsu.
All, the cities of the Gershonites, by their families, were thirteen cities, with their pasture lands.
34 Aka ba wa iyalan Merari (sauran Lawiyawa) garuruwa, daga kabilar Zebulun, wato, Yokneyam, Karta,
And, unto the families of the sons of Merari, the Levites that remained, out of the tribe of Zebulun, Jokneam, with her pasture land, —Kartah, with her pasture land;
35 Dimna da kuma Nahalal, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Dimnah, with her pasture land, Nahalal, with her pasture land, —four cities.
36 daga kabilar Ruben kuma aka ba su, Bezer, Yahza,
And, out of the tribe of Reuben, Bezer, with her pasture land, —and Jahaz, with her pasture land;
37 Kedemot da kuma Mefa’at, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Kedemoth, with her pasture land and Mephaath, with her pasture land, —four cities.
38 daga kabilar Gad kuwa aka ba su, Ramot Gileyad (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Mahanayim,
And, out of the tribe of Gad, a city of refuge for the manslayer—even Ramoth in Gilead, with her pasture land, —and Mahanaim, with her pasture land;
39 Heshbon da kuma Yazer, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
Heshbon, with her pasture land, Jazer, with her pasture land, —in all, four cities.
40 Duka-duka garuruwan da aka ba iyalan mutanen Merari, waɗanda su ne sauran Lawiyawa, garuruwa goma sha biyu ne.
All the cities for the sons of Merari, by their families, who remained of the families of the Levites, yea their lot was, twelve, cities.
41 Jimillar birane da wurarensu na kiwon da aka ba Lawiyawa daga cikin mallakar jama’ar Isra’ila guda arba’in da takwas ne.
All the cities of the Levites, in the midst of the possession of the sons of Israel, were forty-eight cities, with their pasture lands:
42 Dukan garuruwan nan kowannensu yana kewaye da wurin kiwo.
these cities passed, each severally, with its pasture lands round about it; thus, was it with all these cities.
43 Ubangiji kuwa ya ba Isra’ilawa dukan ƙasar da ya yi wa kakanninsu alkawari, suka kuwa mallake ta, suka zauna a cikinta.
So Yahweh gave unto Israel, all the land which he had sworn to give unto their fathers, —and they took possession thereof, and dwelt therein.
44 Ubangiji ya ba su hutawa a kowane gefe kamar yadda ya yi wa kakanninsu alkawari, ba ko ɗaya daga cikin abokan gābansu da ya iya cinsu da yaƙi.
And Yahweh gave them rest round about, according to all that he had sworn unto their fathers, —and there stood not a man before them, of all their enemies; all their enemies, did Yahweh deliver into their hand.
45 Ubangiji kuwa ya cika kowane alkawarin alherin da ya yi wa mutanen Isra’ila.
There failed not a thing, out of all the good things, whereof Yahweh had spoken unto the house of Israel, —the whole, came to pass.