< Yoshuwa 2 >
1 Sai Yoshuwa ɗan Nun ya aika’yan leƙen asiri guda biyu a ɓoye daga Shittim ya ce, “Ku je ku duba, ku ga yadda wurin yake, musamman Yeriko.” Sai suka je suka shiga gidan wata karuwa mai suna Rahab, suka sauka a can.
Then Joshua [chose] two men from [their camp at] Acacia. He told them, “Go [across the Jordan River] and secretly find out all that you can about the land on that side of the river, especially about Jericho [city].” So the two men crossed [the river and entered Jericho]. They entered the house of a prostitute, whose name was Rahab. They stayed in her house [that night].
2 Aka gaya wa sarkin Yeriko cewa, “Ji fa, waɗansu Isra’ilawa sun shigo nan da dare don su leƙi asirin ƙasar.”
But someone [saw them and] told the king of Jericho, “Some Israeli men have come here tonight to spy out the land!”
3 Saboda haka sai sarki ya aika wannan saƙo zuwa ga Rahab, “Ki fito da mutanen da suka zo suka sauka a gidanki, gama sun zo su leƙi asirin ƙasar ne gaba ɗaya.”
So the king sent some messengers to tell Rahab, “Bring out the men who came and entered your house, [so that we can kill them], because they have come [here] to (spy out/find out all they can about) this land!”
4 Amma matar ta ɓoye mutanen nan biyu. Ta ce, “I, mutanen sun zo wurina, amma ban san daga ina suka zo ba,
She told them that the two men had gone to her house. But she had hidden the two men there. So when the messengers came to her house, she told them, “Two men came here, but I did not know where they had come from.
5 da yamma kuwa, kafin a rufe ƙofar gari sai mutanen suka tafi. Ban san hanyar da suka bi ba, ku yi sauri ku bi su. Mai yiwuwa ku same su.”
At dusk, just before (guards closed the city gate/the city gates were closed), the two men left. I do not know where they went. So, go quickly and search for them! Perhaps you may catch them!”
6 (Amma ta kai su saman rufin ɗaki ta ɓoye su a ƙarƙashin karan rama da ta baza a rufin ɗaki.)
But [she was lying, ] she had taken the two men up to the [flat] roof of her house and had hidden them under the piles of flax that she had laid on the roof.
7 Sai mutanen garin suka kama hanyar Urdun don su nemi’yan leƙen asirin, daga fitar su sai aka rufe ƙofar garin.
The messengers went out of the city to search for the two men. Immediately, the guards shut the city gate. The messengers went along the road that leads down to the place where people can walk across the Jordan [River], [but they did not find the two men].
8 Kafin’yan leƙen asirin su kwanta, sai ta tafi wurinsu a bisa rufin ɗakin
Before the two men lay down [to sleep] that night, Rahab went up to the roof
9 ta ce musu, “Na sani Ubangiji ya riga ya ba ku ƙasan nan, tsoronku kuma ya kama mu har zukatan mazaunan ƙasar duka sun narke saboda ku.
and said to them, “We know that Yahweh [is about to] give this land to you Israelis, and as a result all the people living in this land are terrified because of you.
10 Mun ji yadda Ubangiji ya busar da ruwan Jan Teku domin ku lokacin da kuka fito daga ƙasar Masar, da kuma abin da kuka yi wa Sihon da Og, sarakunan nan biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, waɗanda kuka hallaka su sarai.
We have heard about how Yahweh dried up the water of the Red Sea for you to cross it when you left Egypt. And we have heard how you killed Sihon and Og, the two kings of the tribe of Amor who lived east of the Jordan [River]. You [Israelis] totally destroyed everyone [and everything in their kingdom].
11 Da muka ji labarin, duk sai zuciyar kowa ta narke, kowa ya karaya saboda ku, gama Ubangiji Allahnku shi ne Allah na sama da ƙasa.
When we heard about those things, we were very dismayed. We no longer have enough courage to fight against you, because we know that Yahweh, the God whom you [worship], is helping you. [And we know that] he rules everything in heaven and here on earth.
12 Yanzu ina roƙonku ku rantse mini da Ubangiji cewa za ku yi wa iyalina alheri kamar yadda na yi muku alheri. Ku ba ni ƙwaƙƙwarar shaida cewa
So now [I want you to] solemnly promise me, and ask Yahweh to punish you if you do not do what you promise. Solemnly promise me that you will act kindly to me and my family, because I have acted kindly to you.
13 za ku ceci rayukan mahaifina da mahaifiyata, da’yan’uwana maza da mata, da duk waɗanda suke nasu, za ku cece mu daga mutuwa.”
Do something to prove that you will (spare the lives of/not kill) my father and my mother, my brothers and sisters, and all of their families. Promise me that you [Israelis] will not kill us [when you destroy this city].”
14 Mutanen suka tabbatar mata suka ce, “Ranmu a bakin ranki! In ba ki faɗa wa kowa abin da ya kawo mu ba, za mu yi miki alheri da aminci lokacin da Ubangiji ya ba mu ƙasar.”
The two men replied, “We desire that God will cause us to die if we do not do as we say! If you do not tell others what we [are planning to] do, we will act kindly toward you all when Yahweh enables us to possess the land.”
15 Sai ta zura igiya ta taga suka bi, domin gidan da take yana haɗe da katangar birnin.
[One of] the outside walls of the house where Rahab lived was part of the wall [that was around] the city. So she fastened a rope outside the window [that was in that wall], by which the men could climb down the wall.
16 Ta ce musu, “Ku tafi cikin tuddan ƙasar don kada mutanen sarki su same ku. Ku ɓuya a can na kwana uku, har sai masu nemanku su komo, sa’an nan ku kama hanyarku.”
Then she said to them, “When you leave the city, go up into the hills so that the men who are searching for you will not find you. Hide in caves in the hills for three days, until the men who are searching for you return to the city. Then you can return safely to your camp.”
17 Mutanen suka ce mata, “Rantsuwar da kika sa muka yi, ba za tă yi amfani ba
The two men [gave her a red cord, and] said to her, “This is what you must do; if you do not do this, we will not be required to do what we have vowed to do.
18 sai in kin ɗaura jan ƙyalle a tagar da kika zura mu, kuma sai in kin kawo mahaifinki da mahaifiyarki, da’yan’uwanki, da dukan iyalinki cikin gidanki.
You must tie this red cord in the window that has the rope by which we will climb down. You must let the cord hang there. And you must bring your father and your mother and your brothers and all the others in your family inside the house. Then, when our army enters your land, we will see the cord, and we will not kill the people in your house.
19 In wani ya fita kan hanya, alhakin jininsa yă kasance a kansa; ba ruwanmu. Amma in aka taɓa wani da yake cikin gidanki tare da ke, alhakin jininsa yana kanmu.
If anyone in your family goes outside this house into the street, [our soldiers] will kill them, and we will not be guilty [MTY] for doing that. But if anyone who is in this house with you is injured, we will be guilty for causing that.
20 In kika tone mana asiri, za mu karya alkawarin da kika sa muka yi.”
But if you tell anyone what we [are planning to] do, we are not required to do what we have vowed to do.”
21 Ta ce, “Na yarda! Bari yă zama yadda kuka ce.” Sai ta sallame su suka tafi. Ta kuwa ɗaura jan ƙyalle a tagar.
Rahab said, “I agree to do what you say.” So they climbed down the rope and left. And she left the red cord tied in the window.
22 Sai suka tafi, suka shiga cikin tuddai, suka yi zamansu a can kwana uku har masu nemansu suka koma, gama masu nemansu suka yi ta nema ko’ina a hanyar, amma ba su sami kowa ba.
When the two men left the city, they went up into the hills. They stayed there for three days, while the men [who had been sent by the king] continued to search for them. They searched all along the road, but they did not find the two men. So they returned to the city.
23 Sa’an nan mutanen nan biyu,’yan leƙen asiri suka sauka daga tuddai suka haye kogi zuwa wurin Yoshuwa ɗan Nun, suka gaya masa duk abin da ya faru da su.
Then the two men started back toward their camp. They went down from the hills, went down to the river, crossed it at the place where people can walk across it, and returned to their camp. They told Joshua everything that had happened to them.
24 Suka ce wa Yoshuwa, “Ba shakka Ubangiji ya ba mu ƙasan nan duka, tana hannunmu, mutane can duk sun narke da tsoro saboda mu.”
They said to Joshua, “We are sure that Yahweh is going to enable us to possess everything that is in that land. The people there are terrified [IDM] because of us.”