< Yoshuwa 17 >

1 Wannan shi ne gādon da aka ba wa kabilar Manasse, a matsayin ɗan farin Yusuf. Manasse yana da ɗan farin mai suna Makir. Makir shi ne mahaifin mutanen Gileyad, aka ba shi Gileyad da Bashan gama Makiriyawa jarumai ne ƙwarai.
Och lotten föll till Manasse slägte, den Josephs förste son var, och föll till Machir, Manasse första son, Gileads fader; ty han var en god stridsman, derföre fick han Gilead och Basan.
2 Aka kuma raba wa sauran mutanen kabilar Manasse rabon gādonsu bisa ga iyalansu, wato, Abiyezer, Helek, Asriyel, Shekem, Hefer da Shemida. Waɗannan su ne’ya’yan Manasse, maza, ɗan Yusuf bisa ga iyalansu.
Dem androm Manasse barnom uti deras ätter föll också till, nämliga: Abiesers barnom, Heleks barnom, Asriels barnom, Sechems barnom, Hephers barnom, och Semida barnom. Desse äro Manasse barn, Josephs sons, som mankön voro i deras ätter.
3 Zelofehad kuwa ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse ba shi da’ya’ya maza, sai dai mata. Ga sunayensu, Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.
Men Zelaphehad, Hephers son, Gileads sons, Machirs sons, Manasse sons, hade inga söner, utan döttrar; och deras namn äro desse: Mahela, Noa, Hogla, Milca, Thirza.
4 Suka je wurin Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin, suka ce musu, “Ubangiji ya umarci Musa cewa yă ba mu gādonmu tare da’yan’uwanmu maza.” Saboda haka Yoshuwa ya ba su gādo tare da’yan’uwan mahaifinsu maza bisa ga umarnin Ubangiji.
Och de gingo fram för Presten Eleazar, och för Josua, Nuns son, och för de öfversta, och sade: Herren böd Mose, att han skulle gifva oss arfvedel ibland våra bröder; så gaf han dem ock arfvedel ibland deras faders bröder, efter Herrans befallning.
5 Dalilin ke nan Manasse ya sami kashi goma ban da ƙasar Gileyad da Bashan a gabashin Urdun,
Men Manasse föllo tio snöre till, förutan det landet Gilead och Basan, som på hinsidon Jordan ligger.
6 domin’ya’ya mata na kabilar Manasse sun sami gādo tare da’ya’ya maza. Aka ba wa sauran mutanen kabilar Manasse ƙasar Gileyad.
Ty Manasse döttrar togo arfvedel med hans söner; och det landet Gilead kom de andra Manasse barn till.
7 Iyakar ƙasar Manasse ta tashi daga Asher zuwa Mikmetat a gabashin Shekem. Iyakar kuma ta miƙe har zuwa kudu wadda ta ƙunshi mutanen da suke zaune a En Taffuwa.
Och Manasse gränsa var ifrån Asser till Michmethath, som ligger för Sechem, och går ut på högra handena intill dem af EnTappuah.
8 (Manasse ne yake da ƙasar Taffuwa, amma garin Taffuwa kansa, a kan iyakar Manasse ta mutanen Efraim ce.)
Ty det landet Tappuah kom Manasse till, och är Manasse gränsa invid Ephraims barn.
9 Sa’an nan iyakar ta ci gaba ta yi kudu zuwa Rafin Kana. Akwai garuruwan da suke kudancin rafin, waɗanda suke Efraim, ko da yake suna cikin yankin Manasse. Iyakar Manasse ta miƙe zuwa arewa ta bi gefen rafin ta kuma ƙarasa a Bahar Rum.
Sedan går hon neder till NahalKana söderut till bäckstäderna, hvilka Ephraim tillhöra ibland Manasse städer; men ifrå nordan är Manasse gränsa inpå bäcken, och går ut i hafvet;
10 Ƙasar a wajen kudu ta Efraim ce, ta wajen arewa kuma ta Manasse ce. Bahar Rum ita ce iyakarsu. Asher yana wajen arewa, Issakar kuma a wajen gabas.
Ephraims söderut, och Manasse norrut, och hafvet är hans landamäre, och stöter inpå Asser ifrå nordan, och inpå Isaschar ifrån östan.
11 A yanki tsakanin Issakar da Asher, Manasse yana da waɗannan wurare, Bet-Sheyan, Ibileyam da ƙauyukanta, da mazaunan Dor da ƙauyukanta, da mazaunan En Dor da ƙauyukanta, da mazaunan Ta’anak da ƙauyukanta, da mazaunan Megiddo da ƙauyukanta (Na uku cikin jerin shi ne Nafot).
Så hade nu Manasse ibland Isaschar och Asser, BethSean och dess döttrar, Jibleam och dess döttrar, och dem i Dor och dess döttrar, och dem i Endor och dess döttrar, och dem i Thaanach och dess döttrar, och dem i Megiddo och dess döttrar, och tredje delen Naphet.
12 Duk da haka mutanen Manasse ba su iya mallakar garuruwan nan ba, domin Kan’aniyawa sun nace da zama a wannan yanki.
Och Manasse barn kunde icke intaga de städer; utan de Cananeer begynte till att bo i dessa landena.
13 Da Isra’ilawa suka yi ƙarfi, sai suka sa Kan’aniyawa suka zama masu yin musu aiki, amma ba su iya korarsu duka ba.
Men då Israels barn vordo mägtige, gjorde de de Cananeer skattskyldiga, och fördrefvo dem icke.
14 Mutanen Yusuf kuwa suka ce wa Yoshuwa, “Me ya sa ka ba mu rabon gādo ɗaya kawai? Ga shi muna da yawa kuma Ubangiji ya albarkace mu sosai.”
Då talade Josephs barn till Josua, och sade: Hvi hafver du icke gifvit mig mer än en lott, och ett snöre af arfvedelenom, och jag är dock ett mycket folk, såsom Herren hafver välsignat mig?
15 Yoshuwa ya ce musu, “In kuna da yawa sosai, in kuma ƙasar kan tudu ta Efraim ba ta ishe ku ba, sai ku je cikin jeji, ku nema wa kanku ƙasa a ƙasar Ferizziyawa da Refahiyawa.”
Då sade Josua till dem: Efter du äst ett mycket folk, så gack upp i skogen, och rödj dig der rum uti de Phereseers och Resars land, efter Ephraims berg är dig för trångt.
16 Mutanen Yusuf suka amsa suka ce, “Ƙasar kan tudu ba ta ishe mu ba, ga kuma Kan’aniyawan da suke zama a filin, da waɗanda suke Bet-Sheyan da ƙauyukanta, da waɗanda suke Kwarin Yezireyel, duk suna da keken yaƙin ƙarfe.”
Då sade Josephs barn: Berget kunne vi icke få; ty de Cananeer bruka alle jernvagnar, som i de landena Emek bo, när hvilko ligger BethSean och dess döttrar, och Jisreel i Emek.
17 Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Yusuf, wa Efraim da Manasse, “Kuna da yawa, kuna kuma da ƙarfi sosai. Ba wuri ɗaya kaɗai za ku samu gādo ba,
Josua sade till Josephs hus, Ephraim och Manasse: Du äst ett mycket folk; och efter du så mycket äst, måste du icke hafva en lott;
18 amma har da ƙasar kan tudu ma, ko da yake jeji ne, ku je ku gyara shi, duk yă zama naku. Ko da yake Kan’aniyawa suna da kekunan yaƙi na ƙarfe, suna kuma da ƙarfi, duk da haka za ku kore su.”
Utan berget skall höra dig till, der skogen är; der rödj om dig, så blifver det dins lotts ände, när du fördrifver de Cananeer, som jernvagnar hafva och mägtige äro.

< Yoshuwa 17 >