< Yoshuwa 19 >

1 Ƙuri’a ta biyu ta fāɗa a kan kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu. Ƙasarsu ta gādo tana cikin yankin Yahuda.
The second lot came out for Simeon, even for the tribe of the descendants of Simeon according to their families. Their inheritance was in the midst of the inheritance of the descendants of Judah.
2 Waɗannan su ne wuraren da suka gāda. Beyersheba (ko Sheba), Molada,
And they had for their inheritance Beersheba, and Moladah,
3 Hazar Shuwal, Bilha, Ezem,
and Hazar Shual, and Balah, and Ezem,
4 Eltolad, Betul, Horma,
and Eltolad, and Bethul, and Hormah,
5 Ziklag, Bet-Markabot, Hazar-Susa,
and Ziklag, and Beth Marcaboth, and Hazar Susah,
6 Bet-Lebayot da Sharuhen, garuruwa goma sha uku ke nan da ƙauyukansu.
and Beth Lebaoth, and Sharuhen; thirteen cities with their villages;
7 Akwai kuma Ayin, Rimmon, Eter da Ashan, garuruwa huɗu ke nan da ƙauyukansu,
En Rimmon, and Token, and Ether, and Ashan; four cities with their villages;
8 da kuma dukan ƙauyukan da suke kewaye da garuruwan nan har zuwa Rama na Negeb (wato, Ba’alat-Beyer). Wannan shi ne gādon kabilar Simeyon bisa ga iyalansu.
and all the villages that were around these cities to Baalath Beer, Ramath Negev. This is the inheritance of the tribe of the descendants of Simeon according to their families.
9 Daga cikin gādon mutanen Yahuda ne aka fitar da gādon kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu, domin rabon da kabilar Yahuda suka samu ya fi ƙarfin abin da suke bukata. Saboda haka kabilar gādon Simeyon yana cikin harabar Yahuda.
Out of the part of the descendants of Judah was the inheritance of the descendants of Simeon; for the portion of the descendants of Judah was too much for them. Therefore the descendants of Simeon had inheritance in the midst of their inheritance.
10 Ƙuri’a ta uku ta fāɗa a kan Zebulun bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kai har Sarid.
And the third lot came up for the descendants of Zebulun according to their families, and the border of their inheritance was to Sadud.
11 Ta nufi yamma zuwa Marala, ta taɓa Dabbeshet, ta wuce zuwa rafin da yake kusa da Yokneyam.
Their border went up westward, and to Maralah, and reached to Dabbesheth, and it reached to the wadi that is before Jokneam.
12 Daga Sarid, ta juya gabas zuwa harabar Kislot Tabor, ta kuma wuce zuwa Daberat har zuwa Yafiya.
And it turned from Sadud eastward toward the sunrise to the border of Chisloth Tabor, and it went out to Daberath, and went up to Japhia.
13 Sa’an nan ta ci gaba, ta yi gabas zuwa Gat-Hefer da Et Kazin; ta ɓulla a Rimmon, ta juya zuwa Neya.
From there it passed along eastward to Gath Hepher, to Eth Kazin; and it went out to Rimmon which bends toward Neah.
14 A can ne iyakar ta kewaya zuwa Hannaton, sa’an nan ta ƙarasa a Kwarin Ifta El.
The border turned around it on the north to Hannathon; and it ended at the Valley of Iphtah El;
15 Zebulun ta ƙunshi garuruwa goma sha biyu da ƙauyukansu. Garuruwan sun haɗa da Kattat, Nahalal, Shimron, Idala da Betlehem.
Kattath, Nahalal, Shim'on, Idalah, and Bethlehem: twelve cities with their villages.
16 Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Zebulun ta samu, bisa ga iyalansu.
This is the inheritance of the descendants of Zebulun according to their families, these cities with their villages.
17 Ƙuri’a ta huɗu ta fāɗa a kan kabilar Issakar, bisa ga iyalansu.
The fourth lot came out for Issachar, even for the descendants of Issachar according to their families.
18 Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Yezireyel, Kessulot, Shunem,
And their border was to Jezreel, and Chesulloth, and Shunem,
19 Hafarayim, Anaharat,
and Hapharaim, and Shion, and Anaharath,
20 Rabbat, Kishiyon, Ebez,
and Daberath, and Kishion, and Ebez,
21 Remet, En Gannim, En Hadda da Bet-Fazez.
and Remeth, and Engannim, and En Haddah, and Beth Pazzez.
22 Iyakar ta taɓa Tabor Shahazuma da Bet-Shemesh ta kuma ƙarasa a Urdun. Duka-duka garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
The border reached to Tabor, and Shahazumah, and Beth Shemesh; and their border ended at the Jordan: sixteen cities with their villages.
23 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Issakar ta samu, bisa ga iyalansu.
This is the inheritance of the tribe of the descendants of Issachar according to their families, the cities with their villages.
24 Ƙuri’a ta biyar ta fāɗa a kan kabilar Asher, bisa ga iyalansu.
The fifth lot came out for the tribe of the descendants of Asher according to their families.
25 Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Helkat, Hali, Beten, Akshaf,
Their border was from Helkath (and Hali, and Beten, and Achshaph,
26 Allammelek, Amad da Mishal. A arewanci kuma iyakar ta taɓa Karmel da Shihor Libnat.
and Allammelech, and Amad, and Mishal) and it reached to Carmel westward, and to Shihor Libnath.
27 Sai ta yi gabas zuwa Bet-Dagon, ta taɓa Zebulun da kuma Kwarin Ifta El, ta wuce arewa zuwa Bet-Emek da Neyiyel, ta wuce Kabul a hagu,
And it turned eastward to Beth Dagon, and reached to Zebulun and to the Valley of Iphtah El on the north. And the border goes north to Beth Emek and Neiel, and it went out to Cabul on the north,
28 ta kai Abdon, Rehob, Hammon da Kana, har zuwa Sidon Babba.
and Abdon, and Rehob, and Hammon, and Kanah, even to Greater Sidon.
29 Daga nan iyakar ta juya baya zuwa Rama, ta bi ta birnin nan mai katanga na Taya, ta juya ta nufi Hosa, sa’an nan ta ɓulla ta Bahar Rum cikin yankin Akzib,
The border turned to Ramah, to the fortified city of Tyre; and the border turned to Hosah, and it ended at the sea; Mahalab, and Achzib,
30 Umma, Afek da Rehob. Garuruwa ashirin da biyu ke nan da ƙauyukansu.
and Acco, and Aphek, and Rehob: twenty-two cities with their villages.
31 Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Asher ta samu bisa ga iyalansu.
This is the inheritance of the tribe of the descendants of Asher according to their families, these cities with their villages.
32 Ƙuri’a ta shida ta fāɗa a kan kabilar Naftali, bisa ga iyalansu.
The sixth lot came out for the descendants of Naphtali, even for the descendants of Naphtali according to their families.
33 Iyakarsu ta kama daga Helef, daga babban itacen Mamre nan da yake a Za’anannim, ta wuce Adami Nekeb da Yabneyel zuwa Lakkum, ta kuma ƙarasa a Urdun.
Their border was from Heleph, from the oak in Zaanannim, Adaminekeb, and Jabneel, to Lakkum. It ended at the Jordan.
34 Iyakar kuma ta juya yamma ta cikin Aznot-Tabo ta ɓulla a Hukkok. Ta taɓa Zebulun a kudu, Asher a yamma, da kuma Urdun a gabas.
The border turned westward to Aznoth Tabor, and went out from there to Hukkok. It reached to Zebulun on the south, and reached to Asher on the west, and to Judah at the Jordan toward the east.
35 Biranen da suke da katanga su ne Ziddim, Zer, Hammat, Rakkat, Kinneret,
The fortified cities were Ziddim, Zer, Hammath, Rakkath, Kinnereth,
36 Adama, Rama, Hazor,
Adamah, Ramah, Hazor,
37 Kedesh, Edireyi, En Hazor,
Kedesh, Edrei, En Hazor,
38 Yiron, Migdal El, Horem, Bet-Anat da Bet-Shemesh. Garuruwa goma sha tara ke nan da ƙauyukansu.
Yiron, Migdal El, Horem, Beth Anath, and Beth Shemesh; nineteen cities with their villages.
39 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Naftali ta samu, bisa ga iyalansu.
This is the inheritance of the tribe of the descendants of Naphtali according to their families, the cities with their villages.
40 Ƙuri’a ta bakwai ta fāɗa a kan kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
The seventh lot came out for the tribe of the descendants of Dan according to their families.
41 Ƙasarsu ta gādo ta haɗa da, Zora, Eshtawol, Ir Shemesh,
And the border of their inheritance was Zorah, and Eshtaol, and Ir Shemesh,
42 Shalim, Aiyalon, Itla,
and Shaalbin, and Aijalon, and Jithlah,
43 Elon, Timna, Ekron,
and Elon, and Timnah, and Ekron,
44 Elteke, Gibbeton, Ba’alat,
and Eltekeh, and Gibbethon, and Baalath,
45 Yehud, Bene-Berak, Gat-Rimmon,
and Jehud, and Azzur, and Bene Berak, and Gath Rimmon,
46 Me Yarkon da Rakkon tare da sashen da yake fuskantar Yaffa.
and from the sea, Jarkon, and Rakkon, with the border over against Joppa.
47 (Amma ya zama wa mutanen kabilar Dan da wahala su mallaki ƙasar da aka ba su gādo, saboda haka sai suka nufi Leshem suka ci su da yaƙi, suka karkashe mutanen wurin, suka mallake ta, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato, Dan.)
And the border of the descendants of Dan slipped out of their control, so the descendants of Dan went up and fought against Leshem, and after capturing it and striking it with the sword they took possession of it and dwelt in it, and called Leshem, Dan, after the name of Dan their ancestor.
48 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
This is the inheritance of the tribe of the descendants of Dan according to their families, these cities with their villages.
49 Sa’ad da aka gama raba gādon ƙasar bisa ga ƙuri’a. Sai Isra’ilawa suka ba Yoshuwa ɗan Nun nasa rabo a cikinsu,
So they made an end of distributing the land for inheritance by its borders. The children of Israel gave an inheritance among them to Joshua the son of Nun.
50 yadda Ubangiji ya umarta, suka ba shi garin da ya ce a ba shi, Timnat Serad a ƙasar tudu ta Efraim. Ya kuma gina garin ya zauna a can.
According to the commandment of the LORD, they gave him the city which he asked, even Timnath Serah in the hill country of Ephraim; and he built the city, and lived there.
51 Waɗannan su ne rabe-raben gādon da Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin kabilan iyalan Isra’ila suka rarraba ta hanyar jefa ƙuri’a a Shilo a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada. Da haka suka yi suka gama rarraba ƙasar.
These are the inheritances, which Eleazar the priest, Joshua the son of Nun, and the heads of ancestral houses of the tribes of the children of Israel distributed by lot in Shiloh before the LORD, at the door of the Tent of Meeting. So they made an end of dividing the land.

< Yoshuwa 19 >