< Yoshuwa 20 >

1 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
Ensuite le Seigneur parla à Josué, disant: Parle aux enfants d’Israël, et dis-leur:
2 “Ka gaya wa Isra’ilawa su keɓe waɗansu birane su zama biranen mafaka kamar yadda na umarce ku ta wurin Musa,
Séparez les villes des fugitifs dont je vous ai parlé par l’entremise de Moïse,
3 domin idan wani ya kashe wani bisa kuskure ba da niyyar yin kisankai ba, mutumin zai iya gudu zuwa can yă fake don kada a kashe shi.
Afin que s’y réfugie quiconque aura frappé une âme par mégarde, et qu’il puisse échapper à la colère du proche parent, qui est le vengeur du sang.
4 Lokacin da ya gudu zuwa ɗaya daga cikin biranen nan, sai yă tsaya a ƙofar birnin yă gaya wa dattawan wannan birni damuwarsa. Sa’an nan su karɓe shi su ba shi wurin zama a cikin birninsu.
Et lorsqu’il se sera réfugié dans une de ces villes, il se présentera devant la porte de la ville, et il dira aux anciens de cette ville, ce qui peut le prouver innocent: et ainsi ils le recevront et lui donneront un lieu pour habiter.
5 In mai neman yă kashe shi don ramako ya bi shi zuwa can, ba za su miƙa shi ba domin ba da niyya ya kashe wani ba, kuma ba fushi ne ya sa ya yi kisan ba.
Et lorsque le vengeur du sang le poursuivra, ils ne le livreront point entre ses mains, parce que c’est en l’ignorant qu’il a frappé son prochain, et que, deux ou trois jours auparavant, il n’était pas prouvé qu’il fût son ennemi.
6 Zai zauna a wannan birni har sai taron jama’a sun yi masa shari’a, kuma har sai lokacin da babban firist wanda yake aiki a lokacin ya mutu, sa’an nan zai iya koma garinsa na dā.”
Et il habitera dans cette ville, jusqu’à ce qu’il comparaisse en jugement pour rendre compte de son action, et que meure le grand prêtre qu’il y aura en ce temps-là; alors reviendra l’homicide, et il rentrera dans sa ville et dans sa maison, de laquelle il avait fui.
7 Saboda haka suka keɓe Kedesh a Galili a ƙasar kan tudu ta Naftali, Shekem a ƙasar kan tudu ta Efraim, da Kiriyat Arba (wato, Hebron) a ƙasar kan tudu ta Yahuda.
Ils désignèrent donc Cédés en Galilée, sur la montagne de Nephthali, Sichem, sur la montagne d’Ephraïm, et Cariatharbé, qui est la même qu’Hébron, sur la montagne de Juda.
8 A hayin Urdun, gabas da Yeriko, suka keɓe Bezer ta jeji a kan tudu a cikin yankin kabilar Ruben, Ramot cikin Gileyad a kabilar Gad, da Golan cikin Bashan a kabilar Manasse.
Et au-delà du Jourdain, contre la partie orientale, ils déterminèrent Bosor qui est située dans la plaine du désert, de la tribu de Ruben, Ramoth en Galaad, de la tribu de Gad, et Gaulon en Basan, de la tribu de Manassé.
9 In wani mutumin Isra’ila ko kuma wani baƙon da yake zama a cikinsu, ya yi kisankai cikin kuskure, zai iya gudu zuwa biranen da aka keɓe, ba za a bari mai neman ramako yă kashe shi kafin jama’a su yi masa shari’a ba.
Ces villes furent établies pour tous les enfants d’Israël, et pour les étrangers, qui habitaient parmi eux, afin que celui qui, par mégarde, aurait frappé une âme, s’y réfugiât, et ne mourût pas de la main du parent, désirant venger le sang versé, jusqu’à ce qu’il se présentât devant le peuple, pour défendre sa cause.

< Yoshuwa 20 >