< Yoshuwa 16 >

1 Rabon da aka ba wa Yusuf ya fara tun daga Urdun kusa da Yeriko, gabas da ruwan Yeriko, sai ya miƙe zuwa jeji, ya haura har zuwa cikin ƙasar tudu na Betel.
Puis le sort échut aux enfants de Joseph, depuis le Jourdain de Jérico aux eaux de Jérico vers l'Orient, qui est le désert; montant de Jérico par la montagne jusqu'à Béthel.
2 Ya ci gaba daga Betel (wato, Luz), ya zarce zuwa sashen Arkitawa na Atarot,
Et cette frontière devait sortir de Béthel vers Luz, puis passer sur les confins de l'Arkien jusqu'à Hataroth.
3 ya sauka zuwa yammancin bakin iyakar Yalfetiyawa har zuwa yankin Bet-Horon wanda yake cikin kwari. Ya zarce kuma zuwa Gezer, ya gangara ya yi ƙarshe a Bahar Rum.
Et elle devait descendre tirant vers l'Occident, aux confins du Japhletien, jusqu'aux confins de Beth-horon la basse, et jusqu'à Guézer; de sorte que ses extrémités se devaient rendre à la mer.
4 Wannan ne yankin da aka ba wa Manasse da Efraim zuriyar Yusuf gādonsu.
Ainsi les enfants de Joseph, [savoir] Manassé et Ephraïm, prirent leur héritage.
5 Yankin Efraim ke nan bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kama daga Atarot Addar a gabas zuwa Bet-Horon,
Or la frontière des enfants d'Ephraïm selon leurs familles était telle, que la frontière de leur héritage vers l'Orient fut Hatroth-addar, jusqu'à Beth-horon la haute.
6 ta wuce zuwa Bahar Rum. Daga Mikmetat a arewa kuwa iyakar ta karkata gabas zuwa Ta’anat Shilo, ta wuce zuwa Yanowa a gabas.
Et cette frontière devait sortir vers la mer en Micmethah [du côté] du Septentrion; et cette frontière devait se tourner vers l'Orient jusqu'à Tahanath-Silo, et passant du côté d'Orient, se rendre à Janoah;
7 Sai ta gangara daga Yanowa zuwa Atarot da Na’ara, ta bi ta Yeriko, ta kuma fito ta Urdun.
Puis descendre de vers Janoah à Hataroth, et vers Naharath, et se rencontrer à Jérico, et sortir au Jourdain.
8 Daga Taffuwa kuma iyakar ta bi yamma zuwa kwazazzaban Kana, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne gādon mutanen Efraim bisa ga iyalansu.
Et cette frontière devait aller de Tappuah tirant vers la mer, jusqu'au torrent de Kana; tellement que ses extrémités se devaient rendre à la mer. Ce fut là l'héritage de la Tribu des enfants d'Ephraïm, selon leurs familles;
9 Gādon ya kuma haɗa da dukan garuruwa da ƙauyuka waɗanda aka keɓe wa mutanen Efraim daga cikin gādon mutanen Manasse.
Avec les villes qui furent séparées pour les enfants d'Ephraïm parmi l'héritage des enfants de Manassé; toutes ces villes, [dis-je], avec leurs villages.
10 Ba su kori Kan’aniyawan da suke zama a Gezer ba, don haka Kan’aniyawa suna zama tare da mutanen Efraim har wa yau; amma Kan’aniyawa suka zama masu yin aikin dole.
Or ils ne dépossédèrent point les Cananéens qui habitaient à Guézer; c'est pourquoi les Cananéens ont habité parmi Ephraïm jusqu'à ce jour; mais ils ont été tributaires, et asservis.

< Yoshuwa 16 >