< Yoshuwa 20 >
1 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
L’Eternel parla à Josué en ces termes:
2 “Ka gaya wa Isra’ilawa su keɓe waɗansu birane su zama biranen mafaka kamar yadda na umarce ku ta wurin Musa,
"Parle aux enfants d’Israël, et dis-leur: Désignez entre vous les villes de refuge dont je vous ai parlé par l’organe de Moïse,
3 domin idan wani ya kashe wani bisa kuskure ba da niyyar yin kisankai ba, mutumin zai iya gudu zuwa can yă fake don kada a kashe shi.
afin de recueillir, dans sa fuite, le meurtrier qui aurait frappé une personne par imprudence, involontairement, et de vous servir ainsi d’asile contre le vengeur du sang.
4 Lokacin da ya gudu zuwa ɗaya daga cikin biranen nan, sai yă tsaya a ƙofar birnin yă gaya wa dattawan wannan birni damuwarsa. Sa’an nan su karɓe shi su ba shi wurin zama a cikin birninsu.
Celui qui se réfugiera dans l’une de ces villes s’arrêtera à l’entrée de la porte de la ville, exposera son cas aux anciens de cette ville, qui l’y admettront dans leur sein et lui assigneront une demeure où il habitera parmi eux.
5 In mai neman yă kashe shi don ramako ya bi shi zuwa can, ba za su miƙa shi ba domin ba da niyya ya kashe wani ba, kuma ba fushi ne ya sa ya yi kisan ba.
Et si le vengeur du sang le poursuit, ils ne lui livreront pas le meurtrier, vu qu’il n’a point frappé son prochain avec intention ni par suite d’une haine antérieure.
6 Zai zauna a wannan birni har sai taron jama’a sun yi masa shari’a, kuma har sai lokacin da babban firist wanda yake aiki a lokacin ya mutu, sa’an nan zai iya koma garinsa na dā.”
Il restera dans cette ville jusqu’à ce qu’il comparaisse devant l’assemblée qui doit le juger, jusqu’à la mort du grand-prêtre en fonctions à cette époque: alors seulement, le meurtrier pourra rentrer chez lui, dans sa ville, dans cette ville d’où il se sera enfui."
7 Saboda haka suka keɓe Kedesh a Galili a ƙasar kan tudu ta Naftali, Shekem a ƙasar kan tudu ta Efraim, da Kiriyat Arba (wato, Hebron) a ƙasar kan tudu ta Yahuda.
On consacra à cet effet: Kédech en Galilée, dans la montagne de Nephtali; Sichem, dans la montagne d’Ephraïm; Kiryath-Arba ou Hébron, dans la montagne de Juda.
8 A hayin Urdun, gabas da Yeriko, suka keɓe Bezer ta jeji a kan tudu a cikin yankin kabilar Ruben, Ramot cikin Gileyad a kabilar Gad, da Golan cikin Bashan a kabilar Manasse.
Du côté oriental du Jourdain, vers Jéricho, on avait déjà choisi: Bécer, dans le désert, dans le plat pays, parmi les possessions de la tribu de Ruben; Ramoth, en Galaad, parmi celles de la tribu de Dan, et Golân, dans le Basan, parmi celles de Manassé.
9 In wani mutumin Isra’ila ko kuma wani baƙon da yake zama a cikinsu, ya yi kisankai cikin kuskure, zai iya gudu zuwa biranen da aka keɓe, ba za a bari mai neman ramako yă kashe shi kafin jama’a su yi masa shari’a ba.
Telles furent les villes déterminées pour tous les enfants d’Israël et pour l’étranger séjournant parmi eux, comme refuge de tout meurtrier par imprudence, afin qu’il ne pût périr sous la main du vengeur du sang avant d’avoir comparu devant le tribunal.