< Yoshuwa 2 >

1 Sai Yoshuwa ɗan Nun ya aika’yan leƙen asiri guda biyu a ɓoye daga Shittim ya ce, “Ku je ku duba, ku ga yadda wurin yake, musamman Yeriko.” Sai suka je suka shiga gidan wata karuwa mai suna Rahab, suka sauka a can.
Josué, fils de Nun, envoya donc de Sétim deux hommes comme espions secrets, et il leur dit: Allez et considérez la terre et la ville de Jéricho. Et ceux-ci s’étant mis en chemin, entrèrent dans la maison d’une femme de mauvaise vie, du nom de Rahab, et se reposèrent chez elle.
2 Aka gaya wa sarkin Yeriko cewa, “Ji fa, waɗansu Isra’ilawa sun shigo nan da dare don su leƙi asirin ƙasar.”
Or, on l’annonça au roi de Jéricho, et on lui dit: Voilà que des hommes d’entre les enfants d’Israël sont entrés ici pendant la nuit pour explorer la terre.
3 Saboda haka sai sarki ya aika wannan saƙo zuwa ga Rahab, “Ki fito da mutanen da suka zo suka sauka a gidanki, gama sun zo su leƙi asirin ƙasar ne gaba ɗaya.”
Et le roi de Jéricho envoya chez Rahab, disant: Fais sortir les hommes qui sont venus chez toi, et qui sont entrés dans ta maison; car ce sont des espions, et ils sont venus considérer toute cette terre.
4 Amma matar ta ɓoye mutanen nan biyu. Ta ce, “I, mutanen sun zo wurina, amma ban san daga ina suka zo ba,
Mais Rahab, prenant ces hommes, les cacha, et dit: Je l’avoue, ils sont venus chez moi, mais je ne savais pas d’où ils étaient:
5 da yamma kuwa, kafin a rufe ƙofar gari sai mutanen suka tafi. Ban san hanyar da suka bi ba, ku yi sauri ku bi su. Mai yiwuwa ku same su.”
Et comme on fermait la porte de la ville pendant la nuit, ils sont sortis en même temps; je ne sais où ils sont allés: poursuivez-les promptement et vous les atteindrez.
6 (Amma ta kai su saman rufin ɗaki ta ɓoye su a ƙarƙashin karan rama da ta baza a rufin ɗaki.)
Mais elle, elle fit monter ces hommes sur la terrasse de sa maison, et elle les couvrit avec de la paille de Un, qui était là.
7 Sai mutanen garin suka kama hanyar Urdun don su nemi’yan leƙen asirin, daga fitar su sai aka rufe ƙofar garin.
Or, ceux qui avaient été envoyés les poursuivirent par la voie qui mène au gué du Jourdain; et, eux sortis, aussitôt la porte fut fermée.
8 Kafin’yan leƙen asirin su kwanta, sai ta tafi wurinsu a bisa rufin ɗakin
Ceux qui étaient cachés ne dormaient pas encore, et voilà que Rahab monta vers eux, et dit:
9 ta ce musu, “Na sani Ubangiji ya riga ya ba ku ƙasan nan, tsoronku kuma ya kama mu har zukatan mazaunan ƙasar duka sun narke saboda ku.
Je sais que le Seigneur vous a livré cette terre; car la terreur de votre nom nous a saisis, et tous les habitants de cette terre sont dans l’abattement.
10 Mun ji yadda Ubangiji ya busar da ruwan Jan Teku domin ku lokacin da kuka fito daga ƙasar Masar, da kuma abin da kuka yi wa Sihon da Og, sarakunan nan biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, waɗanda kuka hallaka su sarai.
Nous avons appris que le Seigneur a desséché les eaux de la mer rouge, à votre entrée, quand vous êtes sortis de l’Egypte, et ce que vous avez fait aux deux rois des Amorrhéens, qui étaient au-delà du Jourdain, Séhon et Og, que vous avez tués.
11 Da muka ji labarin, duk sai zuciyar kowa ta narke, kowa ya karaya saboda ku, gama Ubangiji Allahnku shi ne Allah na sama da ƙasa.
Et apprenant cela, nous avons craint fortement; notre cœur a défailli, et le courage nous a abandonnés à votre entrée; car le Seigneur votre Dieu est Dieu aussi dans le ciel en haut, et sur la terre en bas.
12 Yanzu ina roƙonku ku rantse mini da Ubangiji cewa za ku yi wa iyalina alheri kamar yadda na yi muku alheri. Ku ba ni ƙwaƙƙwarar shaida cewa
Maintenant donc, jurez-moi par le Seigneur, que, comme je vous ai fait miséricorde, ainsi vous ferez à la maison de mon père, et que vous me donnerez un signe certain,
13 za ku ceci rayukan mahaifina da mahaifiyata, da’yan’uwana maza da mata, da duk waɗanda suke nasu, za ku cece mu daga mutuwa.”
Que vous sauverez mon père et ma mère, mes frères et mes sœurs et tout ce qui est à eux, et que vous arracherez ainsi nos âmes à la mort.
14 Mutanen suka tabbatar mata suka ce, “Ranmu a bakin ranki! In ba ki faɗa wa kowa abin da ya kawo mu ba, za mu yi miki alheri da aminci lokacin da Ubangiji ya ba mu ƙasar.”
Et ils lui répondirent: Que notre âme soit pour vous jusqu’à la mort, si toutefois tu ne nous trahis point; et lorsque le Seigneur nous aura livré cette terre, nous accomplirons envers toi la miséricorde et la fidélité.
15 Sai ta zura igiya ta taga suka bi, domin gidan da take yana haɗe da katangar birnin.
Elle les fit donc descendre avec une corde par la fenêtre; car sa maison tenait au mur de la ville,
16 Ta ce musu, “Ku tafi cikin tuddan ƙasar don kada mutanen sarki su same ku. Ku ɓuya a can na kwana uku, har sai masu nemanku su komo, sa’an nan ku kama hanyarku.”
Et elle leur dit: Allez vers les montagnes, de peur qu’en revenant, ils ne vous rencontrent; et cachez-vous là trois jours, jusqu’à ce qu’ils reviennent; et alors vous irez par votre chemin.
17 Mutanen suka ce mata, “Rantsuwar da kika sa muka yi, ba za tă yi amfani ba
Ils lui répondirent: Nous ne manquerons pas à ce serment par lequel tu nous a adjurés,
18 sai in kin ɗaura jan ƙyalle a tagar da kika zura mu, kuma sai in kin kawo mahaifinki da mahaifiyarki, da’yan’uwanki, da dukan iyalinki cikin gidanki.
Si, nous entrant dans cette terre, ce cordon d’écarlate sert de signe, et si tu le lies à la fenêtre par laquelle tu nous a fait descendre, et que tu assembles dans ta maison ton père et ta mère, tes frères et toute ta parenté,
19 In wani ya fita kan hanya, alhakin jininsa yă kasance a kansa; ba ruwanmu. Amma in aka taɓa wani da yake cikin gidanki tare da ke, alhakin jininsa yana kanmu.
Celui qui sortira de la porte de ta maison, son sang sera sur sa tête, et nous, nous y serons étrangers; mais le sang de tous ceux qui seront avec toi dans ta maison retombera sur nous, si quelqu’un les touche.
20 In kika tone mana asiri, za mu karya alkawarin da kika sa muka yi.”
Que si tu veux nous trahir, et publier ces paroles, nous serons libres de ce serment par lequel tu nous as adjurés.
21 Ta ce, “Na yarda! Bari yă zama yadda kuka ce.” Sai ta sallame su suka tafi. Ta kuwa ɗaura jan ƙyalle a tagar.
Et elle leur répondit: Qu’il soit fait ainsi que vous avez dit. Et les laissant aller, elle suspendit le cordon d’écarlate à la fenêtre.
22 Sai suka tafi, suka shiga cikin tuddai, suka yi zamansu a can kwana uku har masu nemansu suka koma, gama masu nemansu suka yi ta nema ko’ina a hanyar, amma ba su sami kowa ba.
Et eux, cheminant, parvinrent aux montagnes, et demeurèrent là trois jours, jusqu’à ce que revinrent ceux qui les avaient poursuivis; car les cherchant dans tout le chemin, ils ne les trouvèrent pas.
23 Sa’an nan mutanen nan biyu,’yan leƙen asiri suka sauka daga tuddai suka haye kogi zuwa wurin Yoshuwa ɗan Nun, suka gaya masa duk abin da ya faru da su.
Et ceux-ci étant déjà entrés dans la ville, les espions s’en retournèrent, et descendirent de la montagne; puis, le Jourdain passé, ils vinrent vers Josué, fils de Nun, et lui racontèrent tout ce qui leur était arrivé,
24 Suka ce wa Yoshuwa, “Ba shakka Ubangiji ya ba mu ƙasan nan duka, tana hannunmu, mutane can duk sun narke da tsoro saboda mu.”
Et ils dirent: Le Seigneur a livré toute cette terre en nos mains et tous ses habitants sont consternés par la frayeur.

< Yoshuwa 2 >