< Yoshuwa 19 >

1 Ƙuri’a ta biyu ta fāɗa a kan kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu. Ƙasarsu ta gādo tana cikin yankin Yahuda.
ויצא הגורל השני לשמעון--למטה בני שמעון למשפחותם ויהי נחלתם בתוך נחלת בני יהודה
2 Waɗannan su ne wuraren da suka gāda. Beyersheba (ko Sheba), Molada,
ויהי להם בנחלתם--באר שבע ושבע ומולדה
3 Hazar Shuwal, Bilha, Ezem,
וחצר שועל ובלה ועצם
4 Eltolad, Betul, Horma,
ואלתולד ובתול וחרמה
5 Ziklag, Bet-Markabot, Hazar-Susa,
וצקלג ובית המרכבות וחצר סוסה
6 Bet-Lebayot da Sharuhen, garuruwa goma sha uku ke nan da ƙauyukansu.
ובית לבאות ושרוחן ערים שלש עשרה וחצריהן
7 Akwai kuma Ayin, Rimmon, Eter da Ashan, garuruwa huɗu ke nan da ƙauyukansu,
עין רמון ועתר ועשן ערים ארבע וחצריהן
8 da kuma dukan ƙauyukan da suke kewaye da garuruwan nan har zuwa Rama na Negeb (wato, Ba’alat-Beyer). Wannan shi ne gādon kabilar Simeyon bisa ga iyalansu.
וכל החצרים אשר סביבות הערים האלה עד בעלת באר ראמת נגב זאת נחלת מטה בני שמעון--למשפחתם
9 Daga cikin gādon mutanen Yahuda ne aka fitar da gādon kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu, domin rabon da kabilar Yahuda suka samu ya fi ƙarfin abin da suke bukata. Saboda haka kabilar gādon Simeyon yana cikin harabar Yahuda.
מחבל בני יהודה נחלת בני שמעון כי היה חלק בני יהודה רב מהם וינחלו בני שמעון בתוך נחלתם
10 Ƙuri’a ta uku ta fāɗa a kan Zebulun bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kai har Sarid.
ויעל הגורל השלישי לבני זבולן למשפחתם ויהי גבול נחלתם עד שריד
11 Ta nufi yamma zuwa Marala, ta taɓa Dabbeshet, ta wuce zuwa rafin da yake kusa da Yokneyam.
ועלה גבולם לימה ומרעלה ופגע בדבשת ופגע אל הנחל אשר על פני יקנעם
12 Daga Sarid, ta juya gabas zuwa harabar Kislot Tabor, ta kuma wuce zuwa Daberat har zuwa Yafiya.
ושב משריד קדמה מזרח השמש על גבול כסלת תבר ויצא אל הדברת ועלה יפיע
13 Sa’an nan ta ci gaba, ta yi gabas zuwa Gat-Hefer da Et Kazin; ta ɓulla a Rimmon, ta juya zuwa Neya.
ומשם עבר קדמה מזרחה גתה חפר עתה קצין ויצא רמון המתאר הנעה
14 A can ne iyakar ta kewaya zuwa Hannaton, sa’an nan ta ƙarasa a Kwarin Ifta El.
ונסב אתו הגבול מצפון חנתן והיו תצאתיו גי יפתח אל
15 Zebulun ta ƙunshi garuruwa goma sha biyu da ƙauyukansu. Garuruwan sun haɗa da Kattat, Nahalal, Shimron, Idala da Betlehem.
וקטת ונהלל ושמרון וידאלה ובית לחם ערים שתים עשרה וחצריהן
16 Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Zebulun ta samu, bisa ga iyalansu.
זאת נחלת בני זבולן למשפחותם--הערים האלה וחצריהן
17 Ƙuri’a ta huɗu ta fāɗa a kan kabilar Issakar, bisa ga iyalansu.
ליששכר--יצא הגורל הרביעי לבני יששכר למשפחותם
18 Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Yezireyel, Kessulot, Shunem,
ויהי גבולם--יזרעאלה והכסולת ושונם
19 Hafarayim, Anaharat,
וחפרים ושיאן ואנחרת
20 Rabbat, Kishiyon, Ebez,
והרבית וקשיון ואבץ
21 Remet, En Gannim, En Hadda da Bet-Fazez.
ורמת ועין גנים ועין חדה ובית פצץ
22 Iyakar ta taɓa Tabor Shahazuma da Bet-Shemesh ta kuma ƙarasa a Urdun. Duka-duka garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
ופגע הגבול בתבור ושחצומה (ושחצימה) ובית שמש והיו תצאות גבולם הירדן ערים שש עשרה וחצריהן
23 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Issakar ta samu, bisa ga iyalansu.
זאת נחלת מטה בני יששכר--למשפחתם הערים וחצריהן
24 Ƙuri’a ta biyar ta fāɗa a kan kabilar Asher, bisa ga iyalansu.
ויצא הגורל החמישי למטה בני אשר למשפחותם
25 Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Helkat, Hali, Beten, Akshaf,
ויהי גבולם--חלקת וחלי ובטן ואכשף
26 Allammelek, Amad da Mishal. A arewanci kuma iyakar ta taɓa Karmel da Shihor Libnat.
ואלמלך ועמעד ומשאל ופגע בכרמל הימה ובשיחור לבנת
27 Sai ta yi gabas zuwa Bet-Dagon, ta taɓa Zebulun da kuma Kwarin Ifta El, ta wuce arewa zuwa Bet-Emek da Neyiyel, ta wuce Kabul a hagu,
ושב מזרח השמש בית דגן ופגע בזבלון ובגי יפתח אל צפונה בית העמק ונעיאל ויצא אל כבול משמאל
28 ta kai Abdon, Rehob, Hammon da Kana, har zuwa Sidon Babba.
ועברן ורחב וחמון וקנה עד צידון רבה
29 Daga nan iyakar ta juya baya zuwa Rama, ta bi ta birnin nan mai katanga na Taya, ta juya ta nufi Hosa, sa’an nan ta ɓulla ta Bahar Rum cikin yankin Akzib,
ושב הגבול הרמה ועד עיר מבצר צר ושב הגבול חסה ויהיו (והיו) תצאתיו הימה מחבל אכזיבה
30 Umma, Afek da Rehob. Garuruwa ashirin da biyu ke nan da ƙauyukansu.
ועמה ואפק ורחב ערים עשרים ושתים וחצריהן
31 Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Asher ta samu bisa ga iyalansu.
זאת נחלת מטה בני אשר--למשפחתם הערים האלה וחצריהן
32 Ƙuri’a ta shida ta fāɗa a kan kabilar Naftali, bisa ga iyalansu.
לבני נפתלי יצא הגורל הששי--לבני נפתלי למשפחתם
33 Iyakarsu ta kama daga Helef, daga babban itacen Mamre nan da yake a Za’anannim, ta wuce Adami Nekeb da Yabneyel zuwa Lakkum, ta kuma ƙarasa a Urdun.
ויהי גבולם מחלף מאלון בצעננים ואדמי הנקב ויבנאל--עד לקום ויהי תצאתיו הירדן
34 Iyakar kuma ta juya yamma ta cikin Aznot-Tabo ta ɓulla a Hukkok. Ta taɓa Zebulun a kudu, Asher a yamma, da kuma Urdun a gabas.
ושב הגבול ימה אזנות תבור ויצא משם חוקקה ופגע בזבלון מנגב ובאשר פגע מים וביהודה הירדן מזרח השמש
35 Biranen da suke da katanga su ne Ziddim, Zer, Hammat, Rakkat, Kinneret,
וערי מבצר--הצדים צר וחמת רקת וכנרת
36 Adama, Rama, Hazor,
ואדמה והרמה וחצור
37 Kedesh, Edireyi, En Hazor,
וקדש ואדרעי ועין חצור
38 Yiron, Migdal El, Horem, Bet-Anat da Bet-Shemesh. Garuruwa goma sha tara ke nan da ƙauyukansu.
ויראון ומגדל אל חרם ובית ענת ובית שמש ערים תשע עשרה וחצריהן
39 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Naftali ta samu, bisa ga iyalansu.
זאת נחלת מטה בני נפתלי--למשפחתם הערים וחצריהן
40 Ƙuri’a ta bakwai ta fāɗa a kan kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
למטה בני דן למשפחתם יצא הגורל השביעי
41 Ƙasarsu ta gādo ta haɗa da, Zora, Eshtawol, Ir Shemesh,
ויהי גבול נחלתם--צרעה ואשתאול ועיר שמש
42 Shalim, Aiyalon, Itla,
ושעלבין ואילון ויתלה
43 Elon, Timna, Ekron,
ואילון ותמנתה ועקרון
44 Elteke, Gibbeton, Ba’alat,
ואלתקה וגבתון ובעלת
45 Yehud, Bene-Berak, Gat-Rimmon,
ויהד ובני ברק וגת רמון
46 Me Yarkon da Rakkon tare da sashen da yake fuskantar Yaffa.
ומי הירקון והרקון עם הגבול מול יפו
47 (Amma ya zama wa mutanen kabilar Dan da wahala su mallaki ƙasar da aka ba su gādo, saboda haka sai suka nufi Leshem suka ci su da yaƙi, suka karkashe mutanen wurin, suka mallake ta, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato, Dan.)
ויצא גבול בני דן מהם ויעלו בני דן וילחמו עם לשם וילכדו אותה ויכו אותה לפי חרב וירשו אותה וישבו בה ויקראו ללשם דן כשם דן אביהם
48 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
זאת נחלת מטה בני דן--למשפחתם הערים האלה וחצריהן
49 Sa’ad da aka gama raba gādon ƙasar bisa ga ƙuri’a. Sai Isra’ilawa suka ba Yoshuwa ɗan Nun nasa rabo a cikinsu,
ויכלו לנחל את הארץ לגבולתיה ויתנו בני ישראל נחלה ליהושע בן נון בתוכם
50 yadda Ubangiji ya umarta, suka ba shi garin da ya ce a ba shi, Timnat Serad a ƙasar tudu ta Efraim. Ya kuma gina garin ya zauna a can.
על פי יהוה נתנו לו את העיר אשר שאל--את תמנת סרח בהר אפרים ויבנה את העיר וישב בה
51 Waɗannan su ne rabe-raben gādon da Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin kabilan iyalan Isra’ila suka rarraba ta hanyar jefa ƙuri’a a Shilo a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada. Da haka suka yi suka gama rarraba ƙasar.
אלה הנחלת אשר נחלו אלעזר הכהן ויהושע בן נון וראשי האבות למטות בני ישראל בגורל בשלה לפני יהוה--פתח אהל מועד ויכלו מחלק את הארץ

< Yoshuwa 19 >