< Yoshuwa 18 >

1 Isra’ilawa duka suka taru a Shilo suka kafa tenti inda za su dinga taruwa. Yanzu ƙasar tana ƙarƙashin mulkinsu,
And all the children of Israel assembled together in Silo, and there they set up the tabernacle of the testimony, and the land was subdued before them.
2 amma akwai sauran kabilu bakwai na Isra’ila waɗanda ba su samu rabon gādonsu ba tukuna.
But there remained seven tribes of the children of Israel, which as yet had not received their possessions.
3 Saboda haka Yoshuwa ya ce wa Isra’ilawa, “Har yaushe za ku yi jinkirin shiga, ku mallaki ƙasar da Ubangiji Allah na iyayenku ya ba ku?
And Josue said to them: How long are you indolent and slack, and go not in to possess the land which the Lord the God of your fathers hath given you?
4 Ku ba da mutum uku daga kowace kabila, ni kuwa in aike su, su zagaya dukan ƙasar su rubuta bayani game da ita, bisa ga yadda za a raba ta gādo ga kowace kabila, sa’an nan su dawo wurina.
Choose of every tribe three men, that I may send them, and they may go and compass the land, and mark it out according to the number of each multitude: and bring back to me what they have marked out.
5 Za ku raba ƙasar kashi bakwai. Mutanen Yahuda za su ci gaba da kasancewa a wurin da suke a kudu, sai kuma mutanen Yusuf a wurin da suke a arewa.
Divide to yourselves the land into seven parts: let Juda be in his bounds on the south side, and the house of Joseph on the north.
6 Bayan kun auna ƙasar, ku raba ta kashi bakwai, sai ku kawo mini taswirar ƙasar. Ni kuma in yi muku ƙuri’a a gaban Ubangiji Allahnmu.
The land in the midst between these mark ye out into seven parts; and you shall come hither to me, that I may cast lots for you before the Lord your God.
7 Lawiyawa ba su da rabo a cikinku, domin aikin firistocin da suke yi wa Ubangiji shi ne gādonsu. Gad, Ruben da rabin kabilar Manasse kuwa sun riga sun samu gādonsu a gabashin gefen Urdun, Musa bawan Ubangiji ya ba su.”
For the Levites have no part among you, but the priesthood of the Lord is their inheritance. And Gad and Ruben, and the half tribe of Manasses have already received their possessions beyond the Jordan eastward: which Moses the servant of the Lord gave them.
8 Da mutanen za su kama hanya su je su zāna yadda ƙasar take, Yoshuwa ya umarce su cewa, “Ku je ku ga yadda ƙasar take. Sa’an nan ku dawo wurina, zan yi muku ƙuri’a a nan Shilo a gaban Ubangiji.”
And when the men were risen up, to go to mark out the land, Josue commanded them, saying: Go round the land and mark it out, and return to me: that I may cast lots for you before the Lord in Silo.
9 Mutanen kuwa suka tafi suka bi ta cikin ƙasar, suka bayyana yadda take a rubuce, gari-gari, kashi bakwai, suka koma wurin Yoshuwa a Shilo.
So they went: and surveying it divided it into seven parts, writing them down in a book. And they returned to Josue, to the camp in Silo.
10 Sai Yoshuwa ya yi musu ƙuri’a a gaban Ubangiji, a nan ne ya raba wa Isra’ilawa ƙasar bisa ga yadda aka raba su kabila-kabila.
And he cast lots before the Lord in Silo, and divided the land to the children of Israel into seven parts.
11 Ƙuri’ar kabilar Benyamin bisa ga iyalansu. Rabonsu ya kama daga ƙasar da take tsakanin kabilar Yahuda da ta Yusuf.
And first came up the lot of the children of Benjamin by their families, to possess the land between the children of Juda, and the children of Joseph.
12 Daga gefen arewa, iyakarsu ta kama ne daga Urdun, ta wuce arewa a gangaren Yeriko, ta nufi yamma cikin ƙasar kan tudu, ta fito a jejin Bet-Awen.
And their border northward was from the Jordan: going along by the side of Jericho on the north side, and thence going up westward to the mountains, and reaching to the wilderness of Bethaven,
13 Daga can ta ƙetare zuwa gangaren Luz a kudu (wato, Betel), ta wuce zuwa Atarot Adda a tudun arewa na kwarin Bet-Horon.
And passing along southward by Luza, the same is Bethel: and it goeth down into Ataroth-addar to the mountain, that is on the south of the nether Beth-horon.
14 Daga tudun da yake fuskantar Bet-Horon a kudu, iyakar ta juya kudu ta gefen yamma ta ɓullo a Kiriyat Ba’al (wato, Kiriyat Yeyarim), birnin Yahuda. Wannan ita ce iyakar a wajen yamma.
And it bendeth thence going round towards the sea, south of the mountain that looketh towards Beth-horon to the southwest: and the outgoings thereof are into Cariathbaal, which is called also Cariathiarim, a city of the children of Juda. This is their coast towards the sea, westward.
15 A gefen kudu kuwa, iyakar ta fara daga ƙauyukan Kiriyat Yeyarim wajen yamma sai ta miƙe zuwa maɓuɓɓugar ruwan Neftowa.
But on the south side the border goeth out from part of Cariathiarim towards the sea, and cometh to the fountain of the waters of Nephtoa.
16 Iyakar ta gangara zuwa gefen dutsen da yake fuskantar Kwarin Ben Hinnom, wanda yake arewa da Kwarin Refayim. Ta ci gaba ta gangara ta Kwarin Hinnom ta yi kudu kusa da birnin Yebusiyawa har zuwa En Rogel.
And it goeth down to that part of the mountain that looketh on the valley of the children of Ennom: and is over against the north quarter in the furthermost part of the valley of Raphaim, and it goeth down into Geennom (that is the valley of Ennom) by the side of the Jebusite to the south: and cometh to the fountain of Rogel,
17 Sai ta nausa ta yi wajen arewa, zuwa En Shemesh, ta ci gaba zuwa Gelilot, wanda yake fuskantar hawan Adummim. Daga can ta gangara zuwa Dutsen Bohan, ɗan Ruben.
Passing thence to the north, and going out to Ensemes, that is to say, the fountain of the sue:
18 Sai ta wuce ta yi arewancin gangaren Bet-Araba, ta wuce har zuwa cikin Araba.
And it passeth along to the hills that are over against the ascent of Adommim: and it goeth down to Abenboen, that is, the stone of Been the son of Ruben: and it passeth on the north side to the champaign countries; and goeth down into the plain,
19 Sa’an nan ta wuce zuwa arewancin gangaren Bet-Hogla ta kuma ɓulla a arewancin gaɓar Tekun Gishiri, a bakin Urdun a kudu. Wannan ita ce iyakar a wajen kudu.
And it passeth by Bethhagla northward: and the outgoings thereof are towards the north of the most salt sea at the south end of the Jordan:
20 Urdun shi ne iyaka a wajen gabas. Waɗannan su ne iyakokin yankin ƙasar da iyalan kabilar Benyamin suka gāda.
Which is the border of it on the east side. This is the possession of the children of Benjamin by their borders round about, and their families.
21 Waɗannan su ne garuruwan da kabilar Benyamin suke da su na gādo. Yeriko, Bet-Hogla, Emek Keziz,
And their cities were, Jericho and Bethhagla and Vale-Casis,
22 Bet-Araba, Zemarayim, Betel,
Betharaba and Samaraim and Bethel,
23 Awwim, Fara, Ofra,
And Avim and Aphara and Ophera,
24 Kefar Ammoni, Ofni da Geba, garuruwa goma sha biyu ke nan da ƙauyukansu.
The town Emona and Ophni and Gabee: twelve cities, and their villages.
25 Akwai kuma Gibeyon, Rama, Beyerot,
Gabam and Rama and Beroth,
26 Mizfa Kefira, Moza,
And Mesphe, and Caphara, and Amosa,
27 Rekem, Irfeyel, Tarala,
And Recem, Jarephel and Tharela,
28 Zela, Hayelef, birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima), Gibeya da Kiriyat, garuruwa goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu. Wannan shi ne rabon gādon kabilar Benyamin bisa ga iyalansu.
And Sela, Eleph and Jebus, which is Jerusalem, Gabaath and Cariath: fourteen cities, and their villages. This is the possession of the children of Benjamin by their families.

< Yoshuwa 18 >