< Yoshuwa 19 >
1 Ƙuri’a ta biyu ta fāɗa a kan kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu. Ƙasarsu ta gādo tana cikin yankin Yahuda.
The second casting of lots fell to Simeon, clan by clan. Their inheritance was in the middle of the inheritance that belonged to the tribe of Judah.
2 Waɗannan su ne wuraren da suka gāda. Beyersheba (ko Sheba), Molada,
They had for their inheritance Beersheba, Sheba, Moladah,
3 Hazar Shuwal, Bilha, Ezem,
Hazar Shual, Balah, Ezem,
Eltolad, Bethul, and Hormah.
5 Ziklag, Bet-Markabot, Hazar-Susa,
Simeon also had Ziklag, Beth Markaboth, Hazar Susah,
6 Bet-Lebayot da Sharuhen, garuruwa goma sha uku ke nan da ƙauyukansu.
Beth Lebaoth, and Sharuhen. These were thirteen cities, including their villages.
7 Akwai kuma Ayin, Rimmon, Eter da Ashan, garuruwa huɗu ke nan da ƙauyukansu,
Simeon also had Ain, Rimmon, Ether, and Ashan. These were four cities, including their villages.
8 da kuma dukan ƙauyukan da suke kewaye da garuruwan nan har zuwa Rama na Negeb (wato, Ba’alat-Beyer). Wannan shi ne gādon kabilar Simeyon bisa ga iyalansu.
These were together, including their the villages around these cities as far as Baalath Beer (the same as Ramah in the Negev). This was the inheritance of the tribe of Simeon, clan by clan.
9 Daga cikin gādon mutanen Yahuda ne aka fitar da gādon kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu, domin rabon da kabilar Yahuda suka samu ya fi ƙarfin abin da suke bukata. Saboda haka kabilar gādon Simeyon yana cikin harabar Yahuda.
The inheritance of the tribe of Simeon formed part of the territory of the tribe of Judah. Because the portion of land assigned to the tribe of Judah was too large for them, the tribe of Simeon received their inheritance out of the middle of their portion.
10 Ƙuri’a ta uku ta fāɗa a kan Zebulun bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kai har Sarid.
The third casting of lots fell to the tribe of Zebulun, clan by clan. The border of their inheritance began at Sarid.
11 Ta nufi yamma zuwa Marala, ta taɓa Dabbeshet, ta wuce zuwa rafin da yake kusa da Yokneyam.
Their border went up westward toward Maralah and touched Dabbesheth; then it extended to the brook that was opposite Jokneam.
12 Daga Sarid, ta juya gabas zuwa harabar Kislot Tabor, ta kuma wuce zuwa Daberat har zuwa Yafiya.
From Sarid the border turned eastward toward the east and went to the border of Kisloth Tabor. From there it went to Daberath and then up to Japhia.
13 Sa’an nan ta ci gaba, ta yi gabas zuwa Gat-Hefer da Et Kazin; ta ɓulla a Rimmon, ta juya zuwa Neya.
From there it passed on eastward to Gath Hepher, and then to Eth Kazin; next it went to Rimmon and turned toward Neah.
14 A can ne iyakar ta kewaya zuwa Hannaton, sa’an nan ta ƙarasa a Kwarin Ifta El.
The border made a turn to the north to Hannathon and ended at the Valley of Iphtah El.
15 Zebulun ta ƙunshi garuruwa goma sha biyu da ƙauyukansu. Garuruwan sun haɗa da Kattat, Nahalal, Shimron, Idala da Betlehem.
This region included the cities of Kattath, Nahalal, Shimron, Idalah, and Bethlehem. There were twelve cities, including their villages.
16 Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Zebulun ta samu, bisa ga iyalansu.
This was the inheritance of the tribe of Zebulun, clan by clan, including these cities, including their villages.
17 Ƙuri’a ta huɗu ta fāɗa a kan kabilar Issakar, bisa ga iyalansu.
The fourth casting of lots fell to Issachar, clan by clan.
18 Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Yezireyel, Kessulot, Shunem,
Their territory included Jezreel, Chesulloth, Shunem,
Hapharaim, Shion, and Anaharath.
20 Rabbat, Kishiyon, Ebez,
It also included Rabbith, Kishion, Ebez,
21 Remet, En Gannim, En Hadda da Bet-Fazez.
Remeth, En Gannim, En Haddah, and Beth Pazzez.
22 Iyakar ta taɓa Tabor Shahazuma da Bet-Shemesh ta kuma ƙarasa a Urdun. Duka-duka garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
Their border also touched Tabor, Shahazumah, and Beth Shemesh, and ended at the Jordan. There were sixteen cities, including their villages.
23 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Issakar ta samu, bisa ga iyalansu.
This was the inheritance of the tribe of Issachar, according to their clans—the cities, including their villages.
24 Ƙuri’a ta biyar ta fāɗa a kan kabilar Asher, bisa ga iyalansu.
The fifth casting of lots fell to the tribe of Asher, clan by clan.
25 Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Helkat, Hali, Beten, Akshaf,
Their territory included Helkath, Hali, Beten, Akshaph,
26 Allammelek, Amad da Mishal. A arewanci kuma iyakar ta taɓa Karmel da Shihor Libnat.
Allammelek, Amad, and Mishall. On the west the boundary extended to Carmel and Shihor Libnath.
27 Sai ta yi gabas zuwa Bet-Dagon, ta taɓa Zebulun da kuma Kwarin Ifta El, ta wuce arewa zuwa Bet-Emek da Neyiyel, ta wuce Kabul a hagu,
Then it turned eastward to Beth Dagon and went as far as Zebulun, and then to the Valley of Iphtah El, northward to Beth Emek and Neiel. Then it continued on to Kabul toward the north.
28 ta kai Abdon, Rehob, Hammon da Kana, har zuwa Sidon Babba.
It then went on to Abdon, Rehob, Hammon, and Kanah, as far as Greater Sidon.
29 Daga nan iyakar ta juya baya zuwa Rama, ta bi ta birnin nan mai katanga na Taya, ta juya ta nufi Hosa, sa’an nan ta ɓulla ta Bahar Rum cikin yankin Akzib,
The border turned back to Ramah, and then to the fortified city of Tyre. Then the border turned to Hosah and ended at the sea, in the region of Akzib,
30 Umma, Afek da Rehob. Garuruwa ashirin da biyu ke nan da ƙauyukansu.
Ummah, Aphek, and Rehob. There were twenty-two cities, including their villages.
31 Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Asher ta samu bisa ga iyalansu.
This was the inheritance of the tribe of Asher, clan by clan—the cities, including their villages.
32 Ƙuri’a ta shida ta fāɗa a kan kabilar Naftali, bisa ga iyalansu.
The sixth casting of lots fell to tribe of Naphtali, clan by clan.
33 Iyakarsu ta kama daga Helef, daga babban itacen Mamre nan da yake a Za’anannim, ta wuce Adami Nekeb da Yabneyel zuwa Lakkum, ta kuma ƙarasa a Urdun.
Their border ran from Heleph, from the oak at Zaanannim, on to Adami Nekeb and Jabneel, as far as Lakkum; it ended at the Jordan.
34 Iyakar kuma ta juya yamma ta cikin Aznot-Tabo ta ɓulla a Hukkok. Ta taɓa Zebulun a kudu, Asher a yamma, da kuma Urdun a gabas.
The border turned westward to Aznoth Tabor and went on to Hukkok; it touched Zebulun on the south, and reached to Asher on the west and Judah on the east at the Jordan River.
35 Biranen da suke da katanga su ne Ziddim, Zer, Hammat, Rakkat, Kinneret,
The fortified cities were Ziddim, Zer, Hammath, Rakkath, Kinnereth,
37 Kedesh, Edireyi, En Hazor,
Kedesh, Edrei, and En Hazor.
38 Yiron, Migdal El, Horem, Bet-Anat da Bet-Shemesh. Garuruwa goma sha tara ke nan da ƙauyukansu.
There were also Yiron, Migdal El, Horem, Beth Anath, and Beth Shemesh. There were nineteen cities, including their villages.
39 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Naftali ta samu, bisa ga iyalansu.
This was the inheritance of the tribe of Naphtali, clan by clan—the cities, including their villages.
40 Ƙuri’a ta bakwai ta fāɗa a kan kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
The seventh casting of lots fell to the tribe of Dan, clan by clan.
41 Ƙasarsu ta gādo ta haɗa da, Zora, Eshtawol, Ir Shemesh,
The territory of its inheritance included Zorah, Eshtaol, Ir Shemesh,
42 Shalim, Aiyalon, Itla,
Shaalabbin, Aijalon, and Ithlah.
It also included Elon, Timnah, Ekron,
44 Elteke, Gibbeton, Ba’alat,
Eltekeh, Gibbethon, Baalath,
45 Yehud, Bene-Berak, Gat-Rimmon,
Jehud, Bene Berak, Gath Rimmon,
46 Me Yarkon da Rakkon tare da sashen da yake fuskantar Yaffa.
Me Jarkon, and Rakkon along with the territory across from Joppa.
47 (Amma ya zama wa mutanen kabilar Dan da wahala su mallaki ƙasar da aka ba su gādo, saboda haka sai suka nufi Leshem suka ci su da yaƙi, suka karkashe mutanen wurin, suka mallake ta, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato, Dan.)
When the territory of the tribe of Dan was lost to them, Dan attacked Leshem, fought against it, capturing it and striking it with the sword; taking possession of it and settled in it. They renamed Leshem, calling it Dan after their ancestor.
48 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
This was the inheritance of the tribe of Dan, clan by clan—the cities, including their villages.
49 Sa’ad da aka gama raba gādon ƙasar bisa ga ƙuri’a. Sai Isra’ilawa suka ba Yoshuwa ɗan Nun nasa rabo a cikinsu,
When they finished the allocation of the land as an inheritance, the people of Israel gave an inheritance among themselves to Joshua son of Nun.
50 yadda Ubangiji ya umarta, suka ba shi garin da ya ce a ba shi, Timnat Serad a ƙasar tudu ta Efraim. Ya kuma gina garin ya zauna a can.
By the command of Yahweh they gave him the city for which he asked, Timnath Serah in the hill country of Ephraim. He rebuilt the city and lived there.
51 Waɗannan su ne rabe-raben gādon da Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin kabilan iyalan Isra’ila suka rarraba ta hanyar jefa ƙuri’a a Shilo a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada. Da haka suka yi suka gama rarraba ƙasar.
These are the inheritances that Eleazar the priest, Joshua son of Nun, and the leaders of the tribes of the people of Israel assigned by lot at Shiloh, before Yahweh, at the entrance of the tent of meeting. So they finished assigning the land.