< Yoshuwa 17 >

1 Wannan shi ne gādon da aka ba wa kabilar Manasse, a matsayin ɗan farin Yusuf. Manasse yana da ɗan farin mai suna Makir. Makir shi ne mahaifin mutanen Gileyad, aka ba shi Gileyad da Bashan gama Makiriyawa jarumai ne ƙwarai.
Og Loddet faldt for Manasses Stamme: thi han var Josefs førstefødte. Makir, Manasses førstefødte, Gileads Fader — han var nemlig Kriger — fik Gilead og Basan.
2 Aka kuma raba wa sauran mutanen kabilar Manasse rabon gādonsu bisa ga iyalansu, wato, Abiyezer, Helek, Asriyel, Shekem, Hefer da Shemida. Waɗannan su ne’ya’yan Manasse, maza, ɗan Yusuf bisa ga iyalansu.
Og de øvrige Manassiter fik Land efter deres Slægter, Abiezers, Heleks, Asriels, Sjekems, Hefers og Sjemidas Sønner; det er Josefs Søn Manasses mandlige Efterkommere efter deres Slægter.
3 Zelofehad kuwa ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse ba shi da’ya’ya maza, sai dai mata. Ga sunayensu, Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.
Men Zelofhad, en Søn af Hefer, en Søn af Gilead, en Søn af Makir, en Søn af Manasse, havde ingen Sønner, kun Døtre; og hans Døtre hed Mala, Noa, Hogla, Milka og Tirza.
4 Suka je wurin Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin, suka ce musu, “Ubangiji ya umarci Musa cewa yă ba mu gādonmu tare da’yan’uwanmu maza.” Saboda haka Yoshuwa ya ba su gādo tare da’yan’uwan mahaifinsu maza bisa ga umarnin Ubangiji.
De traadte frem for Præsten Eleazar og Josua, Nuns Søn, og Øversterne og sagde: »HERREN bød Moses give os Arvelod iblandt vore Brødre!« Da gav han dem efter HERRENS Bud en Arvelod iblandt deres Faders Brødre.
5 Dalilin ke nan Manasse ya sami kashi goma ban da ƙasar Gileyad da Bashan a gabashin Urdun,
Saaledes faldt ti Parter paa Manasse foruden Landet Gilead og Basan hinsides Jordan.
6 domin’ya’ya mata na kabilar Manasse sun sami gādo tare da’ya’ya maza. Aka ba wa sauran mutanen kabilar Manasse ƙasar Gileyad.
Thi Manasses døtre fik Arvelod blandt hans Sønner. Men Landet Gilead tilfaldt Manasses øvrige Efterkommere.
7 Iyakar ƙasar Manasse ta tashi daga Asher zuwa Mikmetat a gabashin Shekem. Iyakar kuma ta miƙe har zuwa kudu wadda ta ƙunshi mutanen da suke zaune a En Taffuwa.
Og Manasses Grænse gaar fra Aser til Mikmetat, som ligger østen for Sikem; derpaa gaar Grænsen mod Syd til Befolkningen i En-Tappua.
8 (Manasse ne yake da ƙasar Taffuwa, amma garin Taffuwa kansa, a kan iyakar Manasse ta mutanen Efraim ce.)
Manasse fik Landskabet Tappua; men Byen Tappua ved Manasses Grænse tilfaldt Efraimiterne.
9 Sa’an nan iyakar ta ci gaba ta yi kudu zuwa Rafin Kana. Akwai garuruwan da suke kudancin rafin, waɗanda suke Efraim, ko da yake suna cikin yankin Manasse. Iyakar Manasse ta miƙe zuwa arewa ta bi gefen rafin ta kuma ƙarasa a Bahar Rum.
Derpaa strækker Grænsen sig ned til Kanabækken, sønden om Bækken; Byerne der tilfaldt Efraim, midt iblandt Manasses Byer; Manasses Landomraade ligger norden for Bækken. Grænsen ender derpaa ved Havet.
10 Ƙasar a wajen kudu ta Efraim ce, ta wajen arewa kuma ta Manasse ce. Bahar Rum ita ce iyakarsu. Asher yana wajen arewa, Issakar kuma a wajen gabas.
Sydsiden tilhører Efraim og Nordsiden Manasse. Havet danner Grænse; mod Nord støder de op til Aser, mod Øst til Issakar.
11 A yanki tsakanin Issakar da Asher, Manasse yana da waɗannan wurare, Bet-Sheyan, Ibileyam da ƙauyukanta, da mazaunan Dor da ƙauyukanta, da mazaunan En Dor da ƙauyukanta, da mazaunan Ta’anak da ƙauyukanta, da mazaunan Megiddo da ƙauyukanta (Na uku cikin jerin shi ne Nafot).
I Issakar og Aser tilfaldt følgende Byer Manasse: Bet-Sjean med Smaabyer, Jibleam med Smaabyer, Befolkningen i Dor med Smaabyer, Befolkningen i En-Dor med Smaabyer, Befolkningen i Ta'anak med Smaabyer og Befolkningen i Megiddo med Smaabyer, de tre Højdedrag.
12 Duk da haka mutanen Manasse ba su iya mallakar garuruwan nan ba, domin Kan’aniyawa sun nace da zama a wannan yanki.
Men Manassiterne kunde ikke drive disse Byers Indbyggere bort, det lykkedes Kana'anæerne at holde sig i disse Egne.
13 Da Isra’ilawa suka yi ƙarfi, sai suka sa Kan’aniyawa suka zama masu yin musu aiki, amma ba su iya korarsu duka ba.
Da Israeliterne blev de stærkeste, gjorde de Kana'anæerne til Hoveriarbejdere, men drev dem ikke bort.
14 Mutanen Yusuf kuwa suka ce wa Yoshuwa, “Me ya sa ka ba mu rabon gādo ɗaya kawai? Ga shi muna da yawa kuma Ubangiji ya albarkace mu sosai.”
Da talte Josefs Sønner til Josua og sagde: »Hvorfor har du kun givet mig een Lod og een Part til Arvelod, skønt jeg er et talrigt Folk, eftersom HERREN hidtil har velsignet mig?«
15 Yoshuwa ya ce musu, “In kuna da yawa sosai, in kuma ƙasar kan tudu ta Efraim ba ta ishe ku ba, sai ku je cikin jeji, ku nema wa kanku ƙasa a ƙasar Ferizziyawa da Refahiyawa.”
Josua svarede dem: »Naar du er et talrigt Folk, saa drag op i Skovlandet og ryd dig Jord der i Perizziternes og Refaiternes Land, siden Efraims Bjergland er dig for trangt!«
16 Mutanen Yusuf suka amsa suka ce, “Ƙasar kan tudu ba ta ishe mu ba, ga kuma Kan’aniyawan da suke zama a filin, da waɗanda suke Bet-Sheyan da ƙauyukanta, da waɗanda suke Kwarin Yezireyel, duk suna da keken yaƙin ƙarfe.”
Da sagde Josefs Sønner: »Bjerglandet er os ikke nok, og alle Kana'anæerne, som bor paa Slettelandet, baade de i Bet-Sjean med Smaabyer og de paa Jizre'elsletten, har jernbeslagne Vogne!«
17 Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Yusuf, wa Efraim da Manasse, “Kuna da yawa, kuna kuma da ƙarfi sosai. Ba wuri ɗaya kaɗai za ku samu gādo ba,
Da sagde Josua til Josefs Slægt, til Efraim og Manasse: »Du er et talrigt Folk og har stor Kraft; du skal ikke komme til at nøjes med een Lod,
18 amma har da ƙasar kan tudu ma, ko da yake jeji ne, ku je ku gyara shi, duk yă zama naku. Ko da yake Kan’aniyawa suna da kekunan yaƙi na ƙarfe, suna kuma da ƙarfi, duk da haka za ku kore su.”
men et Bjergland skal tilfalde dig, thi det er skovbevokset, og naar du rydder det, skal det tilfalde dig med Udløberne derfra; thi du skal drive Kana'anæerne bort, selv om de har jernbeslagne Vogne; du er nemlig stærkere end de.«

< Yoshuwa 17 >