< Yoshuwa 16 >

1 Rabon da aka ba wa Yusuf ya fara tun daga Urdun kusa da Yeriko, gabas da ruwan Yeriko, sai ya miƙe zuwa jeji, ya haura har zuwa cikin ƙasar tudu na Betel.
و قرعه برای بنی یوسف به سمت مشرق، از اردن اریحا به طرف آبهای اریحا تا صحرایی که از اریحا به سوی کوه بیت ئیل بر می‌آید، بیرون آمد.۱
2 Ya ci gaba daga Betel (wato, Luz), ya zarce zuwa sashen Arkitawa na Atarot,
و از بیت ئیل تالوز برآمده، به‌سرحد ارکیان تا عطاروت گذشت.۲
3 ya sauka zuwa yammancin bakin iyakar Yalfetiyawa har zuwa yankin Bet-Horon wanda yake cikin kwari. Ya zarce kuma zuwa Gezer, ya gangara ya yi ƙarshe a Bahar Rum.
و به سمت مغرب به‌سرحد یفلیطیان تا کناربیت حورون پایین و تا جازر پایین آمد، و انتهایش تا دریا بود.۳
4 Wannan ne yankin da aka ba wa Manasse da Efraim zuriyar Yusuf gādonsu.
پس پسران یوسف، منسی و افرایم، ملک خود را گرفتند.۴
5 Yankin Efraim ke nan bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kama daga Atarot Addar a gabas zuwa Bet-Horon,
و حدود بنی افرایم به حسب قبایل ایشان چنین بود که حد شرقی ملک ایشان عطاروت ادارتا بیت حورون بالا بود.۵
6 ta wuce zuwa Bahar Rum. Daga Mikmetat a arewa kuwa iyakar ta karkata gabas zuwa Ta’anat Shilo, ta wuce zuwa Yanowa a gabas.
و حد غربی ایشان به طرف شمال نزد مکمیت برآمد و حد ایشان به سمت مشرق به تانه شیلوه برگشته، به طرف مشرق یانوحه از آن گذشت.۶
7 Sai ta gangara daga Yanowa zuwa Atarot da Na’ara, ta bi ta Yeriko, ta kuma fito ta Urdun.
و از یانوحه به عطاروت و نعره پایین آمده، به اریحا رسید و به اردن منتهی شد.۷
8 Daga Taffuwa kuma iyakar ta bi yamma zuwa kwazazzaban Kana, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne gādon mutanen Efraim bisa ga iyalansu.
و سرحد غربی آن از تفوح تاوادی قانه رفت و آخر آن به دریا بود، این است ملک سبط بنی افرایم به حسب قبایل ایشان.۸
9 Gādon ya kuma haɗa da dukan garuruwa da ƙauyuka waɗanda aka keɓe wa mutanen Efraim daga cikin gādon mutanen Manasse.
علاوه بر شهرهایی که از میان ملک بن منسی برای بنی افرایم جدا شده بود، جمیع شهرها بادهات آنها بود.۹
10 Ba su kori Kan’aniyawan da suke zama a Gezer ba, don haka Kan’aniyawa suna zama tare da mutanen Efraim har wa yau; amma Kan’aniyawa suka zama masu yin aikin dole.
و کنعانیان را که در جازر ساکن بودند، بیرون نکردند. پس کنعانیان تا امروز درمیان افرایم ساکنند، و برای جزیه، بندگان شدند.۱۰

< Yoshuwa 16 >