< Yoshuwa 19 >

1 Ƙuri’a ta biyu ta fāɗa a kan kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu. Ƙasarsu ta gādo tana cikin yankin Yahuda.
And the second lot came out to Simeon, euen for the tribe of the children of Simeon according to their families: and their inheritance was in the middes of the inheritance of the children of Iudah.
2 Waɗannan su ne wuraren da suka gāda. Beyersheba (ko Sheba), Molada,
Nowe they had in their inheritance, Beersheba, and Sheba, and Moladah,
3 Hazar Shuwal, Bilha, Ezem,
And Hazur-shual, and Balah, and Azem,
4 Eltolad, Betul, Horma,
And Eltolad, and Bethul, and Hormah,
5 Ziklag, Bet-Markabot, Hazar-Susa,
And Ziklag, and Beth-marcaboth, and Hazar-susah,
6 Bet-Lebayot da Sharuhen, garuruwa goma sha uku ke nan da ƙauyukansu.
And Beth-lebaoth, and Sharuhen: thirteene cities with their villages.
7 Akwai kuma Ayin, Rimmon, Eter da Ashan, garuruwa huɗu ke nan da ƙauyukansu,
Ain, Remmon, and Ether, and Ashan: foure cities with their villages.
8 da kuma dukan ƙauyukan da suke kewaye da garuruwan nan har zuwa Rama na Negeb (wato, Ba’alat-Beyer). Wannan shi ne gādon kabilar Simeyon bisa ga iyalansu.
And all the villages that were round about these cities, vnto Baalathbeer, and Ramath Southward: this is the inheritance of the tribe of the children of Simeon according to their families.
9 Daga cikin gādon mutanen Yahuda ne aka fitar da gādon kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu, domin rabon da kabilar Yahuda suka samu ya fi ƙarfin abin da suke bukata. Saboda haka kabilar gādon Simeyon yana cikin harabar Yahuda.
Out of the portion of the children of Iudah came ye inheritance of the childre of Simeon: for the part of ye children of Iudah was too much for them: therefore the children of Simeon had their inheritance within their inheritance.
10 Ƙuri’a ta uku ta fāɗa a kan Zebulun bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kai har Sarid.
Also the third lot arose for the children of Zebulun according to their families: and the coastes of their inheritance came to Sarid,
11 Ta nufi yamma zuwa Marala, ta taɓa Dabbeshet, ta wuce zuwa rafin da yake kusa da Yokneyam.
And their border goeth vp Westwarde, euen to Maralah, and reacheth to Dabbasheth, and meeteth with the riuer that lyeth before Iokneam,
12 Daga Sarid, ta juya gabas zuwa harabar Kislot Tabor, ta kuma wuce zuwa Daberat har zuwa Yafiya.
And turneth from Sarid Eastward towarde the sunne rising vnto the border of Chisloth-tabor, and goeth out to Daberath, and ascendeth to Iaphia,
13 Sa’an nan ta ci gaba, ta yi gabas zuwa Gat-Hefer da Et Kazin; ta ɓulla a Rimmon, ta juya zuwa Neya.
And from thence goeth along Eastwarde towarde the sunne rising to Gittah-hepher to Ittah-kazin, and goeth foorth to Rimmon, and turneth to Neah.
14 A can ne iyakar ta kewaya zuwa Hannaton, sa’an nan ta ƙarasa a Kwarin Ifta El.
And this border compasseth it on ye North side to Hannathon, and the endes thereof are in the valley of Iiphtah-el,
15 Zebulun ta ƙunshi garuruwa goma sha biyu da ƙauyukansu. Garuruwan sun haɗa da Kattat, Nahalal, Shimron, Idala da Betlehem.
And Kattath, and Nahallal, and Shimron, and Idalah, and Beth-lehem: twelue cities with their villages.
16 Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Zebulun ta samu, bisa ga iyalansu.
This is the inheritance of the children of Zebulun according to their families: that is, these cities and their villages.
17 Ƙuri’a ta huɗu ta fāɗa a kan kabilar Issakar, bisa ga iyalansu.
The fourth lot came out to Issachar, euen for the children of Issachar according to their families.
18 Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Yezireyel, Kessulot, Shunem,
And their coast was Izreelah, and Chesulloth, and Shunem,
19 Hafarayim, Anaharat,
And Hapharaim, and Shion, and Anaharath,
20 Rabbat, Kishiyon, Ebez,
And Harabbith, and Kishion, and Abez,
21 Remet, En Gannim, En Hadda da Bet-Fazez.
And Remeth, and En-gannim, and Enhaddah, and Beth-pazzez.
22 Iyakar ta taɓa Tabor Shahazuma da Bet-Shemesh ta kuma ƙarasa a Urdun. Duka-duka garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
And this coast reacheth to Tabor, and Shahazimath, and Beth-shemesh, and the endes of their coast reach to Iorden: sixteene cities with their villages.
23 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Issakar ta samu, bisa ga iyalansu.
This is the inheritance of the tribe of the children of Issachar according to their families: that is, the cities, and their villages.
24 Ƙuri’a ta biyar ta fāɗa a kan kabilar Asher, bisa ga iyalansu.
Also the fift lot came out for the tribe of the children of Asher according to their families.
25 Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Helkat, Hali, Beten, Akshaf,
And their coast was Helcath, and Hali, and Beten, and Achshaph,
26 Allammelek, Amad da Mishal. A arewanci kuma iyakar ta taɓa Karmel da Shihor Libnat.
And Alammelech, and Amad, and Misheal, and came to Carmel Westward, and to Shihor Libnath,
27 Sai ta yi gabas zuwa Bet-Dagon, ta taɓa Zebulun da kuma Kwarin Ifta El, ta wuce arewa zuwa Bet-Emek da Neyiyel, ta wuce Kabul a hagu,
And turneth towarde the sunne rising to Beth-dagon, and commeth to Zebulun, and to the valley of Iiphtah-el, toward the Northside of Beth-emek, and Neiel, and goeth out on the left side of Cabul,
28 ta kai Abdon, Rehob, Hammon da Kana, har zuwa Sidon Babba.
And to Ebron, and Rehob, and Hammon, and Kanah, vnto great Zidon.
29 Daga nan iyakar ta juya baya zuwa Rama, ta bi ta birnin nan mai katanga na Taya, ta juya ta nufi Hosa, sa’an nan ta ɓulla ta Bahar Rum cikin yankin Akzib,
Then the coast turneth to Ramah and to the strong citie of Zor, and this border turneth to Hosah, and the ends thereof are at the Sea from Hebel to Achzib,
30 Umma, Afek da Rehob. Garuruwa ashirin da biyu ke nan da ƙauyukansu.
Vmmah also and Aphek, and Rehob: two and twentie cities with their villages.
31 Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Asher ta samu bisa ga iyalansu.
This is the inheritance of the tribe of the children of Asher according to their families: that is, these cities and their villages.
32 Ƙuri’a ta shida ta fāɗa a kan kabilar Naftali, bisa ga iyalansu.
The sixt lot came out to the children of Naphtali, euen to the children of Naphtali according to their families.
33 Iyakarsu ta kama daga Helef, daga babban itacen Mamre nan da yake a Za’anannim, ta wuce Adami Nekeb da Yabneyel zuwa Lakkum, ta kuma ƙarasa a Urdun.
And their coast was from Heleph, and from Allon in Zaanannim, and Adaminekeb, and Iabneel, euen to Lakum, and the ends thereof are at Iorden.
34 Iyakar kuma ta juya yamma ta cikin Aznot-Tabo ta ɓulla a Hukkok. Ta taɓa Zebulun a kudu, Asher a yamma, da kuma Urdun a gabas.
So this coast turneth Westwarde to Aznoth-tabor, and goeth out from thence to Hukkok, and reacheth to Zebulun on the Southside, and goeth to Asher on the Westside, and to Iudah by Iorden toward the sunne rising.
35 Biranen da suke da katanga su ne Ziddim, Zer, Hammat, Rakkat, Kinneret,
And the strong cities are Ziddim, Zer, and Hammath, Rakkath, and Cinneereth,
36 Adama, Rama, Hazor,
And Adamah, and Ramah, and Hazor,
37 Kedesh, Edireyi, En Hazor,
And Kedesh, and Edrei, and En-hazor,
38 Yiron, Migdal El, Horem, Bet-Anat da Bet-Shemesh. Garuruwa goma sha tara ke nan da ƙauyukansu.
And Iron, and Migdal-el, Horem, and Beth-anah, and Beth-shemesh: nineteene cities with their villages.
39 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Naftali ta samu, bisa ga iyalansu.
This is the inheritance of the tribe of the children of Naphtali according to their families: that is, the cities and their villages.
40 Ƙuri’a ta bakwai ta fāɗa a kan kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
The seuenth lot came out for the tribe of the children of Dan according to their families.
41 Ƙasarsu ta gādo ta haɗa da, Zora, Eshtawol, Ir Shemesh,
And the coast of their inheritance was Zorah, and Eshtaol, and Ir-shemesh,
42 Shalim, Aiyalon, Itla,
And Shaalabbin, and Aiialon, and Ithlah,
43 Elon, Timna, Ekron,
And Elon, and Temnathah, and Ekron,
44 Elteke, Gibbeton, Ba’alat,
And Eltekeh, and Gibbethon, and Baalah,
45 Yehud, Bene-Berak, Gat-Rimmon,
And Iehud, and Bene-berak, and Gath-rimmon,
46 Me Yarkon da Rakkon tare da sashen da yake fuskantar Yaffa.
And Me-iarkon, and Rakkon, with the border that lieth before Iapho.
47 (Amma ya zama wa mutanen kabilar Dan da wahala su mallaki ƙasar da aka ba su gādo, saboda haka sai suka nufi Leshem suka ci su da yaƙi, suka karkashe mutanen wurin, suka mallake ta, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato, Dan.)
But the coastes of the children of Dan fell out too litle for them: therefore the children of Dan went vp to fight against Leshem, and tooke it, and smote it with the edge of the sworde, and possessed it, and dwelt therein, and called Leshem, Dan after the name of Dan their father.
48 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
This is the inheritance of the tribe of the childre of Dan according to their families: that is, these cities and their villages.
49 Sa’ad da aka gama raba gādon ƙasar bisa ga ƙuri’a. Sai Isra’ilawa suka ba Yoshuwa ɗan Nun nasa rabo a cikinsu,
When they had made an ende of deuiding the lande by the coastes thereof, then the children of Israel gaue an inheritance vnto Ioshua the sonne of Nun among them.
50 yadda Ubangiji ya umarta, suka ba shi garin da ya ce a ba shi, Timnat Serad a ƙasar tudu ta Efraim. Ya kuma gina garin ya zauna a can.
According to the worde of the Lord they gaue him the citie which hee asked, euen Timnath-serah in mount Ephraim: and hee built the citie and dwelt therein.
51 Waɗannan su ne rabe-raben gādon da Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin kabilan iyalan Isra’ila suka rarraba ta hanyar jefa ƙuri’a a Shilo a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada. Da haka suka yi suka gama rarraba ƙasar.
These are ye heritages which Eleazar the Priest, and Ioshua the sonne of Nun, and the chiefe fathers of the tribes of the children of Israel deuided by lot in Shiloh before the Lord at the doore of the Tabernacle of the Congregation: so they made an ende of deuiding the countrey.

< Yoshuwa 19 >