< Yoshuwa 18 >
1 Isra’ilawa duka suka taru a Shilo suka kafa tenti inda za su dinga taruwa. Yanzu ƙasar tana ƙarƙashin mulkinsu,
Celotna skupnost Izraelovih otrok se je zbrala skupaj pri Šilu in tam postavila šotorsko svetišče skupnosti. In dežela je bila podjarmljena pred njimi.
2 amma akwai sauran kabilu bakwai na Isra’ila waɗanda ba su samu rabon gādonsu ba tukuna.
Tam je med Izraelovimi otroki ostalo sedem rodov, ki še niso prejeli svoje dediščine.
3 Saboda haka Yoshuwa ya ce wa Isra’ilawa, “Har yaushe za ku yi jinkirin shiga, ku mallaki ƙasar da Ubangiji Allah na iyayenku ya ba ku?
Józue je rekel Izraelovim otrokom: »Doklej se obirate, da greste, da vzamete v last deželo, ki vam jo je dal Gospod, Bog vaših očetov?
4 Ku ba da mutum uku daga kowace kabila, ni kuwa in aike su, su zagaya dukan ƙasar su rubuta bayani game da ita, bisa ga yadda za a raba ta gādo ga kowace kabila, sa’an nan su dawo wurina.
Dajte izmed sebe tri može za vsak rod in poslal jih bom in vstali bodo in šli skozi deželo in jo opisali glede na njihovo dediščino in ponovno bodo prišli k meni.
5 Za ku raba ƙasar kashi bakwai. Mutanen Yahuda za su ci gaba da kasancewa a wurin da suke a kudu, sai kuma mutanen Yusuf a wurin da suke a arewa.
To bodo razdelili na sedem delov. Juda bo ostal v svojih pokrajinah na jugu in Jožefova hiša bo ostala v svojih pokrajinah na severu.
6 Bayan kun auna ƙasar, ku raba ta kashi bakwai, sai ku kawo mini taswirar ƙasar. Ni kuma in yi muku ƙuri’a a gaban Ubangiji Allahnmu.
Vi boste torej opisali deželo v sedmih delih in opis prinesli sèm k meni, da lahko mečem žrebe za vas tukaj pred Gospodom, svojim Bogom.
7 Lawiyawa ba su da rabo a cikinku, domin aikin firistocin da suke yi wa Ubangiji shi ne gādonsu. Gad, Ruben da rabin kabilar Manasse kuwa sun riga sun samu gādonsu a gabashin gefen Urdun, Musa bawan Ubangiji ya ba su.”
Toda Lévijevci nimajo deleža med vami, kajti Gospodovo duhovništvo je njihova dediščina. Gad, Ruben in polovica Manásejevega rodu so prejeli svojo dediščino onkraj Jordana, na vzhodu, ki jim jo je dal Gospodov služabnik Mojzes.«
8 Da mutanen za su kama hanya su je su zāna yadda ƙasar take, Yoshuwa ya umarce su cewa, “Ku je ku ga yadda ƙasar take. Sa’an nan ku dawo wurina, zan yi muku ƙuri’a a nan Shilo a gaban Ubangiji.”
Možje so vstali ter odšli stran in Józue jim je naročil, da gredo, da opišejo deželo, rekoč: »Pojdite in hodite skozi deželo in jo opišite in ponovno pridite k meni, da bom tukaj v Šilu za vas lahko vrgel žrebe pred Gospodom.«
9 Mutanen kuwa suka tafi suka bi ta cikin ƙasar, suka bayyana yadda take a rubuce, gari-gari, kashi bakwai, suka koma wurin Yoshuwa a Shilo.
Možje so odšli in šli skozi deželo in jo v knjigi opisali po mestih v sedmih delih in ponovno prišli k Józuetu, k vojski pri Šilu.
10 Sai Yoshuwa ya yi musu ƙuri’a a gaban Ubangiji, a nan ne ya raba wa Isra’ilawa ƙasar bisa ga yadda aka raba su kabila-kabila.
Józue je zanje v Šilu metal žrebe pred Gospodom in tam je Józue Izraelovim otrokom razdelil deželo glede na njihove oddelke.
11 Ƙuri’ar kabilar Benyamin bisa ga iyalansu. Rabonsu ya kama daga ƙasar da take tsakanin kabilar Yahuda da ta Yusuf.
Žreb rodu Benjaminovih otrok je prišel gor glede na njihove družine in pokrajina njihovega žreba je prišla naprej med Judovimi otroki in Jožefovimi otroki.
12 Daga gefen arewa, iyakarsu ta kama ne daga Urdun, ta wuce arewa a gangaren Yeriko, ta nufi yamma cikin ƙasar kan tudu, ta fito a jejin Bet-Awen.
Njihova meja na severni strani je bila od Jordana in meja je šla gor k strani Jerihe na severni strani in se dvigala skozi gore proti zahodu in njeni izhodi so bili pri divjini Bet Aven.
13 Daga can ta ƙetare zuwa gangaren Luz a kudu (wato, Betel), ta wuce zuwa Atarot Adda a tudun arewa na kwarin Bet-Horon.
Meja je od tam šla preko, proti Luzu, k strani Luza, ki je Betel, proti jugu in meja se je spustila k Atrót Adárju, blizu hriba, ki leži na južni strani spodnjega Bet Horóna.
14 Daga tudun da yake fuskantar Bet-Horon a kudu, iyakar ta juya kudu ta gefen yamma ta ɓullo a Kiriyat Ba’al (wato, Kiriyat Yeyarim), birnin Yahuda. Wannan ita ce iyakar a wajen yamma.
Meja je bila potegnjena od tam in obdala vogal morja proti jugu, od hriba, ki leži pred Bet Horónom proti jugu in njihovi izhodi so bili pri Kirját Báalu, ki je Kirját Jearím, mesto Judovih otrok. To je bila zahodna četrtina.
15 A gefen kudu kuwa, iyakar ta fara daga ƙauyukan Kiriyat Yeyarim wajen yamma sai ta miƙe zuwa maɓuɓɓugar ruwan Neftowa.
Južna četrtina je bila od konca Kirját Jearíma in meja se je nadaljevala na zahod in izšla pri izviru vodá Neftóaha
16 Iyakar ta gangara zuwa gefen dutsen da yake fuskantar Kwarin Ben Hinnom, wanda yake arewa da Kwarin Refayim. Ta ci gaba ta gangara ta Kwarin Hinnom ta yi kudu kusa da birnin Yebusiyawa har zuwa En Rogel.
in meja se je spustila k vznožju gore, ki leži pred dolino sina Hinómovega in ki je v dolini velikanov na severu in se spustila k Hinómovi dolini, k strani Jebúsa na jugu in se spustila k En Rogelu
17 Sai ta nausa ta yi wajen arewa, zuwa En Shemesh, ta ci gaba zuwa Gelilot, wanda yake fuskantar hawan Adummim. Daga can ta gangara zuwa Dutsen Bohan, ɗan Ruben.
in potegnjena je bila od severa in šla naprej k En Šemešu in šla naprej proti Gelilótu, ki je nasproti vzpona k Adumímu in se spustila h kamnu Rubenovega sina Bohana
18 Sai ta wuce ta yi arewancin gangaren Bet-Araba, ta wuce har zuwa cikin Araba.
in šla naprej proti strani nasproti Arábi proti severu in se spustila k Arábi.
19 Sa’an nan ta wuce zuwa arewancin gangaren Bet-Hogla ta kuma ɓulla a arewancin gaɓar Tekun Gishiri, a bakin Urdun a kudu. Wannan ita ce iyakar a wajen kudu.
Meja je šla vzdolž strani Bet Hogle proti severu in izhodi meje so bili pri severnem zalivu slanega morja, pri južnem koncu Jordana. To je bila južna pokrajina.
20 Urdun shi ne iyaka a wajen gabas. Waɗannan su ne iyakokin yankin ƙasar da iyalan kabilar Benyamin suka gāda.
Jordan je bil njegova meja na vzhodni strani. To je bila dediščina Benjaminovih otrok, po njihovih pokrajinah naokoli, glede na njihove družine.
21 Waɗannan su ne garuruwan da kabilar Benyamin suke da su na gādo. Yeriko, Bet-Hogla, Emek Keziz,
Torej mesta rodov Benjaminovih otrok glede na njihove družine so bila Jeriha, Bet Hogla, dolina Kecíc,
22 Bet-Araba, Zemarayim, Betel,
Bet Arába, Cemarájim, Betel,
24 Kefar Ammoni, Ofni da Geba, garuruwa goma sha biyu ke nan da ƙauyukansu.
Kefár Amoní, Ofní in Gaba, dvanajst mest z njihovimi vasmi.
25 Akwai kuma Gibeyon, Rama, Beyerot,
Gibeón, Rama, Beerót,
27 Rekem, Irfeyel, Tarala,
Rekem, Jirpeél, Tarála,
28 Zela, Hayelef, birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima), Gibeya da Kiriyat, garuruwa goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu. Wannan shi ne rabon gādon kabilar Benyamin bisa ga iyalansu.
Cela, Elef, Jebús, kar je Jeruzalem, Gíbea in Kirját, štirinajst mest z njihovimi vasmi. To je dediščina Benjaminovih otrok glede na njihove družine.