< Yoshuwa 20 >
1 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
Jahve reče Jošui:
2 “Ka gaya wa Isra’ilawa su keɓe waɗansu birane su zama biranen mafaka kamar yadda na umarce ku ta wurin Musa,
“Kaži sinovima Izraelovim i reci im: 'Odredite sebi gradove-utočišta za koje sam vam govorio preko Mojsija,
3 domin idan wani ya kashe wani bisa kuskure ba da niyyar yin kisankai ba, mutumin zai iya gudu zuwa can yă fake don kada a kashe shi.
da bi onamo mogao pobjeći ubojica koji nehotice ubije koga i da vam budu utočišta od krvnoga osvetnika.
4 Lokacin da ya gudu zuwa ɗaya daga cikin biranen nan, sai yă tsaya a ƙofar birnin yă gaya wa dattawan wannan birni damuwarsa. Sa’an nan su karɓe shi su ba shi wurin zama a cikin birninsu.
Ako ubojica utekne u koji od tih gradova, neka stane pred gradska vrata i neka starješinama toga grada iznese svoju stvar. Oni neka ga prime u svoj grad i odrede mu mjesto gdje će prebivati među njima.
5 In mai neman yă kashe shi don ramako ya bi shi zuwa can, ba za su miƙa shi ba domin ba da niyya ya kashe wani ba, kuma ba fushi ne ya sa ya yi kisan ba.
Ako ga krvni osvetnik progoni, ne smiju izručiti ubojicu u njegove ruke: tÓa nehotice je ubio svoga bližnjega, a ne iz mržnje.
6 Zai zauna a wannan birni har sai taron jama’a sun yi masa shari’a, kuma har sai lokacin da babban firist wanda yake aiki a lokacin ya mutu, sa’an nan zai iya koma garinsa na dā.”
Ubojica neka ostane u tom gradu sve dok ne stupi pred sud zajednice ili do smrti velikoga svećenika koji bude u ono vrijeme. Tada neka se ubojica vrati i neka ode u svoj grad i svome domu - u grad iz kojega je utekao.'”
7 Saboda haka suka keɓe Kedesh a Galili a ƙasar kan tudu ta Naftali, Shekem a ƙasar kan tudu ta Efraim, da Kiriyat Arba (wato, Hebron) a ƙasar kan tudu ta Yahuda.
I posvete Kedeš u Galileji, u Naftalijevoj gori; Šekem u Efrajimovoj gori; Kirjat-Arbu, to jest Hebron, u Judinoj gori.
8 A hayin Urdun, gabas da Yeriko, suka keɓe Bezer ta jeji a kan tudu a cikin yankin kabilar Ruben, Ramot cikin Gileyad a kabilar Gad, da Golan cikin Bashan a kabilar Manasse.
S druge strane Jordana, istočno od Jerihona, odrede Beser u pustinji, u ravnici plemena Rubenova, i Ramot u Gileadu od plemena Gadova, i Golan u Bašanu od plemena Manašeova.
9 In wani mutumin Isra’ila ko kuma wani baƙon da yake zama a cikinsu, ya yi kisankai cikin kuskure, zai iya gudu zuwa biranen da aka keɓe, ba za a bari mai neman ramako yă kashe shi kafin jama’a su yi masa shari’a ba.
To su bili gradovi određeni svim Izraelcima i došljacima koji borave među njima: ovamo je mogao uteći svaki koji nehotice drugoga ubije, a da sam ne pogine od osvetničke ruke dok ne izađe na sud, pred zajednicu.