< Yoshuwa 19 >

1 Ƙuri’a ta biyu ta fāɗa a kan kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu. Ƙasarsu ta gādo tana cikin yankin Yahuda.
Le deuxième sort sortit pour les enfants de Siméon, selon leur parenté, et l’héritage fut
2 Waɗannan su ne wuraren da suka gāda. Beyersheba (ko Sheba), Molada,
Pour eux au milieu de la possession des fils de Juda: Bersabée, Sabée, Molada;
3 Hazar Shuwal, Bilha, Ezem,
Hasersual, Bala, Asem,
4 Eltolad, Betul, Horma,
Eltholad, Bétul, Harma,
5 Ziklag, Bet-Markabot, Hazar-Susa,
Sicéleg, Bethmarchaboth, Hasersusa,
6 Bet-Lebayot da Sharuhen, garuruwa goma sha uku ke nan da ƙauyukansu.
Béthlébaoth et Sarohen: treize villes et leurs villages;
7 Akwai kuma Ayin, Rimmon, Eter da Ashan, garuruwa huɗu ke nan da ƙauyukansu,
Aïn, Remmon, Athar et Azan: quatre villes et leurs villages;
8 da kuma dukan ƙauyukan da suke kewaye da garuruwan nan har zuwa Rama na Negeb (wato, Ba’alat-Beyer). Wannan shi ne gādon kabilar Simeyon bisa ga iyalansu.
Toutes les bourgades autour de ces villes jusqu’à Baalath, Béer, Ramath contre la partie australe. Tel est l’héritage des enfants de Siméon, selon leur parenté,
9 Daga cikin gādon mutanen Yahuda ne aka fitar da gādon kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu, domin rabon da kabilar Yahuda suka samu ya fi ƙarfin abin da suke bukata. Saboda haka kabilar gādon Simeyon yana cikin harabar Yahuda.
Dans la possession et le partage des enfants de Juda, parce qu’il était trop grand pour eux: et c’est pour cela que les enfants de Siméon eurent leur possession au milieu de leur héritage.
10 Ƙuri’a ta uku ta fāɗa a kan Zebulun bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kai har Sarid.
Le troisième sort échut aux enfants de Zabulon, selon leur parenté; et la frontière de leur possession s’étendait jusqu’à Sarid;
11 Ta nufi yamma zuwa Marala, ta taɓa Dabbeshet, ta wuce zuwa rafin da yake kusa da Yokneyam.
Elle monte de la mer et de Mérala, et elle parvient à Debbaseth, jusqu’au torrent qui est contre Jéconam;
12 Daga Sarid, ta juya gabas zuwa harabar Kislot Tabor, ta kuma wuce zuwa Daberat har zuwa Yafiya.
Elle retourne de Sared contre l’orient, aux confins de Césélethabor, s’avance près Dabéreth et monte contre Japhié;
13 Sa’an nan ta ci gaba, ta yi gabas zuwa Gat-Hefer da Et Kazin; ta ɓulla a Rimmon, ta juya zuwa Neya.
De là, elle passe jusqu’à la partie orientale de Géthhépher et Thacasin, et s’avance vers Remmon, Amthar et Noa.
14 A can ne iyakar ta kewaya zuwa Hannaton, sa’an nan ta ƙarasa a Kwarin Ifta El.
De plus, elle fait, à l’aquilon, le tour d’Hanaton, et elle est terminée par la vallée de Jephtahel,
15 Zebulun ta ƙunshi garuruwa goma sha biyu da ƙauyukansu. Garuruwan sun haɗa da Kattat, Nahalal, Shimron, Idala da Betlehem.
Par Cathed, Naalol, Séméron, Jédala et Bethléem; douze villes et leurs villages.
16 Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Zebulun ta samu, bisa ga iyalansu.
C’est là l’héritage de la tribu des enfants de Zabulon, selon leur parenté; ce sont leurs villes et leurs bourgades.
17 Ƙuri’a ta huɗu ta fāɗa a kan kabilar Issakar, bisa ga iyalansu.
C’est pour Issachar, selon sa parenté, que sortit le quatrième sort;
18 Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Yezireyel, Kessulot, Shunem,
Et son héritage fut Jezraël, Casaloth, Sunem,
19 Hafarayim, Anaharat,
Hapharaïm, Séhon, Anaharat,
20 Rabbat, Kishiyon, Ebez,
Rabboth, Césion, Abès.
21 Remet, En Gannim, En Hadda da Bet-Fazez.
Rameth, Engannim, Enhadda, et Bethphésès;
22 Iyakar ta taɓa Tabor Shahazuma da Bet-Shemesh ta kuma ƙarasa a Urdun. Duka-duka garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
Et sa frontière parvient jusqu’à Thabor, Séhésima et Bethsamès; et se termine au Jourdain: seize villes et leurs villages.
23 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Issakar ta samu, bisa ga iyalansu.
Telle est la possession des enfants d’Issachar, selon leur parenté; telles sont les villes et leurs bourgades.
24 Ƙuri’a ta biyar ta fāɗa a kan kabilar Asher, bisa ga iyalansu.
Le cinquième sort échut aux enfants d’Aser, selon leur parenté;
25 Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Helkat, Hali, Beten, Akshaf,
Et leur frontière fut Halcath, Chali, Béthen, Axaph,
26 Allammelek, Amad da Mishal. A arewanci kuma iyakar ta taɓa Karmel da Shihor Libnat.
Elmélech, Amaad et Messal; et elle parvient jusqu’au Carmel de la mer, jusqu’à Sihor et Labanath;
27 Sai ta yi gabas zuwa Bet-Dagon, ta taɓa Zebulun da kuma Kwarin Ifta El, ta wuce arewa zuwa Bet-Emek da Neyiyel, ta wuce Kabul a hagu,
Et elle retourne contre l’orient à Bethdagon; elle passe jusqu’à Zabulon et à la vallée de Jephthael, contre l’aquilon, jusqu’à Bethémec et Néhiel. Elle s’avance, vers la gauche, vers Cabul,
28 ta kai Abdon, Rehob, Hammon da Kana, har zuwa Sidon Babba.
Abran, Rohob, Hamon et Cana, jusqu’à Sidon la grande;
29 Daga nan iyakar ta juya baya zuwa Rama, ta bi ta birnin nan mai katanga na Taya, ta juya ta nufi Hosa, sa’an nan ta ɓulla ta Bahar Rum cikin yankin Akzib,
Puis elle retourne vers Horma, jusqu’à la ville très fortifiée de Tyr, et jusqu’à Hosa; et elle est terminée, à la mer, au territoire d’Achziba,
30 Umma, Afek da Rehob. Garuruwa ashirin da biyu ke nan da ƙauyukansu.
Amma, Aphec et Rohob: vingt-deux cités et leurs villages.
31 Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Asher ta samu bisa ga iyalansu.
Telle est la possession des enfants d’Aser, selon leur parenté; telles sont les villes et leurs bourgades.
32 Ƙuri’a ta shida ta fāɗa a kan kabilar Naftali, bisa ga iyalansu.
Aux enfants de Nephthali échut le sixième sort, selon leurs familles;
33 Iyakarsu ta kama daga Helef, daga babban itacen Mamre nan da yake a Za’anannim, ta wuce Adami Nekeb da Yabneyel zuwa Lakkum, ta kuma ƙarasa a Urdun.
Et leur frontière commence à Héleph et Elon, va à Saananim et à Adami, qui est la même que Néceb, et à Jebnaël jusqu’à Lécum, et s’avance jusqu’au Jourdain;
34 Iyakar kuma ta juya yamma ta cikin Aznot-Tabo ta ɓulla a Hukkok. Ta taɓa Zebulun a kudu, Asher a yamma, da kuma Urdun a gabas.
Et la frontière retourne, contre l’occident, à Azanoth-Thabor, et de là s’avance vers Hucuca, et passe à Zabulon, contre le midi, à Aser, contre l’occident, et à Juda, vers le Jourdain, contre le levant.
35 Biranen da suke da katanga su ne Ziddim, Zer, Hammat, Rakkat, Kinneret,
Les villes très fortifiées sont Assédim, Ser, Emath, Reccath, Cénéreth,
36 Adama, Rama, Hazor,
Edéma, Arama, Asor,
37 Kedesh, Edireyi, En Hazor,
Cédés, Edraï, Enhasor,
38 Yiron, Migdal El, Horem, Bet-Anat da Bet-Shemesh. Garuruwa goma sha tara ke nan da ƙauyukansu.
Jéron, Magdalel, Horem, Bethanath et Bethsamès: dix-neuf villes et leurs villages.
39 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Naftali ta samu, bisa ga iyalansu.
Telle est la possession de la tribu des enfants de Nephthali, selon leur parenté; telles sont les villes et leurs bourgades.
40 Ƙuri’a ta bakwai ta fāɗa a kan kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
C’est pour la tribu des enfants de Dan, selon leurs familles, que sortit le septième sort;
41 Ƙasarsu ta gādo ta haɗa da, Zora, Eshtawol, Ir Shemesh,
Et la frontière de sa possession fut Saraa, Esthaol et Hirsémès, c’est-à-dire, ville du soleil,
42 Shalim, Aiyalon, Itla,
Sélébin, Aïalon, Jéthéla,
43 Elon, Timna, Ekron,
Elon, Themna et Acron,
44 Elteke, Gibbeton, Ba’alat,
Elthécé, Gébbéhon et Balaath,
45 Yehud, Bene-Berak, Gat-Rimmon,
Jud, Bané, Barach, Gethremmon,
46 Me Yarkon da Rakkon tare da sashen da yake fuskantar Yaffa.
Méjarchon, et Arecon, avec la frontière qui regarde Joppé,
47 (Amma ya zama wa mutanen kabilar Dan da wahala su mallaki ƙasar da aka ba su gādo, saboda haka sai suka nufi Leshem suka ci su da yaƙi, suka karkashe mutanen wurin, suka mallake ta, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato, Dan.)
Et elle est terminée par cette limite. Mais les enfants de Dan montèrent et combattirent contre Lésem, la prirent, la frappèrent du tranchant du glaive, en prirent possession et habitèrent en elle, lui donnant le nom de Lésem-Dan, du nom de Dan leur père.
48 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
Telle est la possession de la tribu des enfants de Dan, selon leur parenté; telles sont les villes et leurs bourgades.
49 Sa’ad da aka gama raba gādon ƙasar bisa ga ƙuri’a. Sai Isra’ilawa suka ba Yoshuwa ɗan Nun nasa rabo a cikinsu,
Or, lorsqu’il eut achevé de partager par le sort la terre à chacun, selon sa tribu, les enfants d’Israël donnèrent en possession à Josué, fils de Nun, au milieu d’eux,
50 yadda Ubangiji ya umarta, suka ba shi garin da ya ce a ba shi, Timnat Serad a ƙasar tudu ta Efraim. Ya kuma gina garin ya zauna a can.
Selon le commandement du Seigneur, la ville qu’il avait demandée, Thamnath-Saraa, sur la montagne d’Ephraïm, et il bâtit la ville et il y habita.
51 Waɗannan su ne rabe-raben gādon da Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin kabilan iyalan Isra’ila suka rarraba ta hanyar jefa ƙuri’a a Shilo a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada. Da haka suka yi suka gama rarraba ƙasar.
Telles sont les possessions que partagèrent au sort Eléazar, le prêtre, Josué, fils de Nun, et les princes des familles et des tribus des enfants d’Israël, à Silo, devant le Seigneur, à la porte du tabernacle de témoignage. C’est ainsi qu’ils partagèrent la terre.

< Yoshuwa 19 >