< Yoshuwa 19 >
1 Ƙuri’a ta biyu ta fāɗa a kan kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu. Ƙasarsu ta gādo tana cikin yankin Yahuda.
POI la seconda sorte fu tratta per Simeone, per la tribù de' figliuoli di Simeone, secondo le lor nazioni; e la loro eredità fu per mezzo l'eredità dei figliuoli di Giuda.
2 Waɗannan su ne wuraren da suka gāda. Beyersheba (ko Sheba), Molada,
Ed ebbero nella loro eredità Beer-seba, e Seba e Molada; e Hasar-sual,
3 Hazar Shuwal, Bilha, Ezem,
e Bala, ed Esem; ed Eltolad, e Betul,
5 Ziklag, Bet-Markabot, Hazar-Susa,
e Bet-marcabot, e Hasar-susa;
6 Bet-Lebayot da Sharuhen, garuruwa goma sha uku ke nan da ƙauyukansu.
e Bet-lebaot, e Saruhem; tredici città, con le lor villate;
7 Akwai kuma Ayin, Rimmon, Eter da Ashan, garuruwa huɗu ke nan da ƙauyukansu,
[poi] Ain, e Rimmon, ed Eter, e Asan; quattro città, con le lor villate;
8 da kuma dukan ƙauyukan da suke kewaye da garuruwan nan har zuwa Rama na Negeb (wato, Ba’alat-Beyer). Wannan shi ne gādon kabilar Simeyon bisa ga iyalansu.
e tutte le villate ch'[erano] d'intorno a queste città, fino a Baalat-beer, [che è] Rama meridionale. Questa [fu] l'eredità della tribù de' figliuoli di Simeone, secondo le lor nazioni.
9 Daga cikin gādon mutanen Yahuda ne aka fitar da gādon kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu, domin rabon da kabilar Yahuda suka samu ya fi ƙarfin abin da suke bukata. Saboda haka kabilar gādon Simeyon yana cikin harabar Yahuda.
L'eredità de' figliuoli di Simeone [fu tolta] della parte de' figliuoli di Giuda; perciocchè la parte de' figliuoli di Giuda era troppo grande per loro; perciò i figliuoli di Simeone ebbero la loro eredità per mezzo l'eredità di essi.
10 Ƙuri’a ta uku ta fāɗa a kan Zebulun bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kai har Sarid.
POI la terza sorte fu tratta per li figliuoli di Zabulon, secondo le lor nazioni; e il confine della loro eredità fu infino a Sarid.
11 Ta nufi yamma zuwa Marala, ta taɓa Dabbeshet, ta wuce zuwa rafin da yake kusa da Yokneyam.
E il lor confine saliva verso il mare, fino a Mareala; e si scontrava in Dabbeset, e giungeva al torrente, che [è] dirincontro a Iocneam.
12 Daga Sarid, ta juya gabas zuwa harabar Kislot Tabor, ta kuma wuce zuwa Daberat har zuwa Yafiya.
E da Sarid si volgeva verso il Levante, a' confini di Chislot-tabor; e si stendeva verso Dabrat, e saliva in Iafia;
13 Sa’an nan ta ci gaba, ta yi gabas zuwa Gat-Hefer da Et Kazin; ta ɓulla a Rimmon, ta juya zuwa Neya.
e di là passava verso il Levante in Ghitta-hefer, [e] Itta-casin; poi, girando verso Nea, si stendeva fino a Rimmon;
14 A can ne iyakar ta kewaya zuwa Hannaton, sa’an nan ta ƙarasa a Kwarin Ifta El.
poi quel confine si volgeva dal Settentrione verso Hannaton, e faceva capo alla valle d'Iftael;
15 Zebulun ta ƙunshi garuruwa goma sha biyu da ƙauyukansu. Garuruwan sun haɗa da Kattat, Nahalal, Shimron, Idala da Betlehem.
e [comprendeva] Cattat, e Nahalal, e Simron, e Ideala, e Betlehem; dodici città, con le lor villate.
16 Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Zebulun ta samu, bisa ga iyalansu.
Questa [fu] l'eredità de' figliuoli di Zabulon, secondo le lor nazioni, [cioè: ] queste città, con le lor villate.
17 Ƙuri’a ta huɗu ta fāɗa a kan kabilar Issakar, bisa ga iyalansu.
LA quarta sorte fu tratta per Issacar, per li figliuoli d'Issacar, secondo le lor nazioni.
18 Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Yezireyel, Kessulot, Shunem,
E della lor contrada [fu] Izreel, e Chesullot, e Sunem;
e Hafaraim, e Sion, e Anaharat;
20 Rabbat, Kishiyon, Ebez,
e Rabbit, e Chision, ed Ebes;
21 Remet, En Gannim, En Hadda da Bet-Fazez.
e Remet, ed Ed-gannim, ed En-hadda, e Bet-passes.
22 Iyakar ta taɓa Tabor Shahazuma da Bet-Shemesh ta kuma ƙarasa a Urdun. Duka-duka garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
E il lor confine si scontrava in Tabor, e in Sahasim, e in Bet-semes; e faceva capo al Giordano: [e v'erano] sedici città, con le lor villate.
23 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Issakar ta samu, bisa ga iyalansu.
Questa [fu] l'eredità della tribù de' figliuoli d'Issacar, secondo le lor nazioni, [cioè: ] queste città, con le lor villate.
24 Ƙuri’a ta biyar ta fāɗa a kan kabilar Asher, bisa ga iyalansu.
POI la quinta sorte fu tratta per la tribù de' figliuoli di Aser, secondo le lor nazioni.
25 Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Helkat, Hali, Beten, Akshaf,
E della lor contrada fu Helcat, e Hali, e Beten,
26 Allammelek, Amad da Mishal. A arewanci kuma iyakar ta taɓa Karmel da Shihor Libnat.
e Acsaf; e Alammelec, e Amead, e Miseal; e il [lor confine] si scontrava in Carmel, verso il mare e in Sihor-libnat.
27 Sai ta yi gabas zuwa Bet-Dagon, ta taɓa Zebulun da kuma Kwarin Ifta El, ta wuce arewa zuwa Bet-Emek da Neyiyel, ta wuce Kabul a hagu,
Poi ritornava verso il Levante in Bet-dagon, e si scontrava in Zabulon, e nella valle d'Iftael, verso il Settentrione, e [in] Bet-emec, e [in] Neiel, e faceva capo a Cabul, dalla [man] sinistra;
28 ta kai Abdon, Rehob, Hammon da Kana, har zuwa Sidon Babba.
e [comprendeva] Ebron, e Rehob, e Hammon, e Cana, fino a Sidon, la gran [città].
29 Daga nan iyakar ta juya baya zuwa Rama, ta bi ta birnin nan mai katanga na Taya, ta juya ta nufi Hosa, sa’an nan ta ɓulla ta Bahar Rum cikin yankin Akzib,
Poi questo confine si volgeva verso Rama infino a Tiro, città forte; e di là si rivolgeva verso Hosa, e faceva capo al mare, dalla costa di Aczib;
30 Umma, Afek da Rehob. Garuruwa ashirin da biyu ke nan da ƙauyukansu.
e [comprendeva] Umma, e Afec, e Rehob; ventidue città, con le lor villate.
31 Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Asher ta samu bisa ga iyalansu.
Questa [fu] l'eredità della tribù de' figliuoli di Aser, secondo le lor nazioni, [cioè: ] queste città con le lor villate.
32 Ƙuri’a ta shida ta fāɗa a kan kabilar Naftali, bisa ga iyalansu.
LA sesta sorte fu tratta per li figliuoli di Neftali, secondo le lor nazioni.
33 Iyakarsu ta kama daga Helef, daga babban itacen Mamre nan da yake a Za’anannim, ta wuce Adami Nekeb da Yabneyel zuwa Lakkum, ta kuma ƙarasa a Urdun.
E il lor confine fu da Helef, [e] da Allon fino in Saanannim; e [da] Adaminecheb, e Iabneel, fino a Laccum; e faceva capo al Giordano.
34 Iyakar kuma ta juya yamma ta cikin Aznot-Tabo ta ɓulla a Hukkok. Ta taɓa Zebulun a kudu, Asher a yamma, da kuma Urdun a gabas.
E questo confine si volgeva dall'Occidente verso Asnot-tabor, e di là procedeva fino a Huccoc; e dal Mezzodì si scontrava in Zabulon, e dall'Occidente in Aser; e da Giuda il Giordano [era] dal Levante.
35 Biranen da suke da katanga su ne Ziddim, Zer, Hammat, Rakkat, Kinneret,
E le città forti [erano] Siddim, e Ser, e Hammat, e Raccat, e Chinneret; e Adama, e Rama, e Hasor;
37 Kedesh, Edireyi, En Hazor,
ed En-hasor; e Ireon, e Migda-el,
38 Yiron, Migdal El, Horem, Bet-Anat da Bet-Shemesh. Garuruwa goma sha tara ke nan da ƙauyukansu.
e Horem, e Bet-anat, e Bet-semes; diciannove città, con le lor villate.
39 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Naftali ta samu, bisa ga iyalansu.
Questa [fu] l'eredità della tribù de' figliuoli di Neftali, secondo le lor nazioni, [cioè: ] queste città, con le lor villate.
40 Ƙuri’a ta bakwai ta fāɗa a kan kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
LA settima sorte fu tratta per la tribù de' figliuoli di Dan, secondo le lor nazioni.
41 Ƙasarsu ta gādo ta haɗa da, Zora, Eshtawol, Ir Shemesh,
E della contrada della loro eredità fu Sorea, ed Estaol, e Irsemes;
42 Shalim, Aiyalon, Itla,
e Saalabbim, e Aialon, e Itla; ed Elon,
44 Elteke, Gibbeton, Ba’alat,
ed Elteche, e Ghibbeton, e Baalat;
45 Yehud, Bene-Berak, Gat-Rimmon,
e Iud, e Bene-berac, e Gat-rimmon;
46 Me Yarkon da Rakkon tare da sashen da yake fuskantar Yaffa.
e Meiarcon, e Raccon, con la contrada [che è] dirimpetto a Iafo.
47 (Amma ya zama wa mutanen kabilar Dan da wahala su mallaki ƙasar da aka ba su gādo, saboda haka sai suka nufi Leshem suka ci su da yaƙi, suka karkashe mutanen wurin, suka mallake ta, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato, Dan.)
Ora, a' figliuoli di Dan scaddero i confini troppo piccoli per loro; e però salirono, e combatterono Lesem, e la presero, e la misero a fil di spada, e la possedettero, e abitarono in essa, e le posero nome Dan, del nome di Dan, lor padre.
48 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
Questa [fu] l'eredità della tribù de' figliuoli di Dan, secondo le lor nazioni, [cioè: ] queste città, con le lor villate.
49 Sa’ad da aka gama raba gādon ƙasar bisa ga ƙuri’a. Sai Isra’ilawa suka ba Yoshuwa ɗan Nun nasa rabo a cikinsu,
ORA, dopo che i figliuoli d'Israele ebber finito di prender la possessione del paese, secondo i suoi confini, diedero eredità a Giosuè, figliuolo di Nun, per mezzo loro.
50 yadda Ubangiji ya umarta, suka ba shi garin da ya ce a ba shi, Timnat Serad a ƙasar tudu ta Efraim. Ya kuma gina garin ya zauna a can.
Secondo il comandamento del Signore, gli diedero la città ch'egli chiese, [cioè: ] Timnat-sera, nel monte di Efraim; ed egli riedificò la città, e abitò in essa.
51 Waɗannan su ne rabe-raben gādon da Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin kabilan iyalan Isra’ila suka rarraba ta hanyar jefa ƙuri’a a Shilo a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada. Da haka suka yi suka gama rarraba ƙasar.
Queste [sono] le eredità, le quali il Sacerdote Eleazaro, e Giosuè, figliuolo di Nun, e i capi delle [nazioni] paterne delle tribù de' figliuoli d'Israele, spartirono a sorte, in Silo, davanti al Signore, all'entrata del Tabernacolo della convenenza; e [così] finirono di spartire il paese.