< Yoshuwa 2 >

1 Sai Yoshuwa ɗan Nun ya aika’yan leƙen asiri guda biyu a ɓoye daga Shittim ya ce, “Ku je ku duba, ku ga yadda wurin yake, musamman Yeriko.” Sai suka je suka shiga gidan wata karuwa mai suna Rahab, suka sauka a can.
And so Joshua, the son of Nun, sent two men from Shittim to explore in secret. And he said to them, “Go and consider the land and the city of Jericho.” And while traveling, they entered into the house of a harlot woman named Rahab, and they rested with her.
2 Aka gaya wa sarkin Yeriko cewa, “Ji fa, waɗansu Isra’ilawa sun shigo nan da dare don su leƙi asirin ƙasar.”
And it was reported to the king of Jericho, and it was said: “Behold, men have entered to this place in the night, from the sons of Israel, so that they might explore the land.”
3 Saboda haka sai sarki ya aika wannan saƙo zuwa ga Rahab, “Ki fito da mutanen da suka zo suka sauka a gidanki, gama sun zo su leƙi asirin ƙasar ne gaba ɗaya.”
And the king of Jericho sent to Rahab, saying: “Bring out the men who came to you, and who entered into your house. For certainly they are spies, and they have arrived to consider the entire land.”
4 Amma matar ta ɓoye mutanen nan biyu. Ta ce, “I, mutanen sun zo wurina, amma ban san daga ina suka zo ba,
And the woman, taking the men, hid them. And she said: “I admit that they came to me, but I did not know where they were from.
5 da yamma kuwa, kafin a rufe ƙofar gari sai mutanen suka tafi. Ban san hanyar da suka bi ba, ku yi sauri ku bi su. Mai yiwuwa ku same su.”
And when the gate was closed, they went out together in the darkness. I do not know where they have gone. Pursue them quickly, and you will overtake them.”
6 (Amma ta kai su saman rufin ɗaki ta ɓoye su a ƙarƙashin karan rama da ta baza a rufin ɗaki.)
But she caused the men to ascend to the roof of her house, and she covered them with the stalks of flax that were there.
7 Sai mutanen garin suka kama hanyar Urdun don su nemi’yan leƙen asirin, daga fitar su sai aka rufe ƙofar garin.
But those who had been sent pursued after them along the way that leads to the ford of the Jordan. And as soon as they went out, the gate was closed.
8 Kafin’yan leƙen asirin su kwanta, sai ta tafi wurinsu a bisa rufin ɗakin
Those who were hiding had not yet fallen asleep, and behold, the woman went up to them, and she said:
9 ta ce musu, “Na sani Ubangiji ya riga ya ba ku ƙasan nan, tsoronku kuma ya kama mu har zukatan mazaunan ƙasar duka sun narke saboda ku.
“I know that the Lord has given this land to you. For the terror of you has fallen upon us, and all the inhabitants of the land have languished.
10 Mun ji yadda Ubangiji ya busar da ruwan Jan Teku domin ku lokacin da kuka fito daga ƙasar Masar, da kuma abin da kuka yi wa Sihon da Og, sarakunan nan biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, waɗanda kuka hallaka su sarai.
We have heard that the Lord dried up the water of the Red Sea upon your arrival, when you were departing from Egypt, and we heard of the things that you did to the two kings of the Amorites, who were beyond the Jordan, Sihon and Og, whom you put to death.
11 Da muka ji labarin, duk sai zuciyar kowa ta narke, kowa ya karaya saboda ku, gama Ubangiji Allahnku shi ne Allah na sama da ƙasa.
And upon hearing these things, we were very afraid, and our heart languished. Neither did there remain in us any spirit at your arrival. For the Lord your God is the very God in heaven above and on earth below.
12 Yanzu ina roƙonku ku rantse mini da Ubangiji cewa za ku yi wa iyalina alheri kamar yadda na yi muku alheri. Ku ba ni ƙwaƙƙwarar shaida cewa
Now, therefore, swear to me by the Lord that in the same way that I have acted with mercy toward you, so also shall you act toward the house of my father. And may you give me a true sign
13 za ku ceci rayukan mahaifina da mahaifiyata, da’yan’uwana maza da mata, da duk waɗanda suke nasu, za ku cece mu daga mutuwa.”
that you will save my father and mother, my brothers and sisters, and all that is theirs, and that you may rescue our souls from death.”
14 Mutanen suka tabbatar mata suka ce, “Ranmu a bakin ranki! In ba ki faɗa wa kowa abin da ya kawo mu ba, za mu yi miki alheri da aminci lokacin da Ubangiji ya ba mu ƙasar.”
They responded to her: “May our lives be yours unto death, if only you do not betray us. And when the Lord will have delivered the land to us, we will act toward you with mercy and truth.”
15 Sai ta zura igiya ta taga suka bi, domin gidan da take yana haɗe da katangar birnin.
Therefore, she sent them down from a window with a rope. For her house was joined to the wall.
16 Ta ce musu, “Ku tafi cikin tuddan ƙasar don kada mutanen sarki su same ku. Ku ɓuya a can na kwana uku, har sai masu nemanku su komo, sa’an nan ku kama hanyarku.”
And she said to them: “Climb up to the mountains; otherwise, they may meet you as they are returning. And lay hidden there for three days, until they return. And then you will go on your way.”
17 Mutanen suka ce mata, “Rantsuwar da kika sa muka yi, ba za tă yi amfani ba
And they said to her: “We shall be innocent of this oath, to which you have sworn us,
18 sai in kin ɗaura jan ƙyalle a tagar da kika zura mu, kuma sai in kin kawo mahaifinki da mahaifiyarki, da’yan’uwanki, da dukan iyalinki cikin gidanki.
if, when we enter into the land, this scarlet cord has been placed as a sign, and you have tied it at the window by which you let us down. And so, gather your father, and mother, and brothers, and all your family into your house.
19 In wani ya fita kan hanya, alhakin jininsa yă kasance a kansa; ba ruwanmu. Amma in aka taɓa wani da yake cikin gidanki tare da ke, alhakin jininsa yana kanmu.
Whoever will have exited from the door of your house, his blood will be on his own head, and we will be uninvolved. But the blood of all who will be with you in the house shall fall back upon our own head, if anyone touches them.
20 In kika tone mana asiri, za mu karya alkawarin da kika sa muka yi.”
But if you will have betrayed us, so that you spread this word in their midst, we will be free from this oath, to which you have sworn us.”
21 Ta ce, “Na yarda! Bari yă zama yadda kuka ce.” Sai ta sallame su suka tafi. Ta kuwa ɗaura jan ƙyalle a tagar.
And she responded, “Just as you have spoken, so let it be done.” And sending them to travel on, she hung the scarlet cord at the window.
22 Sai suka tafi, suka shiga cikin tuddai, suka yi zamansu a can kwana uku har masu nemansu suka koma, gama masu nemansu suka yi ta nema ko’ina a hanyar, amma ba su sami kowa ba.
And truly, walking on, they arrived at the mountains, and they stayed there for three days, until those who had been pursuing them returned. For having sought them along the entire way, they did not find them.
23 Sa’an nan mutanen nan biyu,’yan leƙen asiri suka sauka daga tuddai suka haye kogi zuwa wurin Yoshuwa ɗan Nun, suka gaya masa duk abin da ya faru da su.
And when they returned and entered the city, the explorers descended from the mountain. And crossing the Jordan, they went to Joshua, the son of Nun, and they reported to him all that had happened to them.
24 Suka ce wa Yoshuwa, “Ba shakka Ubangiji ya ba mu ƙasan nan duka, tana hannunmu, mutane can duk sun narke da tsoro saboda mu.”
And they said, “The Lord has delivered this entire land into our hands, and all its inhabitants have been struck down by fear.”

< Yoshuwa 2 >