< Yoshuwa 16 >
1 Rabon da aka ba wa Yusuf ya fara tun daga Urdun kusa da Yeriko, gabas da ruwan Yeriko, sai ya miƙe zuwa jeji, ya haura har zuwa cikin ƙasar tudu na Betel.
And the lot, `ethir part, of the sones of Joseph felde fro Jordan ayens Jerico, and at the watris therof, fro the eest; is the wildirnesse, that stieth fro Jerico to the hil of Bethel,
2 Ya ci gaba daga Betel (wato, Luz), ya zarce zuwa sashen Arkitawa na Atarot,
and it goith out fro Bethel `in to Luzan, and passith the terme of Architaroth,
3 ya sauka zuwa yammancin bakin iyakar Yalfetiyawa har zuwa yankin Bet-Horon wanda yake cikin kwari. Ya zarce kuma zuwa Gezer, ya gangara ya yi ƙarshe a Bahar Rum.
and it goith doun to the west, bisidis the terme of Jefleti, `til to the termes of the lowere Bethoron, and of Gazer; and the cuntrees therof ben endid with the greet see,
4 Wannan ne yankin da aka ba wa Manasse da Efraim zuriyar Yusuf gādonsu.
whiche cuntreis Manasses and Effraym, the sones of Joseph, weldiden.
5 Yankin Efraim ke nan bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kama daga Atarot Addar a gabas zuwa Bet-Horon,
And the terme of the sones of Effraym, bi her meynees, and `the possessioun of hem was maad ayens the eest, Accarothaddar `til to the hiyere Bethoron.
6 ta wuce zuwa Bahar Rum. Daga Mikmetat a arewa kuwa iyakar ta karkata gabas zuwa Ta’anat Shilo, ta wuce zuwa Yanowa a gabas.
And the coostis goon out in to the see; sotheli Mathmetath biholdith the north, and cumpassith the termes ayens the eest in Tharnarselo,
7 Sai ta gangara daga Yanowa zuwa Atarot da Na’ara, ta bi ta Yeriko, ta kuma fito ta Urdun.
and passith fro the stronde of Janee; and it goith doun fro Janee in to Atharoth and Noathara, and cometh in to Jerico; and it goith out to Jordan fro Taphua,
8 Daga Taffuwa kuma iyakar ta bi yamma zuwa kwazazzaban Kana, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne gādon mutanen Efraim bisa ga iyalansu.
and passith ayens the see in to the valey of `the place of rehedis; and the goyngis out therof ben to the salteste see. This is the possessioun of the sones of Effraym, bi her meynees;
9 Gādon ya kuma haɗa da dukan garuruwa da ƙauyuka waɗanda aka keɓe wa mutanen Efraim daga cikin gādon mutanen Manasse.
and citees and the townes of tho ben departid to the sones of Effraym, in the myddis of the possessioun of the sones of Manasses.
10 Ba su kori Kan’aniyawan da suke zama a Gezer ba, don haka Kan’aniyawa suna zama tare da mutanen Efraim har wa yau; amma Kan’aniyawa suka zama masu yin aikin dole.
And the sones of Effraym killiden not Cananey, that dwellide in Gazer; and Cananey dwellide tributarie in the myddis of Effraym til in to this day.