< Yoshuwa 19 >

1 Ƙuri’a ta biyu ta fāɗa a kan kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu. Ƙasarsu ta gādo tana cikin yankin Yahuda.
And the second lot came forth to Simeon, for the tribe of the children of Simeon according to their families; and their inheritance was within the inheritance of the children of Judah.
2 Waɗannan su ne wuraren da suka gāda. Beyersheba (ko Sheba), Molada,
And they had in their inheritance Beer-sheba, and Sheba, and Moladah,
3 Hazar Shuwal, Bilha, Ezem,
and Hazar-Shual, and Balah, and Ezem,
4 Eltolad, Betul, Horma,
and Eltolad, and Bethul, and Hormah,
5 Ziklag, Bet-Markabot, Hazar-Susa,
and Ziklag, and Beth-marcaboth, and Hazar-susah,
6 Bet-Lebayot da Sharuhen, garuruwa goma sha uku ke nan da ƙauyukansu.
and Beth-lebaoth, and Sharuhen: thirteen cities and their hamlets;
7 Akwai kuma Ayin, Rimmon, Eter da Ashan, garuruwa huɗu ke nan da ƙauyukansu,
Ain, Rimmon, and Ether, and Ashan: four cities and their hamlets;
8 da kuma dukan ƙauyukan da suke kewaye da garuruwan nan har zuwa Rama na Negeb (wato, Ba’alat-Beyer). Wannan shi ne gādon kabilar Simeyon bisa ga iyalansu.
and all the hamlets that are round these cities to Baalath-beer, [that is] Ramah of the south. This is the inheritance of the tribe of the children of Simeon according to their families.
9 Daga cikin gādon mutanen Yahuda ne aka fitar da gādon kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu, domin rabon da kabilar Yahuda suka samu ya fi ƙarfin abin da suke bukata. Saboda haka kabilar gādon Simeyon yana cikin harabar Yahuda.
Out of the lot of the children of Judah was the inheritance of the children of Simeon; for the portion of the children of Judah was too great for them, and the children of Simeon inherited within their inheritance.
10 Ƙuri’a ta uku ta fāɗa a kan Zebulun bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kai har Sarid.
And the third lot came up for the children of Zebulun according to their families. And the border of their inheritance was unto Sarid;
11 Ta nufi yamma zuwa Marala, ta taɓa Dabbeshet, ta wuce zuwa rafin da yake kusa da Yokneyam.
and their border went up westwards, and [to] Marealah, and reached to Dabbesheth, and reached to the torrent that is before Jokneam;
12 Daga Sarid, ta juya gabas zuwa harabar Kislot Tabor, ta kuma wuce zuwa Daberat har zuwa Yafiya.
and turned from Sarid eastward, toward the sun-rising, to the border of Chisloth-Tabor, and went out to Dabrath, and went up to Japhia;
13 Sa’an nan ta ci gaba, ta yi gabas zuwa Gat-Hefer da Et Kazin; ta ɓulla a Rimmon, ta juya zuwa Neya.
and from thence it passed eastward toward the sun-rising to Gath-Hepher, to Eth-kazin, and went out to Rimmon which reaches to Neah;
14 A can ne iyakar ta kewaya zuwa Hannaton, sa’an nan ta ƙarasa a Kwarin Ifta El.
and the border turned round it northwards to Hannathon: and ended in the valley of Jiphthah-el; ...
15 Zebulun ta ƙunshi garuruwa goma sha biyu da ƙauyukansu. Garuruwan sun haɗa da Kattat, Nahalal, Shimron, Idala da Betlehem.
and Kattath, and Nahalal, and Shimron, and Jidalah, and Beth-lehem: twelve cities and their hamlets.
16 Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Zebulun ta samu, bisa ga iyalansu.
This was the inheritance of the children of Zebulun according to their families, these cities and their hamlets.
17 Ƙuri’a ta huɗu ta fāɗa a kan kabilar Issakar, bisa ga iyalansu.
The fourth lot came forth to Issachar, for the children of Issachar according to their families.
18 Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Yezireyel, Kessulot, Shunem,
And their territory was toward Jizreel, and Chesulloth, and Shunem,
19 Hafarayim, Anaharat,
and Hapharaim, and Shion, and Anaharath,
20 Rabbat, Kishiyon, Ebez,
and Rabbith, and Kishion, and Ebez,
21 Remet, En Gannim, En Hadda da Bet-Fazez.
and Remeth, and En-gannim, and En-haddah, and Beth-pazzez;
22 Iyakar ta taɓa Tabor Shahazuma da Bet-Shemesh ta kuma ƙarasa a Urdun. Duka-duka garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
and the border reached to Tabor, and Shahazimah, and Beth-shemesh; and their border ended at the Jordan: sixteen cities and their hamlets.
23 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Issakar ta samu, bisa ga iyalansu.
This was the inheritance of the tribe of the children of Issachar according to their families, the cities and their hamlets.
24 Ƙuri’a ta biyar ta fāɗa a kan kabilar Asher, bisa ga iyalansu.
And the fifth lot came forth for the tribe of the children of Asher according to their families.
25 Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Helkat, Hali, Beten, Akshaf,
And their territory was Helkath, and Hali, and Beten, and Acshaph,
26 Allammelek, Amad da Mishal. A arewanci kuma iyakar ta taɓa Karmel da Shihor Libnat.
and Allammelech, and Amead, and Mishal; and [the border] reached to Carmel westwards, and to Shihor-libnath,
27 Sai ta yi gabas zuwa Bet-Dagon, ta taɓa Zebulun da kuma Kwarin Ifta El, ta wuce arewa zuwa Bet-Emek da Neyiyel, ta wuce Kabul a hagu,
and turned towards the sun-rising to Beth-Dagon, and reached to Zebulun, and to the valley of Jiphthah-el northward [to] Beth-emek and Neiel, and went out to Cabul on the left,
28 ta kai Abdon, Rehob, Hammon da Kana, har zuwa Sidon Babba.
and Ebron, and Rehob, and Hammon, and Kanah, as far as great Zidon;
29 Daga nan iyakar ta juya baya zuwa Rama, ta bi ta birnin nan mai katanga na Taya, ta juya ta nufi Hosa, sa’an nan ta ɓulla ta Bahar Rum cikin yankin Akzib,
and the border turned to Ramah, and as far as the fortified city of Tyre; and the border turned to Hosah; and ended at the sea by the tract of country of Achzib;
30 Umma, Afek da Rehob. Garuruwa ashirin da biyu ke nan da ƙauyukansu.
and Ummah, and Aphek, and Rehob: twenty-two cities and their hamlets.
31 Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Asher ta samu bisa ga iyalansu.
This was the inheritance of the tribe of the children of Asher according to their families, these cities and their hamlets.
32 Ƙuri’a ta shida ta fāɗa a kan kabilar Naftali, bisa ga iyalansu.
The sixth lot came forth to the children of Naphtali, for the children of Naphtali according to their families.
33 Iyakarsu ta kama daga Helef, daga babban itacen Mamre nan da yake a Za’anannim, ta wuce Adami Nekeb da Yabneyel zuwa Lakkum, ta kuma ƙarasa a Urdun.
And their border was from Heleph, from the oak of Zaanannim; and Adami-nekeb and Jabneel to Lakkum; and ended at the Jordan;
34 Iyakar kuma ta juya yamma ta cikin Aznot-Tabo ta ɓulla a Hukkok. Ta taɓa Zebulun a kudu, Asher a yamma, da kuma Urdun a gabas.
and the border turned westwards to Aznoth-Tabor, and went out from thence to Hukkok, and reached to Zebulun on the south, and reached to Asher on the west, and to Judah upon Jordan towards the sun-rising.
35 Biranen da suke da katanga su ne Ziddim, Zer, Hammat, Rakkat, Kinneret,
And the fortified cities were Ziddim, Zer, and Hammath, Rakkath, and Chinnereth,
36 Adama, Rama, Hazor,
and Adamah, and Ramah, and Hazor,
37 Kedesh, Edireyi, En Hazor,
and Kedesh, and Edrei, and En-Hazor,
38 Yiron, Migdal El, Horem, Bet-Anat da Bet-Shemesh. Garuruwa goma sha tara ke nan da ƙauyukansu.
and Jiron, and Migdal-el, Horem, and Beth-anath, and Beth-shemesh: nineteen cities and their hamlets.
39 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Naftali ta samu, bisa ga iyalansu.
This was the inheritance of the tribe of the children of Naphtali according to their families, the cities and their hamlets.
40 Ƙuri’a ta bakwai ta fāɗa a kan kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
The seventh lot came forth for the tribe of the children of Dan according to their families.
41 Ƙasarsu ta gādo ta haɗa da, Zora, Eshtawol, Ir Shemesh,
And the territory of their inheritance was Zoreah, and Eshtaol, and Ir-shemesh,
42 Shalim, Aiyalon, Itla,
and Shaalabbin, and Ajalon, and Jithlah,
43 Elon, Timna, Ekron,
and Elon, and Timnathah, and Ekron,
44 Elteke, Gibbeton, Ba’alat,
and El-tekeh, and Gibbethon, and Baalath,
45 Yehud, Bene-Berak, Gat-Rimmon,
and Jehud, and Beneberak, and Gath-Rimmon,
46 Me Yarkon da Rakkon tare da sashen da yake fuskantar Yaffa.
and Me-jarkon, and Rakkon, with the border over against Japho.
47 (Amma ya zama wa mutanen kabilar Dan da wahala su mallaki ƙasar da aka ba su gādo, saboda haka sai suka nufi Leshem suka ci su da yaƙi, suka karkashe mutanen wurin, suka mallake ta, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato, Dan.)
And the border of the children of Dan ended with these; and the children of Dan went up and fought against Leshem, and took it, and smote it with the edge of the sword, and took possession of it, and dwelt in it, and called Leshem, Dan, after the name of Dan their father.
48 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
This was the inheritance of the tribe of the children of Dan according to their families, these cities and their hamlets.
49 Sa’ad da aka gama raba gādon ƙasar bisa ga ƙuri’a. Sai Isra’ilawa suka ba Yoshuwa ɗan Nun nasa rabo a cikinsu,
And they ended dividing the land for inheritance according to its borders. And the children of Israel gave an inheritance to Joshua the son of Nun among them.
50 yadda Ubangiji ya umarta, suka ba shi garin da ya ce a ba shi, Timnat Serad a ƙasar tudu ta Efraim. Ya kuma gina garin ya zauna a can.
According to the word of Jehovah they gave him the city that he asked, Timnath-serah in the hill-country of Ephraim; and he built the city, and dwelt in it.
51 Waɗannan su ne rabe-raben gādon da Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin kabilan iyalan Isra’ila suka rarraba ta hanyar jefa ƙuri’a a Shilo a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada. Da haka suka yi suka gama rarraba ƙasar.
These were the inheritances, which Eleazar the priest, and Joshua the son of Nun, and the chief fathers of the tribes of the children of Israel, distributed by lot in Shiloh before Jehovah, at the entrance of the tent of meeting. And they ended dividing the land.

< Yoshuwa 19 >