< Yoshuwa 20 >

1 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
And he spoke Yahweh to Joshua saying.
2 “Ka gaya wa Isra’ilawa su keɓe waɗansu birane su zama biranen mafaka kamar yadda na umarce ku ta wurin Musa,
Speak to [the] people of Israel saying assign for yourselves [the] cities of refuge which I spoke to you by [the] hand of Moses.
3 domin idan wani ya kashe wani bisa kuskure ba da niyyar yin kisankai ba, mutumin zai iya gudu zuwa can yă fake don kada a kashe shi.
To flee there towards a killer [who] strikes down a person by inadvertence with not knowledge and they will become for you a refuge from [the] avenger of blood.
4 Lokacin da ya gudu zuwa ɗaya daga cikin biranen nan, sai yă tsaya a ƙofar birnin yă gaya wa dattawan wannan birni damuwarsa. Sa’an nan su karɓe shi su ba shi wurin zama a cikin birninsu.
And he will flee to one - of the cities these and he will stand [the] entrance of [the] gate of the city and he will speak in [the] ears of ([the] elders of the city *LA(bh)*) that words his and they will gather him the city towards to themselves and they will give to him a place and he will dwell with them.
5 In mai neman yă kashe shi don ramako ya bi shi zuwa can, ba za su miƙa shi ba domin ba da niyya ya kashe wani ba, kuma ba fushi ne ya sa ya yi kisan ba.
And if he will pursue [the] avenger of blood after him and not they will deliver up the killer in hand his for with not knowledge he struck neighbor his and not [was] hating he him from yesterday [the] third day.
6 Zai zauna a wannan birni har sai taron jama’a sun yi masa shari’a, kuma har sai lokacin da babban firist wanda yake aiki a lokacin ya mutu, sa’an nan zai iya koma garinsa na dā.”
And he will dwell - in the city that until stands he before the congregation for judgment until [the] death of the priest great who he will be in the days those then - he will return the killer and he will go to own city his and to own house his to the city where he fled from there.
7 Saboda haka suka keɓe Kedesh a Galili a ƙasar kan tudu ta Naftali, Shekem a ƙasar kan tudu ta Efraim, da Kiriyat Arba (wato, Hebron) a ƙasar kan tudu ta Yahuda.
And they set apart Kedesh in Galilee in [the] hill country of Naphtali and Shechem in [the] hill country of Ephraim and Kiriath Arba that [is] Hebron in [the] hill country of Judah.
8 A hayin Urdun, gabas da Yeriko, suka keɓe Bezer ta jeji a kan tudu a cikin yankin kabilar Ruben, Ramot cikin Gileyad a kabilar Gad, da Golan cikin Bashan a kabilar Manasse.
And from [the] other side of [the] Jordan of Jericho east-ward they assigned Bezer in the wilderness in the plain from [the] tribe of Reuben and Ramoth in Gilead from [the] tribe of Gad and (Golan *Q(K)*) in Bashan from [the] tribe of Manasseh.
9 In wani mutumin Isra’ila ko kuma wani baƙon da yake zama a cikinsu, ya yi kisankai cikin kuskure, zai iya gudu zuwa biranen da aka keɓe, ba za a bari mai neman ramako yă kashe shi kafin jama’a su yi masa shari’a ba.
These they were [the] cities of appointing for all - [the] people of Israel and for the sojourner who sojourns in midst of them to flee there towards any [one who] strikes down a person by inadvertence and not he will die by [the] hand of [the] avenger of blood until stands he before the congregation.

< Yoshuwa 20 >