< Yoshuwa 16 >

1 Rabon da aka ba wa Yusuf ya fara tun daga Urdun kusa da Yeriko, gabas da ruwan Yeriko, sai ya miƙe zuwa jeji, ya haura har zuwa cikin ƙasar tudu na Betel.
Sinovima Josipovim pripao je ždrijebom posjed: od Jordana kod Jerihona, od Jerihonskih voda na istok, pa pustinjom k Betelskoj gori;
2 Ya ci gaba daga Betel (wato, Luz), ya zarce zuwa sashen Arkitawa na Atarot,
od Betel-Luza međa se nastavljala područjem Arkijaca do Atarota.
3 ya sauka zuwa yammancin bakin iyakar Yalfetiyawa har zuwa yankin Bet-Horon wanda yake cikin kwari. Ya zarce kuma zuwa Gezer, ya gangara ya yi ƙarshe a Bahar Rum.
Potom se spuštala na zapad do jafletske međe, sve do Donjeg Bet-Horona i do Gezera, odakle je izlazila na more.
4 Wannan ne yankin da aka ba wa Manasse da Efraim zuriyar Yusuf gādonsu.
To je bila baština Josipovih sinova: Manašea i Efrajima.
5 Yankin Efraim ke nan bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kama daga Atarot Addar a gabas zuwa Bet-Horon,
Područje sinova Efrajimovih po njihovim porodicama bilo je ovo: međa baštine njihove prema istoku išla je od Atrot Adara pa do Gornjega Bet-Horona.
6 ta wuce zuwa Bahar Rum. Daga Mikmetat a arewa kuwa iyakar ta karkata gabas zuwa Ta’anat Shilo, ta wuce zuwa Yanowa a gabas.
Odatle se pružala do mora ... (išla na) Mikmetat na sjeveru i zavijala dalje na istok prema Taanat Šilu i prolazila s istočne strane do Janoaha.
7 Sai ta gangara daga Yanowa zuwa Atarot da Na’ara, ta bi ta Yeriko, ta kuma fito ta Urdun.
Od Janoaha spuštala se u Atarot i Naarat i onda, dotičući se Jerihona, udarala na Jordan.
8 Daga Taffuwa kuma iyakar ta bi yamma zuwa kwazazzaban Kana, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne gādon mutanen Efraim bisa ga iyalansu.
Od Tapuaha išla je ta međa prema zapadu do potoka Kane te izbijala na more. To je bila baština plemena sinova Efrajimovih po njihovim porodicama.
9 Gādon ya kuma haɗa da dukan garuruwa da ƙauyuka waɗanda aka keɓe wa mutanen Efraim daga cikin gādon mutanen Manasse.
A Efrajimovi su sinovi imali sve te gradove s njihovim selima i još odvojene gradove usred baštine sinova Manašeovih.
10 Ba su kori Kan’aniyawan da suke zama a Gezer ba, don haka Kan’aniyawa suna zama tare da mutanen Efraim har wa yau; amma Kan’aniyawa suka zama masu yin aikin dole.
Ali nisu uspjeli otjerati Kanaanaca koji su živjeli u Gezeru. Tako su Kanaanci ostali među sinovima Efrajimovim do danas, ali im bijaše nametnuta tlaka.

< Yoshuwa 16 >